Showing 42001 words to 45000 words out of 51618 words

Chapter 15 - Gudun Kaddara Book 1 Hausa Novel Complete

dai"

" Ranka ya dade?,barawon mutane kuma dan fyade za'a bi a hankali?"

"A'uzubillahi" aba ya furta yana jin laifukan sunyi girma da yawa

"Wallahi yallabai,yaro da duka duka bai wuce shekara ashirin da biyar ba amma ya iya tara manyan laifuka haka,bari ka ganshi yallabai.......kai sanda,fito da yaronnan,a sake gwada bashi abinci a waje tunda yaqi ci ata ciki kada ya mace mana ya jawo mana masifa" ya fadi yana duban hanyar guraren,sannan ya dawo da hankalinsa ga littafin statement yana qananun mitoci

"Allah ya sawwaqe,Allah ya kyauta" aba ya sake fada kawai yana sauraren statement din da oncle bashar ya fara bayarwa.

Kalaman oncle bashar ne suka maqale masa a maqoshi sanda ake shigowa da maina gurin

"Uban waye ya kawo mana yaro ya daure mana shi?,uban me yayi?" Oncle bashar ya fada cikin matuqar zafi da zafin zuciya yana duban dan sandan da wani irin kallo da ya sanyashi yasha jinin jikinsa

"Ah......yallabai ai shine barawon mutanen kuma dan fyaden"

"Rufemin baki shashasha!" Oncle umar gwanin zuciya ya fada da wata mahaukaciyar tsawa

"Ku kwance masa hannu ku bashi takalmansa"

"Yallabai...... yallabai bari a kira DPO"

"Kayi hauka ne?!" Oncle umar ya sake fadi a fusace,fusatar data tabbatarwa da dan sandan lallai akwai abinda oncle umar din ya taka

"Omar......yi a hankali mana,a hukuma kake fa" aba da ya dafa kafadarsa ya fadi cikin tausasawa,kasancewarsa mutum me nisan zangon daukar zafi

"To 'yar gidan uban waye zai yiwa fyaden?,uban waye kuma ya sata?,wanan da alama baisan FAMILYN MAYAK'I ba" Oncle umar ya sake maimaitawa a fusace yana duban aba

"Ka bari dai ayi komai a nutse......yallabi ku kira DPO din"

"Okay sir" dan sanda da jinin jikinsa ya kusa daskarewa tunda aka furta mayak'i family ya fadi da rawar jiki yana saluting aba,don sai a sannan hankalinsa ya dauko masa hoton fuskar waye aba din.

Har dan sandan yaje ya musu iso wajen dpo ya dawo maina baice komai ba sai kansa dake qasa,duk kuwa da tambayoyin da oncle umar keta jero masa

"Ka gani ko yaya?,baya magana fa,Allah muddin wani abu ya sameshi dasu da wanda ya kawoshi nan din sai ya raina kanshi"

"Muje dai Omar " aba ya fadi yana sanyasu a gaba.

Aba din yana shiga DPO din ya miqe cikin mamaki

"Barka da zuwa yallabai,yau kaine da kanka a office dina?,bismillanku" murmushi kawai aba din yayi,yaja kujerar ya zauna sannan su oncle bashar suka zauna,banda maina dake a tsaye bashi da ko alaman tsaiwa,don bai qaunar dogon zama sam cikin office din mutumin,shi daya yasan me yakeji a zuciyarsa,shi kansa din ma bazai iya tantancewa ba. Bayason kallon fuskar mutumin sam,saboda tana tuna masa da mummunar lafazin da suka jefeshi da shi shida sultana,tana tuna tozarcin da yayi masa irin wanda ba'a taba masa irinsa ba tunda ama ta kawoshi duniya

"Kada dai ace wannan yaronka ne?" Dpoya fada yana nuna maina

"Eh yarona ne,nazo kawo cigiyarsa kuma muka sameshi a nan"

"Subhanallahi" tiryan tiryan ya gaya musu yadda komai ya faru,sannan ya dora da cewa

"Yaqi bayani ne yaqi fadin komai,ko kare kansa wallahi yaqi yayi,bansan ba mara laifi bane tunda baiyi yunqurin bawa kansa kariya ba"

"Amma yarinyar wace a ina kuma take?"

"Bansani ba tunda baiyi bayani ba amma dai ga unguwarsu ga kuma hotonta mun ajjiye report saboda gaba" ya fada yana miqa musu wani file

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,sultana ce,'yaruwarsa ce ai,'ya take a wajensa" oncle bashar ya fadi,yayin da aba da kuma oncle umar suka bushe a wajen suka kasa cewa komai.

Shuru dakin ya dauka na wasu sakanni,a nutse aba ya daga kai ya dubeshi

"Meye ya hada haka da ita?,a ina ka daukota?" Sai a sannan yadan motsa kadan daga tsaiwar da yayi kamar an dasa itacen bishiya,rayukan 'yan maza ne a dugunzume ainun. Dpo din ya fahimci muddin yana wajen bazaiyi magana ba,su dinma sun fahimci hakan,saboda haka oncle bashar yace

"Maganar nan ta gida ce yaaya"

"Gaskiya dai" DPO ya fadi. Dukkansu cikin mamaki da juya lamarin suke dukka su ukun,har zuwa sanda DPo da kansa ya rufe case din,ya kuma tattara musu dukkan wani document da ya shafi case din suka fice da shi.

Ba wanda suka yiwa bayanin inda suka samoshi,saidai oncle umar daketa banbamin fada kaman zai ari baki,daga qarshe kuma

"Zataci qaniyarta sultana wannan karon" har yanxun maina din bai cewa kowa uffan ba,don bayajin bakinsa zai budu har wasu kalamai su iya fita.

Jikinsa dukka radadin cizon da sauro ya kwana yana masa a jiya,uwa uba tsabar tsantsami ya sanya yake masa qaiqayi jikin nasa,don haka ya hada ruwa me zafi yayi wanka bayan ya watsa kayan jikinsa a dustbin,duk tsadarsu bayajin zai iya sake amfani dasu.

Shi daya suka bari a shiyyar tashi,don yace yanason ya kwanta ya huta,ko abinci da ama tayi masa tayi cewa yayi baici ya qoshi. Da gaske bayajin abincin zaibi ta maqoshinsa,da bibi ma ta aiko dashi sawa yayi aka maida mata,ya rufe qofofinsa ya kwanta yana fatar yayi baccin da bai samu yi ba a daren jiya.

Bayan ya kwanta din labari ne yasha banban. Duk inda ya runtse idanunsa ya juya ba abinda idanu da kunnuwansa ke jiye masa sai kalmar SATONI YAYI,FYADE ZAIYIMIN.

"la haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" ya dinga maimaitawa. Futucin yaqi barin kunnuwansa......Ga tarin mamakin sai yaji wata siririyar qwalla na fito masa ta gefen idonsa guda daya.

Hannu ya sanya ya shafosu yana kalla,shi kam iya tsahon wayonsa da girmansa ya mance yaushe ne lokaci na qarshe da ya ga hawaye cikin idanunsa haka. Duk da ya karbi horo na sajoji masu matuqar wahala da azaba,amma basu taba sakashi dar ba bare damuwa har akai ga qwalla,sai gashi yau furucin sultana ya karya zuciyarsa har haka?.

Haka ya wuni ya kwana,saida tursasawar ama yaci abinci zuwa dare

"Wai ina ka bace?,me sameka da wannan mummunar damuwar take bayyana kan fuskarka?" Ta tsareshi da tambar tana kallon fuskarsa. Har ama din tayi ta gama itama bata samu amsa ba hakanan ta haqura tunda ta samu yaci abincin.

Sultana kuwa tunda taji yaa maina ya dawo gida ta koma tamkar kazar da aka jefa da wuqa,wato kenan tasan wa'adin kwanakin rayuwarta a duniya qididdigaggu ne. Dukka saita tsargi kanta,ta rasa dukkan wani sukuni da walwala,ta yiwa kanta iyaka da kuma shamaki iya dakinta kadai.

Tayi tsammanin games dinta da su nini zasu debe mata kewa,amma kowanne sai taji baya yi mata dadi,idan ta dauko game din sai taji batayi mata ba saita watsar,idan ta dauko nini din ta rungumeta kaman yadda takeyi a baya sai taji ta isheta itama saita ajjiye ta koma ta kwanta. Haka ta dinga juyi kafin daga bisani aminata da lamira suka leqo suna mata dariya tare da sake gaya mata tabbas ya maina fa ya dawo

"To sai me?, mala'ika ne shi?,yayita dawowa,nidai ko banza ai an rama min marina" ta qarashe fada tana murguda baki sannan ta juyar da fuskarta zuwa bango abinta.

[4/18, 10:43 PM] C.E.O HUGUMA CLOSET: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Page 24


Ko washegari wani irin sukuku ta tashi,babu wannan dan banzan surutun da rawar kan da take damun bibi dashi. Komai da takeyi bibi din tana ankare da ita,haka kawai ta dinga jin zuciyarta kwata kwata babu nutswa. Duk motsin da sultana tayi idanunta yana kai. Tare sukayi breakfast da sultana din abinda ba kasafai yake faruwa ba,bayan sun gama suna zaune dai a falon suna kallo,saidai kowa da abinda ke cikin jiki da zuciyarsa.

Da muryar nan tasa dake da wani irin zurfi me cakude da kwarjini yayi sallama cikin falon bibi din. Yau din yana sanye da wasu fararen hoodie and jogger pants da ratsin gray color. Fuskar nan na fidda tsananin kwarjininsa da haibarsa, qamshin turarensa me sanyin qamshi da bashi da damuwa ko kadan ya game ko ina.

Sallamar tasa tayi daidai da miqewar sultana cikin sauri daga saman cinyar bibi. Zumbur kamar wadda aka tsikarama wani kakkaifan abu saman qahon zuciyarta. Idanu ta kafeshi da shi gabanta na bada sautin bugu,shima da idanun ya kafeta,lion eyes dinsa dinnan dake azabar cika mata idanu. Kallon da a yau ya dasa mata wani mugun tsoronsa,kalamansa kuma suka sake dawo kata fes saman kai kamar yadda suka dinga yi mata kai komo a qwaqwalwa.

Yadda suka kafe juna da idanu haka bibi ta kafe maina din da ido. Gabanta nason faduwa zuciyarta na ayyana mata abubuwa da dama. Meye dalilin irin wannan kallo da yakeyi mata haka?. Zuciyarta yanzun bata da tabbas akan maina,duk wani motsi nasa a yanzun abun ta sanya masa ido ne.

Idonsa ya dauke daga kan sultana din yana qarasowa cikin falon. Ba abinda ke dawo masa a rai irin qarfin halinta da kuma taurin zuciyarta,ta yadda har ta iya kaishi ga kwana a policestation,wannan wanne irin hadari ne da ita?,a wadannan shekarun nata da duka duka idan aka kacaccalasu gida uku baifi ta tsira da shekaru qwara hudu ba?,me zai faru a nan gaba muddin dai tana da irin wannan zarrar?.

"Barka da safiya bibi" ya furta yana zama daura da ita,abinda ya sanya sultana sake kame jikinta guri guda kenan,ta kuma lanqwasa qafafunta tana maqalewa jikin bibi,har yanzu idanunta qur a kansa,tana jin kamar ma kowanne motsi idan yayi zai iya zama cutarwane a gareta. Bata sake kuma shiga matuqar tsoro ba saida bibi ta zaunar da ita a daxu bayan sallar asubahi tayi mata irin fadan da bata taba yi mata makamancinsa ba,ta kuma gaya mata meye ma'anat fyade da har zata yiwa dan uwanta mummunan qazafi da shi,illarsa da yadda yake taba rayuwar diya mace. A lokacin ta sakejin jikinta yayi mugun mutuwa,ta kuma sake jin mugun tsanar maina da tsoronsa. Banda haka duk da sanin illarsa shi da yayi din amma yaci alwashin sai yayi mata?,dama ashe shi din DAN ISKA ne bata sani ba?. Tayi furucin fyade ne saboda gani data taba yi wata jaruma tayi cikin shirin film,kuma ta samu kubuta daga hannun jarumin.

"Lafiya qalau" bibi ta amsa masa da salon amsa gaisuwar da ba irinta suka saba ba

"Tashi ki bamu guri" maina ya fadi yana maida dubansa ga sultana dake masa kallon Allah ya tsine uwar me qarya,kallon da yayi kama da kallon ban sanka ba, yau na fara ganinka

"Ki nemi hijabi ki saka" bibi ta fada tana bin sultana da kallo wadda ke sanye da wando da 'yar Short sleeve shirt wadda ta bayyana santala santalan damtsenta. Maganar ta sanya hijabin sai maina ya gaza fahimtar me ma'anarta?,da bai gane ba sai ya share batun ya dubi bibi din bayan sultanan ta iske daki

"Haquri nazo na baki akan furucina na jiya,kiyi haquri,ba kuma ina nufin hakan har raina ba,kuma ba zan sake lafazi makamancin wannan ba" idanu bibi ta gwalalo tana dubansa

"Wa?,ai tsohonka kadai nake jira ya dawo yayi mana shamaki,ni zaka yaudara aliyyu?,kaman bansan halinka ba?,kafiya taurin kai da naci akan dukkan abinda kace zakayi?,ni zaka yaudara da kalaman ban haquri?, tabdi.....bazan taba yarda ba" bibi ta fada tana kada yatsanta dan manuni.

Shuru kawai yayi yana kallonta har ta kammala,sai yadan lumshe idonsa ya bude yana dubanta,can qasan maqoshinsa yana qoqarin hadiye bacin ranshi,donshi a son ranshi banda bin umarnin ama ma bazaizo wani bata haquri ba saidai aje a haka

"Ki yarda dani,da gaske nake baki wannan haqurin bibi" ya maimaita yana kafeta da ido. Dubansa tayi cikin idanu na wasu sakanni,kamar zatayi magana sai kuma ta fasa,ta juye da rufeshi da masifar da yayi imani sultanan ya kamata ta yiwa ita amma tazo shi ta balbaleshi da ita.

Har tayi ta gama bai sake ce mata kanzil ba,sai data sauke sannan yace

"A bani breakfast"

"Yau bamuyi da kai ba"

"Nasan hanyar kitchen" ya fada yana miqewa hadi da gyara zaman rigar jikinsa ya soma takawa

"Kaga,nifa yanxu ina da diya mace da nake raino nan sashen,ba kowanne lokaci ya kamata ma ka dinga shigomin ba,ko zaka shigo ma ka dinga neman izini saboda mu kintsa" cak ya dakata da tafiyar,ya waiwayo yana duban bibi din yana jin maganar nayi masa banbarakwai.

Wata irin dariya mara sauti ce ta subuce masa,sai kawai ya cije lips dinsa yana kada kai. Wai dukka akan sultana take gaya masa haka?,sultana ce wai har za'a kira budurwa?,sultanar da tasan hanyar club tasan hanyar hotel wai yanxu ita akewa kaffa kaffa?,bama haka ba.....shi tasa lalacewar ma ta rasa ina zata qare sai akan wannan qaramar halittar?,ya baro manyan mata da komai yaji a hostel,suna kiransu ma free of charge,matan abzinawa,shuwa da fulani masu shegen kyau da baijin duk kyau irin na sultana zata bude musu idanu tunda nata bai riski 'yammatanci ba,su basu tsone masa idanu ba sai sultana?.

Har zai biyewa bibi din sai yaga ma bashi da lokaci,ya sanya kai kawai ya wuce kitchen din abinsa.

Har ya cinye asabar da lahadinsa baima sake haduwa da sultanan ba. Litinin da sassafe ama ta sakashi a gaba akan ya koma. To shi dinma dama ranar yayi niyyar komawar,don haka ya tattara ya nasa ya nasa ya koma din.

Kamar jira sultana din takeyi dama ya tafi sai ta warware ta koma halayyarta. Sau tari idan ama na veranda dinta tana hangenta ta farfajiyar gidan tana wani iya shegen saidai kawai taja tsaki

"Allah ya shirya". Tana hangen abubuwa da yawa da yarinyar ke dashi wanda sauran sa'aninta a gidan basu dashi. Amma mugun gata da saken da ake bata a gidan ya hana komai ma tasiri.

Bata sake shiga taitayinta ba sai ranar da ya sake zuwa hutun kwanaki uku. Shi zam baima wani lura da yadda take mugun gudunsa da d'ari d'ari da shi ba sai a wannan zuwan da yayi,d'ai d'arin da shi baima fahimci akan meye takeyi ba.

A hankali bibi ta fahimci komai,rashin sakewar sultana din a duk sanda akace yau maina ya sauka a gidan,abunda ya dinga taba ranta kenan,ta dinga jin babu dadi. Hakanan zuciya ta dinga yi mata saqe saqe kala daban daban cikin ranta. Kwata kwata itama bibi din sai ta dinga rasa nutsuwarta idan yana nan din,a hankali itama sultanan saita daina kwana dakinta duk sanda maina yake gari,idan kaga ta koma dakinta to baya nan ne ya koma makaranta.


*********K'arfe hudu na yammacin ranar,ranar da gidan ya kasance akwai qarancin jama'a,saboda kusan duka yaran gidan sun wuce islamiyya idan ka dauke sultana dake kitchen din bibi a dai dai lokacin. Oat takeson sha amma kuma tanja bata kusa,ita kuma baya ga tanja din bata yarda kowa ma yayi mata komai a gidan sai bibi. Bibi a lokacin bacci take,ita kuma ta matsu da tasha din,abinda ya sanya ta shiga kitchen din kenan ta dinga hada kwabarta.

A qalla babban gwangwanin oat da qatuwar gwangwanin madara ta kusa juyewa cikin bowl,ta kammala tayi tsaye riqe da qugunta tana tunanin yadda zata tafasa ruwan zafi. Tana dari dari saboda tana tsoron wuta,tana kuma iya tuna yadda ruwan zafi ke mugun tururi duk sanda tanja ta saukeshi daga saman gas.

Bacci yayi me nauyi a yau din,saboda muguwar gajiyar dake jikinsa sakamakon training da sukayi duka wancan satin babu hutu,wannan dalilin ya sanya yana samun interval na kwanaki a wannan satin yayo gida,yasan a nan dinne kawai zai huta sosai,kanshi yayi fresh yadda ya kamata,babu me takura masa,koma bayan hostel da ba lallai su sultan su barshi ya huta ba su da gayyar abokansu.

Dispenser dinshi babu ruwa ciki,don haka ya zura jallabiyyarsa me sulbi 'yar marocco ya sauko ya fito daga dakin.

Tun azahar yasan ama bata nan,don tana da taro na musamman a qungiyarta data bude don taimakawa mata iyayen marayu da zauwara,wannan dalilin ya sanyashi wucewa kai tsaye sassan bibi.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login