Showing 21001 words to 24000 words out of 153569 words
Chapter 8 - A Duniyata Book 1 Complete Hausa Novel
taurari na daban a cikin familynsu gidansu dama unguwarsu gaba daya......zata nunawa wadanda suke ganin ba zasu iya ba.....ba zasu kai ba......zasu tozarta cewa......zasu iya iya.....za kuma sukai labarin da su basu kai ba.
A nutse ta waiwaya ta kalleta. Tadan zuba mata idanu na second tana nazarinta. Tun tuntuni ta fahimci akwai kwantacciyar damuwa a qasan ranta,kasancewarta mutum me wani irin kakkaifan hange da saurin gano abu. Kaifin fikirarta ya fita daban dana dukkan wani yaro dake cikin gidan,don haka take saurin fahimtar kowanne motsi taku da kuma sauyawar yanayin qannenta.
"Huda......wai baki duban lokaci?" Batace komai ba huda din,saita zare cup din bakinta ta direshi tana niyyar miqewa,abinda ya sakata maida idanunta ga cup din kenan. Ko rabin tea din bata sha ba,ta sake maida kallonta a kanta
"Kin qoshi kenan?" Kai ta jinjina mata kafin tace
"Banajin yunwa dama kwata kwata" Kyawawan idanun nata masu wani irin shape ta lumshe,can qasan zuciyarta tana furta
"Alhamdulillah,astgafirullah" A duniya daya daga cikin sauti da take matuqar son ta yita ji kenan daga harsunan qannenta
"BANA JIN YUNWA" Sauti mafi dadi kenan daga bakinsu zuwa kunnuwanta.
Waiwayawa tayi gefanta ta kalleta sanda ta kammala saka takalmi da socks dinta
"Nadra......shiga daki gefan katifata ki daukomin jakata na sallameku......yau din kamar babu me laka a jikinku"
"Tom" Ta amsa tana saukowa daga saman kujerar da saurinta ta wuce dakin. Sanda take maido dubanta cikin falon sai suka hada idanu da hudan. Huda ta janye daga kallonta,sai ita din taci gaba da kafeta da kallo tana dubanta
"Huda"
"Naam" Ta amsa mata ba tare da sun hada ido ba
"Wai meke damunki?" Ta jefeta da tambayar tana kebe baki......harta bude baki zatayi magana ta dakatar da ita a tsaurare
"Karki soma cemin ba komai.......na gani a idanunki da motsinki......"
"Gida......"
"Ba damuwar mutanen gidan nan ba?" Ta jefa mata tambayar tana duban idanunta,a yanzu akwai sirkin bacin rai kadan a maganarta da idanun nata
"Yaushe kika fara saka maganarsu cikin ranki?" Ta kuma tambayar tata tana kallonta
"Ashe har yanzu baki saba da halayyarsu ba?,bakisan yadda zaki zauna dasu ba?,huda ina duk qoqarin da nake a kanki ke da kike babba ki fahimci yadda zaki zauna da kowa a cikinsu?"
"Anty bakisan me suka ce ba a kanki.....bakisan me suke fada ba kullum" Ta qarashe maganar muryarta tana raurawa sosai da alamun zuciya da ruhinta gaba daya sun sare.
"Kome zasu fada huda su fadi,indai a kaina ne karki azawa kanki damuwa.......kome ma zakiji sun fada,ba wani baquwar kalma da zakiji daga bakinsu ko sabon abu.....me yasa sai yanzu zaki fara sawa kanki kina damuwa?" Ta qarashe da sigar tambaya. Qasa tayi da kanta ba tare data amsa mata ba,ita kanta batasan me yasa sai yanzun abun ke damunta ba duk da sun share shekaru dasu a haka.
Daidai sanda nadra ta qaraso ta miqa mata kyakkyawar hand bag din nata fara tas me adon brown duka jikinta dake dauke da tambarin kamfanin Gucci.
Idanunta masu sheqi ta juya zuwa ga nadra,ta saka hannu ta karbi jakar tana qoqarin zugeta.
"Anata kiran wayarki tunda na shiga" Nadra dake goya jakarta ta fada.
"Okay,barta" Ta amsa mata a taqaice,don ta tabbatar a cikin mutum biyu daya ne yake kiranta,tafi kuma gasgata zatonta akan dayan.
Zip din da take ajiye canji ta zuge,ta fidda kudin ta lissafa daidai yadda tasan zai ishesu break da kudin mota,saboda yau din basuyi abinci yadda suka saba ba kasancewar kayan abincinsu ya qare.
Daga bakin qofar falon nasu tayi tsaye hannayenta goye a qrijinta tana dubansu har suka kammala ficewa daga gidannasu,sai taja Qaqqarfar ajiyar zuciya tana sauke hannayen nata ta juya a hankali don komawa falon don kwata kwata bata samu isashen bacci ba a jiya,tanaso ta runtsa sosai sannan ta shiga kasuwa tayi musu saye saye
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 14
________________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai*
_________________________
Saidai dai dai sanda ta saki labulayen da zummar shiga ciki din taji sallamarsa ta karade tsakar gidan. Qaramin tsaki taja,tabbas tunda aka jishi da sassafen nan kamar haka to ba a shakka wata tijarar yazo yi,ko kuma akwai abinda ya hadoshi da wani. Idan da sabo zata iya cewa sun saba da halayyarsa,macce daya ce cikin gidan suke dasawa har baka iya jin kansu. Har gwara ita tasan maganinsa,ta kuma san ta yadda take bulloma tsiyarsa,duk da bata taba tsaiwa ta kulashi ba anji muryarta a matsayinsa na qanin mahaifi a gareta.
Sakaya qofar kawai tayi ta sake zuge labulen sosai sannan ta wuce uwar dakin ta yadda ba zata tsaya bata lokacin jin meke faruwa a tsakiyar gidan nasu ba,domin ita din tana cikin jerin sahun irin mutanen nan ne dai basa shiga abinda bai shafesu ba,wanda ya shafesun ma sai tura takai bango,bata da magana sam sam bare hayaniya. Wannan hali nata da siffarta ta sanyi da sauqin hali da kuma yauqinta ya sanya da yawa suke mamakin WANNAN DABI'A TATA......Dabi'ar da har yanzu su kansu basu da cikakken yaqinin a kanta,duk da cewa suna kallon gamsassun hujjoji ai sun gama bayyana a fili a game da ita.
Babban bedroom ne qwarai wanda iya dauke gado da wardrobe guda bibbiyu,sai dressing mirror guda daya. Duk da cewa wai daga bacci aka tashi amma dakin neat yake,komansa akan tsari,ga kuma wani sassanyan qamshi da yake fita kaman dai yadda falon yake.
Daya gadon da yake shine qarami ta nufa,wanda ke lullube da lallausar shimfida da tattausan blanket peach color. Tun batakai ga zama ba rurin da wayarta keyi ya cika mata kunnuwa,sai ta haye saman gadon ta lalubo wayar ta cirota daga gefan pillow dinta.
Iphone 15 ce dake dauke da wata irin cover me kyau data dace da wayar da kuma me wayar gaba daya,ta zubawa sunan dake yawo saman screen din idanu
*_ibraheem_* ya nuna mata. Wani gajeran murmushin gefan baki ta saki dake cakude da wani emotion. Siririn tsaki taja saman harshenta,ta fara qoqarin rejecting kiran
"Done and dusted.......an gama da shafinka tun a jiya" Ta fada qasan ranta tana tuna yadda al'amura suka tafi mata successful kaman yadda aka saba.
Sai data tabbatar tayo blocking ta kuma shafe duk wani abu daya shafeshi cikin wayar,bata bar hujja ko qarama ba da zata nuna tsohuwa ko sabuwar alaqa ko kuma mu'amala tsakaninta dashi ba. Ta sake bin wayar ta tabbatar komai ya koma kaman da,sannan ta duba wata ma'ajiya ta daban ta lalubi wata number ta kira ta kara wayar a kunnenta.
Bugu biyu aka daga ana sallama cikin zaquwa da zumudi
"Ina fatan saqon ya riskeki?" Tayi tambaya zuwa ga daya sashen
"Ya riskeni qwarai kuwa tun a daren jiya.......ina godiya......na gode sosai,ina me baki haquri kuma akan sabanin Fahintar da nayi miki a farko.....gashi kuma ko sunanki ma ban sani ba"
"Ba buqatar hakan......infact ma daga yau ba zaki sake samu na ko jin muryata ba......abinda na baki kiyi qoqarin tattalashi,ki kuma boyeshi daga sanin mijinki.......abu na qarshe saiki tayashi jiyya.....kinsan yadda zaki sanya masa tawakkali cikin zuciyarsa,don nayi imani ya zuwa yanzu zaiyi wahala bai zauce ba,na barki lafiya" Ta yanke kiran ba tare data barta tace komai ba,duk da tarin abubuwan fada masu yawa da take dasu take kuma son gaya matan.
Itama goge number dinta tayi ta kuma sakata a sahun sauran tarin lambobin dake akwatin katangewa dake cikin wayarta. Layinta layi ne dake da wani irin tsaro na musamman,wanda ba kowacce number da bata yarjewa bace take iya samunta. Tana da ire irensa sunfi guda ashirin,duk kuma sanda take da muradi ra'ayi ko kuma buqatar hakan ya taso tana iya sauke wanda taga dama ta dora wani.
Tana shirin shigewa duvet ta kwanta wani kiran ya sake shigo mata. Batason takura sam,sai taja tsaki tana kallon fuskar wayar.
Shine din dai,batasan me yasa ya matsa da yawa ba,bataso a yanzun akwak enough kudi a hannunta,tanaso taje hutu koda na taqaitaccen lokaci ne kafin ta fada zuwa wani agenda din.
"Tsautsayi da alama keta kiranka" Ta furta qasa qasa ta jawo wayar tana rejecting kiran shima sannan ta kashe kiran gaba daya ta jefar da wayar. Kanta ta mayar ta qudundune sosai cikin blanket din,saidai ko minti biyar bata yi ba cikakke ta miqe zumbur kamar wadda aka tsikara,ta sauko daga saman gadon tana qoqarin daure gashinta me santsi dake rufe gefan fuskarta.
Kyakkyawar drawer dinta ta bude banqaran hijabs,ta fidda wani qaramin farin hijab cikin jerin hijban da take amfani dasu a lokaci irin haka idan zata shiga wanka. Sama kanta ta zurashi,wanda wannan ya fidda kyakkyawar fuskarta tsakanin hijab din,ya kuma fidda wata sihirtacciyar kama akan fuskar tata. Towels dinta ta nufa ta zari guda daya,sannan ta matsa gefan daya drawer dinta ta jawo ta can qarshe ta fidda set na kayan wankanta dake cikin wani dan kyakkyawan kwando kaman kwandon kaba,ta rataye toweldon saman kafadarta ta fara takawa a hankali tana fita a dakin tare da sake gauke fuskarta da kyau wanda kusan haka dabi'arta take duk sanda zata fita zuwa ainihin tsakar gidan nasu,duk da dama ita din ba matum bace data cika fara'a.
Duka duka mutanen dake sabgarsu a safiyar ranar cikin sararin tsakar gidan ba zasu wuce mutum biyar ba. Dukkaninsu kuma mata ne da a shekaru suke qasa da nata shekarun idan ka dauke mutum daya dake ta bakin kitchen dinsu,zaune saman kujera 'yar tsuguno tana ta kokawa da wutar ice da take qoqarin kunnawa hayaqinta yana dawo mata cikin idanu yana sake tunzurata da hasalata.
Duk wanda suka hada ido dashi sai ya janye dubanshi daga kanta kamar yadda itama kusan haka take musu,duk kuwa da cewa wasunsu suna son tankawa a gareta kaman yadda a wasu lokutan yake kasancewa,saidai wanzuwar ta bakin kitchen din ya sanya ba wanda yayi gigin aikata hakan a cikinsu.
Bata dakata ba har ta isa bakin makewayensu da ko yaushe yake cike da tsafta da kulawa,ta xare towel din wuyanta ta azashi saman qofar bandakin idanunta nakan shaheed,yaron da aka kawoshi yaye daga gidan mahaifansa zuwa gidan kakanninsa. Yaron yayarta ne,yayarta ta kusan biyar,d'iya a wajen gwaggo mace ta biyu a wajen mahaifinsu.
Ido suka hada da yaron,sai ya sakar mata murmushi,a hankali itama ta motsa bakinta tana maida masa martani. Tana da wani boyayyen soyayya ta yara a zuciyarta,saidai zuwan yaron sai ya zame mata kamar wani mabudi ko kuma wanzuwar sabon abu da bata saba gani ba cikin gidan wato murmushi kowacce safiya a tsakar gidan mahaifinta wanda ya jima da shudewa tun bayan gushewar mahaifiyarta.
Tanason yiwa yaron magana,amma tayi imani rayuka zasu iya baci daga qarshe,dole ta kauda kai,ta sirka ruwan zafin data fito dashi ta fada wankan.
Kafin ta kammala taji masu buqatar shiga bandakin da yawa,masu qananun mitoci da qorafi duka sunayi,wasu su juya wasu su zauna suna dakonta gami da ci gaba da yasar da maganganun da tayi imanin da biyu suke yinsu kamar yadda suka saba.
Zuwa yanzu ta fara tunanin yadda zata maida qaramin dakin dake kusa da dakinsu toilet. Daya daga cikin dabi'a daya ta gidansu data tsana kenan,sharing toilet.
Gini ne irin na da wanda duk yawan jama'ar gida suna hadaka ne a bandaki qwaya daya tal!. Zata iya cewa da sauqi nasu tunda akwai wadatar tsafta.
Ko data fito babu wanda tabi takai,sai data kammala uzurinta na daura alwala a nan bakin famfo sannan ta tattaro kayanta tana barin wajen. Sai a sannan ta kallo mata biyun dake zaune daga bakin bishiyar.
Daya ta girmi daya a shekaru,saidai dayar ta dara dayan jiki. Sun kalleta sun kuma dauke idanu kamar basu ganta din ba. Ba abinda ya dameta da hakan
"Ina kwananku?" Ta furta da muryarta me laushin nan tana yin gaba ba tare da tayi koda yunqurin tsaiwa ba da salon gaisuwar da duk safiyar duniya bata daukewa kowacce cikin su ukun ba muddin zasu hadu a farfajiyar gidan.
Amsa mata sukayi kaman yadda suka saba din,can qasa suna kuma binta da wannan kallon dake dauke da tarin ma'anoni can qasan ransu,wasu.
sun furta su sun kuma bayyana,wasunsu kuwa an barwa zuciya AKWATIN SIRRI.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma*
PAGE 15
A nutse take ratsa falon harta cimma uwar dakin nasu. Duk takunta guda daya sauke qafarta da dauketa zuciyarta cike take da kewa. Wata qatuwar kewa data zamewa kowanne motsi na rayuwarta lazim. Kewa ce da zaiyi wuya ita iya barin gangar jiki. Kewar mahadin rayuwa jigon rayuwa mahadin numfashi wato MAHAIFIYA.