Showing 129001 words to 132000 words out of 148918 words
okay? why are you crying?" Kallon matar kawai Nihad take hawaye na sauka idonta kuma taki ce mata komai, wannan ba ita ce ta gani a hoto ranan a dakinsa ba? Mami tace "C'mon, come in dear...." Nihad taki karasowa sai kallonta take, Mami na ganin haka ta juya ta koma dakinta ta shiga tana kallon Khalil dake kwance saman gadonta da mamaki tace "Khaleel na ganta tsaye bakin kofa tana kuka, is she okay? Nace ta shigo kuma ta ki" Mikewa Khalil yayi ya fita parlon Mami ta bi bayansa, yana kallon Nihad, ya dake yace "Shigo ciki" Mami ta karasa inda take tsaye ta kamo hannunta ta shigo da ita parlon tana kallon Khalil murya can kasa tace "Doesn't she understands English?" Bai ce komai ba ya juya ya koma dakin, Mami ta zauna gefen Nihad da ta zaunar edge din kujera kamar me shirin fillawa da gudu, tace "Ya kike yan mata?" Nihad ta goge idonta tana kallonta a hankali tace "Ina yini" Mami na Murmushi tace "Alhamdulillah, ya su mamanki?" Nihad ta sauke idonta kasa cikin sanyi tace "Lafiya lau" Haka kawai Nihad taji hankalinta ya ɗan kwanta ganin Mami, Mami ta kwantar da murya tace "Ki saki jikinki kinji, nan ma duk gida ne" Nihad ta kasa ce mata komai, Mami tace "Kin yi sallan magariba?" Nihad ta girgiza mata kai, Mami tace "To ga banɗaki kije kiyi alwala, bari in kawo maki darduma a bedroom yanzu" Nihad ta mike ta tafi kofar da Mami ta nuna mata a parlon ta bude a hankali tana kallon ciki, bandakin ya kusa girman dakinta, ta karanto addu'ar shiga banɗaki a ranta sannan ta shiga, Mami ta mike ta tafi daki ta ga Khalil ya dauro alwala ya fito, area din da Mami tayi demarcating a dakin don yin sallah ya nufa, Mami ta dau ma Nihad darduma daya ta kai parlor ta shimfida mata, sannan ta koma dakin ta shiga bandaki ita ma ta dauro alwalan, Khalil na zaune saman darduma yana azkar bayan ya idar da sallah, Mami ta mike bayan ita ma ta idar tana kallon side din da yake tace "Yanzu abincin xan dauka in kai can parlon, ko ta shigo nan kawai ku ci?" Yace "Ki deba kawai ki kai mata can parlon Mami" Mami tace "Ai ban san abinda tafi son ci ba, kawai bari ta shigo ta yi serving kanta ko?" Mami na fadan haka ta fita zuwa parlor tana kallon Nihad dake saman darduma tayi kuri da ido tace "Baby shigo ki ci abinci" Nihad ta mike a hankali ta tafi kofar dakin ganin taki shigowa Mami tace "Shigo mana" Cikin sanyin murya tayi sallama ta shiga dakin, ta dinga bin abincin dake jibge a kasa da kallo kamar za ayi party, Mami tace "Ki duba duk abinda kike so ki diba" Mami na fadan haka ta fita daga dakin, Nihad ta durkusa tana kallon Khalil, murya can kasa tace "Don Allah ina ne nan ka kawo ni?" Sai a sannan Khalil ya kalleta tun da ta shigo dakin yace "Inda za a mana alfarma ba tare da an walakanta mu ko an ci zarafinmu ba, ba kuma tare da an damu da mu talaka ne ko masu arziki ba" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike ya zauna gefen gadon yace "Debi abinda zaki deba ki fita" Ita dai ta kasa cewa komai kuma ta kasa bude ko warmer daya balle ta zuba abincin, Mami ta dawo dakin rike da teapot da cups dinsa biyu a tray, da mamaki ta ke kallon Nihad bayan ta ajiye tray din hannunta tace "Baki debi abincin ba" Sai kuma ta kalli khalil kafin tace komai ya kirkiri murmushi yace "Haka take Mami" Nihad ta daga kai ta kallesa, Mami tace "But why? pls tell her to feel free" Khalil ya maida idonsa kan tv dake aiki silently bai ce komai ba, Mami ta dau plate ta debar ma Nihad shinkafa da miya ta ajiye mata, ta debar mata duk wani abu da xata dibar mata sannan ta mike, Nihad dai bata ta6a jin she is confuse kamar yanda take ji yanzu ba, gaba daga kanta ya kulle ta kasa fahimtar komai, lkci lkci sai ta kalli khalil sannan ta kalli Mami, Mami na kallon Khalil a hankali bayan ta gama zuba ma Nihad abinci tace "When did you say he called you?" Khalil ya kalleta duk da ya gane wanda take nufi yace "Ke baxa ki ci abincin ba Mami? Ki zuba mana tare mu ci" Mami tace "Talk to me son, he is back now" Sai da gaban khalil ya fadi ya mike yace "Really? But hope you didn't...." Sai kuma yayi shiru, ta gefen ido ya kalli Nihad da ta kafesa da ido babu ko kiftawa, sai kuma ya fice daga dakin, Mami na kallon Nihad da murmushi fuskarta tace "Ki ci abinci kin ji Baby" Daga haka ta juya ta bi bayansa, Nihad ta bi su da kallo bata kwakkwaran numfashi, bayan kusan minti sha biyar Khalil ya dawo dakin shi kadai, har sannan Nihad na zaune position din da take kamar warce ruwa ya cinye, gaba daya jikinta yayi sanyi qlau kana mata kallo daya zaka gane hakan, Ta bi sa da kallo har ya dau teapot da cup zai fita, cikin sanyin murya tace "Ka gaya min, wanene kai?" Bai yarda ya kalleta ba yace "Driver!!" Daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da ido babu ko kiftawa, abinda ya fada dazu da turanci ne ke kai komo a ƙwaƙwalwarta, lokaci daya ta runtse ido ko zata samu saukin sara mata da kanta ke yi. Khalil na zaune parlor sai ga Mami ta shigo tana kallonsa, shi ma kallonta yake, a hankali tace "Kaje wajen Abbanka, yana kiranka parlonsa" Khalil ya kalleta looking so worried yace "Mami da baki ce masa na dawo yau ba" Mami ta girgiza kai tace "I never told him, tun daga gate ya tambaya securities, su suka sanar masa kana gidan nan....." Yayi kasa da murya yace "But bana son kowa ya san am around Mami" Mami tace "Zaka iya zagawa ta baya ai, har yanzu babu wanda yasan kana gidan nan" Mikewa yayi ya nufi kofa yana tafiya a hankali ta bi sa da kallo har ya fita.
Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and ur evidence via👇🏻
07087865788
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549
Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
Khalil na shiga parlon Abbansa bai bari suka hada ido ba, yana tafiya a hankali ya zauna saman lallausan Carpet dake kasa, yayi gathering courage yace "Barka da dare Abba" Shirun da Abban nasa yayi yasa a hankali ya daga kai ya kallesa yaga jaridar hannunsa kawai yake dubawa, ya sunkuyar da kansa, bayan kusan minti biyu Abba ya ajiye jaridar hannunsa yana kallonsa a takaice yace "Wani international joint ventures na wata daya zaka min handling a Zanzibar, and the business isn't new to you, you know everything about it, so u can chose to stay there in Zanzibar or come back to Nigeria weekly, bayan kayi min sorting komai zaka iya komawa duk inda ka fito ka ci gaba da rayuwarka since it's the best for you and you are okay with it, i will neva beg you to come stay here!!" Yana gama fadin haka ya mike ya shiga dakinsa Khalil ya bi sa da kallo, sai gashi ya fito da files ya jefa masa nan kasa yace "Everything u will be needing is there, u can leave my sight now" Khalil ya dau files din a hankali yace "In sha Allah, Nagode Abba" Daga haka ya mike ya nufi kofa Abban nasa ya bi sa da kallo har ya fita, yana fita ya juya suna hada ido da Abba, Abba yayi saurin juyawa ya shiga bedroom dinsa. Har Khalil ya shigo parlon Mami na tsaye ta kasa zaune sai kai komo take a dakin, she is so disturbed and worried, Allah ya sa kiran alkhairi yake masa, tana ganin Khalil ya shigo ta nufesa da sauri tace "What did he say to you??" Khalil ya mika mata files din hannunsa ta amsa tana dubawa da sauri, can ta kallesa tace "What about this?" Yace "He wants me to be in charge" Mami ta dinga Kallonsa babu ko kiftawa can tace "He said so?" Khalil yace "Yea" Murmushi tayi ta rungumesa tana hamdala a zuciyarta amma ta kasa cewa komai hawaye ya cika idonta, ta sakesa tace "Yanzu yaushe zaka tafi?" Khalil yace "I need to prepare" Tayi kasa da murya da damuwa tace "Zan so ka shirya first thing in the morning ka bar gidan nan kafin wani yayi noticing dinka, har yanzu basu san u are around ba, nasan shi ma bai sanar masu ba" Khalil bai iya yace mata komai ba, ta goge idonta tace "Shigo ka ci abincin yanzu, i am so happy at this good news" Ta kama hannunsa suka wuce can bedroom dinta, tsaye tayi bakin kofa da mamaki tana kallon Nihad da ko motsi bata yi daga inda take ba balle ta ta6a abinda Mami ta zuba mata a gabanta, Mami ta kalli khalil tayi kasa da murya tace "Are you sure zata yarda ta kwana nan son? She hasn't taken anything yet, are sure baxaka duba ko da akwai flight going to kano a yankar mata ticket ba?" Khalil dai sai kallon Nihad yake, Mami tace "Do so before it's late plss, kasan wasu nature ne hakan basu sakewa a wani waje ba gida ba, so kar a takurata" Juyawa tayi ta fita daga dakin, khalil ya duka dab da ita yana kallonta, kin yarda su hada ido tayi, lkci daya yaga hawaye ya ciko idonta, still looking at her yayi kasa da murya yace "Where u offended in anyway?" Ta kallesa sai kawai ta fashe da kuka sosai, cikin karfin hali tana magana da kyar tace "Don Allah... Kayi hakuri ko a motor park ne ka kai ni ka sa ni a motar Jigawa in tafi wajen Aunty Jamila, don Allah kayi min wannan last alfarman" Tana kuka me ban tausayi ta fadi hakan, sai kuma ta hade kanta da gwiwa, yana ta kallonta kafin yace "An maki wani abu ne a nan din da za ki tafi jigawa?" Ta daga idanuwanta da hawaye ke zuba tana girgiza kai tace "Ni bance an min komai ba" ya dau duk abincin da Mami ta sa mata a plate ya kai parlor sannan ya dawo yace "Fito ki ci" Tace "Ni na koshi" Yace "Fito nace" Mikewa tayi trying hard not to burst into new cry ta fito daga dakin ta tafi ta zauna inda ya ajiye abincin, ta hadiye wani abu da ya tokare mata throat da kyar, Yana kallonta yace "Now eat" Bata san sanda kukan ya subuce mata ba tana girgiza masa kai, ya hade rai yace "Kee" ta daga ido da sauri ta kallesa, ya durkusa yana kallonta, sai kuma ya ciro handkerchief ya mika mata, Da sauri ta sunkuyar da kanta, ganin har sannan mika mata handkerchief din yake ta kai hannu a hankali ta amsa, ta goge hawayen da ke zuba idonta da shi shi dai kallonta kawai yake, bayan ta gama goge idon ta daga kai a hankali tana kallonsa, ya sauke idonsa ya matsar da plate din abincin gabanta, ta kalli cokalin dake cikin abincin ta dauka ta diba ta kai baki a hankali ta fara ci, mikewa yayi ta bi sa da kallo har ya fita zuwa next parlor din, gaba daya taji baxata iya cin abincin ba, she has clearly run out of appetite, this is the third shock of her life so far, but this particular one is so strong and it's about giving her heart attack, of all the shock, this made her felt bata da sauran hope a duniya, this made her loose all hope, she now believe she is now all by her self a duniyan, kwakkwaran wata daya ba ayi ba ta girgiza da lamari har kala uku, yanda take ji a ranta ta kara tabbatar da bata da wani sauran gata kuma a duniya, ganin komai take kamar mafarki amma ita dai tasan ba mafarki take ba, this is nothing but reality, bata ta6a jin ta tsani kanta duk abubuwan dake faruwa ba sae yau, she hate herself for everything so far, ta daure ta tashi da kyar ta mayar da duk abincin cikin warmer dinsu ta fito don tasan baxata ta6a iya ci ba, ta zauna kasa ta jingina da kujera, ko sanin hawaye na zuba idonta bata yi ba. Khalil na zaune first parlor da Maminsa dake waya da sister dinta, she is happily telling her that he is back, daga nan kuma ta kira aminiyarta warce kasar su daya and she is always there for her at all time, shi dai khalil kallonta kawai yake har ta katse wayar, Mami ta mike tace "An samu jirgin kuwa son?" Ya girgiza kai yace "Aa Mami" Tace "Toh gobe first thing sai kayi mata booking ticket kafin ka tafi koh?" Khalil bai ce komai ba, Mami ta koma can ciki, ba a dau lokaci ba sai gata da plate din abinci ta zubo masu, tare suka ci abincin, ya ci peppered chicken din kawai a maimakon pepper soup yace mata ya koshi, Mami ta kira Bilkisu ta kwashe duk abubuwan ta fita da su daga part dinta. Karfe tara da rabi Mami ta shigo parlon da Nihad take tana kallon Nihad tace "Toh ki tashi kiyi wanka don ki ji dadin jikinki ko?" Nihad ta mike tsaye ba tare da ta bari sun hada ido ba, Mami dai sai kallonta take, ganin ta nufi kofa tace "Ga bandaki nan a bedroom" Ta girgiza kai tace "Zanyi a na parlor" Daga haka ta fita daga parlon zuwa daya parlon wanda bandakin ke ciki, tayi hakan ne sbda la'akari da tayi da Mumynta, bata sharing bathroom din dakinta da kowa, khalil dake danna waya ya daga kai ya kalleta, tun da ta kalli iphone din hannunsa bata sake kallon direction din nasa ba, yaga ta shiga bandaki, Mami ta shigo parlon ta kirasa ya mike ya bi bayanta, suna tsaye parlon farko tace "Toh yanzu a haka da taki sakin jiki zan kai ta bangarensu Mimi?" Yace "Aa Mami ki yi mata shimfida kawai a parlor nan ta kwanta" Mami tace "Aa haba dai, ya zata kwana a parlor, abinda yasa kaga bance zata kwanta nawa bedroom din ba i am leaving it for you kai ka kwanta, ni zan je in kwanta wani wajen" Yayi Murmushi yace "Aa Mami ba sai kin bar min gadonki ba, kawai ki kwanta ni zan kwanta parlor, kema kinsan i prefer sleeping on the couch" Tace "Toh shikenan sai mu kwanta da ita a daki, let me get her sleeping dress wajensu Mimi...." Daga haka ta fita sai gashi ta dawo da sabuwar rigar bacci na Noor ta kai dakinta ta ajiye ma Nihad a gefen gado da tsadaddun spray biyu sannan ta fito, Nihad na fitowa daga wankan taki shiga dakin, shi dai yana ta danna wayarsa, ta rakube jikin kujera, Mami ta fito parlon zata ma Khalil shimfida, ganin Nihad a rakube tace "Baby shiga ciki ki shirya, za ki ga sleeping dress da turare na ajiye maki saman gado" A hankali Nihad tace "Nagode" Daga haka ta shiga dakin, Shimfida me lafiya Mami tayi ma Khalil a parlor na biyu, shi dai bin ta kawai yake da kallo, yasan yayi kewar Maminsa fiye da zatonsa, he so missed all this, har bedroom dinsa Mami kan shiga ta gyara masa back then, tana gamawa ya mike ya nufeta yayi mata side Hug cikin sanyin murya yace "Thanks Mamina" Tace "Ai kai ma zaka yi wankan ko?" Yace "Sure" Tace "Let me get u ur pajamas" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo, sai kuma yayi murmushi ya shiga dakinta don shiga banɗakinta yayi wankan, zaro ido Nihad tayi ta rufe jikinta da kayan baccin da take kokarin sakawa ta durkusa kasa da sauri ta rufe fuskarta, ya sauke idonsa ya juya ya fita daga dakin, bandakin da tayi wanka ya shiga kawai, Mami ta ajiye masa pajamas din saman inda tayi masa shimfida bayan ta dawo ta tafi dakinta, dariya Nihad ta bata ganin yanda ta rakube kasa jikin dressing mirror bayan ta saka kayan baccin, Mami tace "To tashi ki hau gado ki kwanta" Nihad ta kalleta da sauri cause she never expect it, can tace "Aa zan kwanta a kasa" Mami tace "Common hau gado kiyi kwanciyar ki Baby" Shiru Nihad tayi sai kuma ta mike a hankali ta tafi ta hau saman babban bed din wanda furnitures dinsa kadai ma abun kallo ne, Mami ta dago mata duvet ta mika mata ta amsa ta rufe jikinta ɗon dakin yayi sanyi ta dalilin Ac dake kunne. Har kusan karfe dayan dare Nihad bata ga bacci ba,