Showing 126001 words to 129000 words out of 148918 words
u are taking first or the cow leg pepper soup?" Kallonta kawai yake ya kasa cewa komai, lkci daya jikinsa yayi sanyi, he knows he missed all this, ta fashe da kuka ta rungumesa tace "My prayers was always with you son, i know i have missed u a lot, i just had nothing to do about it" Kuka take sosai, ya runtse ido yace "Pls ki daina kukan nan Mami, i was fine and comfortable all through, kawai dai na kan yi kewanki da kannena sosai hakan ne kadai ke samin damuwa" Mami ta sake sa ta sauka ta fara zuba masa abincin iri iri a plate, shi dai kallonta kawai yake, bayan ta gama zuba masa tace "Ka ci duk abinda kake son ci sai kayi wanka son, let me get u what to change" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, fadawa yayi saman gadon, gaba daya hankalinsa ya tafi kan Nihad da ya bari ita daya a dakin hotel, from where will he start convincing his mami har ta hakura ta bar sa ya fita?? Not even that, don kuwa wannan me sauki ne, now!! from where is he going to start explaining to Mami cewar ai an masa aure? Ta yaya zai fara mata wannan gagarumin bayanin and how will she even take it balle uwa uba Abbansa, tunanin hakan scent cold all over his body, ya mike zaune a hankali yana jin wani sanyi na shigarsa sosai, tun barinsu kano hankalinsa bai tashi haka ba sai yanzu, ta ina zai fara wannan bayanin yace ai an masa aure wanda shi ma ba da son ransa ya amshi auren ba, Yaya iyayensa da relatives dinsa da ma yan uwansa gaba daya za su dauki wannan babban lamarin, aure without his parents consent, this now is his biggest challenge so far, rike kansa yayi bayan yaji kansa ya wani tsara masa, After some minutes Mami ta dawo dakin da kayansa da ta saka a leda don ma kada wani ya gani, kannen Khalil kuwa duk ta hanasu zuwa ɓangarenta a sunan she is not okay and she needs privacy, da sauri khalil ya dago bayan Maminsa ta shigo dakin, ganin bai ta6a abincin ba da damuwa tace "C'mon pls ka sauko ka ci abinci Khalil kar ya huce, ko dai akwai wani abun dake damunka har yanzu..." Khalil ya dinga kallonta yana tunanin ta inda zai fara, can dai yayi karfin halin cewa "Mami na ji kince baxan fita ba, kuma fitan da xanyi yanxu is very urgent" Mami ta zauna kusa da shi cikin rawar murya tace "I am afraid baxan sake ganinka ba kuma Khalil, kilan idan ka fita baxa a sake barin ka shigo gidan nan ba, i can't..." kawai sae ta fashe da kuka tana girgiza kai cikin tashin hankali tace "Haka jikina ke bani, i can't endure loosing u for the second time son, ban san me zai faru da ni ba idan hakan ta kasance, me xaka fita kayi Plss?" Ya sauke idonsa da ya kada, bayan few seconds cikin sanyin murya yace "Mami gidan da nake zama a garin kano da nace masu zan taho Abuja yau sun hadani da er su muka taho tare da ita, zata karbi admission letter dinta a wani makaranta da tayi applying a nan, she knows nobody in here Mami, kuma har yanzu tana makarantar tana jirana" Mami tace "Oh my God, is that so?? Allah sarki, bari in kira driver sai ka bani numberta in tura masa yaje ya daukota yanzu" Khalil was shocked at what she just said, Mami ta mike da sauri xata dauko wayarta ya bi ta da kallo, can sai gata ta dawo kafin ta kira Drivern yayi saurin cewa "Mami she is just a young girl, bata da waya a hannu, dama sai xata fara karatun ne za su bata waya, kawai ce mata nayi zan zo in dauketa a makarantar later" Mami dake kallonsa tace "Toh ka fadi inda kace ta jira ka a makarantar mana in kira Drivern in sanar masa yaje ya daukota, why are you making this a big deal son??" Khalil ya kamo hannunta a hankali yace "Mami tsoronki kada in fita a hanani shigowa a bakin gate ko? but trust me ya sanar masu zan zo ya kuma masu izinin barina in shigo shi yasa har suka barni na shigo, idan da ba haka bane da baxan ta6a shigowa gidan nan ba" Mami ta fashe da kuka tace "Bana son kowa yasan ka dawo Khalil" Khalil ya girgiza kai a hankali yace "Mami, surely in dai yan gari xai tambayesu ko na zo kuma za su sanar masa na zo ina gidan, kiyi hakuri in je in daukota yanzu in dawo Mami, i promise you ko awa daya baxa ayi ba zan dawo" Mami dai tayi shiru tana goge hawayen dake ta sauka idonta, sosai zuciyarsa ya karaya ganin yanda Maminsa ke kuka, ya rungumeta ya runtse ido yace "Kiyi hakuri Mami, kowa a rayuwar nan da irin tasa kaddarar, and Alhamdulillah so far" Mami ta gyada kai tace "Haka ne son" Yayi kasa da murya yace "Ni kaina bana son ganin kowa na gidan nan a yanzu, don haka ki kwantar da hankalin ki, i will follow the back door idan xan fita..." Cikin sanyin murya tace "Toh mota fa?" Yace "I will order Bolt" Mami bata kuma cewa komai ba, yace "In sha Allah idan na dawo zan ci abincin Mami" Yana fadin haka ya lumshe ido yayi pecking dinta a forehead sannan ya mike, ta bi sa da kallo hawaye na zuba idonta har ya fita daga dakin.
Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
And ur evidence via 07087865788
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549
Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
Khalil na isa hotel din ya nufi dakin direct ya bude kofar, sosai ya ji gabansa ya fadi ganin babu kowa cikin dakin, da sauri ya karasa ciki yana kallon abincin da ya ajiye mata yaga ko ta6awa bata yi ba, lkci daya yaji zufa na keto masa, kallon kofar bandaki yayi nufi can da sauri ya bude kofar nan ma babu ita a ciki, nan yaji hankalinsa ya kara tashi ya fice daga dakin ya sauka kasa yana kallon receptionist din wajen yace "Don Allah yarinyar da muka shigo dazu..." Kafin ya karasa receptionist din tace "Ta fita ai" kasa daina kallonta yayi, yayi karfin halin cewa "Ta fita? When pls?" Matar tace "Some minutes ago" juyawa yayi da sauri ya nufi kofar fita daga cikin hotel din, receptionist din ta bi sa da kallo, Khalil na fita bakin titi yana waiga gefensa ya ganta can zaune daga jikin hotel din kamar marainiya, lokaci daya ya hade rai ya nufeta, ita bata ma lura da shi ba tayi nisa cikin tunanin da take, yana isa dai dai inda take yace "Baki da hankali ne zaki fito nan bayan kinsan jakata na dakin?" Ta daga kai ta kallesa, sae kuma a hankali tace "To ba kai nake nema ba" yace "Me yasa zaki nemeni? Saboda me?" Ita dai bata ce komai ba, sai a sannan ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya juya ya bar ta wajen, ordering wani bolt din ya mayar da wayarsa a aljihu ya juyo yana kallonta yace "Ki jira ni a nan" Daga haka ya koma dakin don dauko jakarsa, yana fitowa sai ga motar, bayan sun gaisa da drivern ya sa jakarsa a booth, ya juya ya kalli Nihad dake kallonsa, ai bata ma jira yace ta taso ba ta taso ta nufosa, ya zaga ta daya side din ya shiga motar, tana dai ta tsaye, jin bai ce mata komai ba ta bude bangaren da take tsaye ta shiga ta jawo kofar motar a hankali. Kamar me Bolt din dazu wannan ma sae da ya tambayi khalil ko zai iya shiga ciki ganin unguwan da suka zo, Khalil ya sauke glass din side dinsa ya daga ma securities din wajen hannu sannan suka wuce, Nihad dai tun da suka shigo anguwan nan take kalle kalle uwa idanuwanta za su fito, she is wondering where he is taking her to, duk inda suka wuce sai taga securities, very tight security, bata ta6a jin tsoron kasancewa da Khalil ba sai wannan moment din, she looked at him looking very afraid, to ko dai inda ake yankan kai ma zai kaita, sosai gabanta ya dinga faduwa hankalinta yayi mugun tashi, ta dinga kallon Mad houses din da suke ta wucewa na masu kudi da suka amsa sunan su kudi a kasar, hakurin Nihad ya soma karewa ta juya a hankali ta sake kallon Khalil for the 5th time, gabansa kawai yake kallo fuskarsa babu yabo babu fallasa, Ai bata san sanda ta marairaice masa ba cikin rawan tace "Don girman Allah ina zaka kai ni? Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri, ina ne nan ka kawo ni?" Sai ta sakar masa kuka a hankali jin ya ki ce mata komai, shi dai ko kallonta baya yi, ko ma wanene yanda Khalil yayi keeping serious and straight face sai ya tsorata balle Nihad da dama can matsoraciya ce, Shi kam drivern bolt din slowly yake tafiya sbda Securities that are everywhere don zuwa lkcn gari yayi duhu, amma sai kayi tunanin rana ce don ko ta ina haske ne tarr, har dai suka isa dai dai gidansu Khalil, sai dai ba ta inda ya shigo dazu bane, wannan second gate din gidan ne dake ta baya, drivern ya tsaya yana duban ma'aikatan da suka nufo motar gadan gadan, Khalil ya bude motar ya sauka, suna ganinsa suka gaishesa suna komawa baya, Ganin Nihad taki saukowa daga motar ya zaga ta inda take ya bude motar yana kallonta babu yabo babu fallasa yace "Malama kina bata masa lokaci" Ta marairaice tana kallonsa cikin rawan murya tace "Don girman Allah ina ne nan din ka kawoni, kayi hakuri ka gaya min" Gaba daya tayi zuru zuru da ita kamar ba Nihad ba, shi dai kallonta kawai yake, can yace "Neman taimako na zo yi nan din, tunda kin ga bamu da inda za mu je" Ta gwalo ido sosai tana kallonsa da mamaki, can tayi karfin halin cewa "Taimako kuma? Unguwar masu kudi ne sosai fa, ba kowa ne ke shigowa nan ba wallahi, kuma ko kallonmu baxa su yi ba sai ma su kore mu ko su sakar mana karnuka, wllh ka shigo idan ba haka ba securities din nan za su iya sa mu tsallan kwado yanzun nan" ya dafa motar yana kallonta da kyau yace "Sa'armu za mu gwada, kuma ni nasan ina da sa'a sai in ke ce baki da, Malama ki sakko kina bata ma me mota lokaci" Da sauri Nihad ta kalli me tukin motar dake jiranta ta sauka patiently, can ta kalli khalil pleadingly tace "Ni dai don Allah ka zo ka shiga mu koma, babu abinda za su mana a nan" Yace "Idan muka koma kina da kudin da za mu ci abinci gobe? Ko kina da kudin da zaki sake biya mana daki a hotel din?" Kallonsa ta dinga yi, lkci daya jikinta yayi sanyi, hawaye ya kawo idonta, sai kuma ta sa hannu ta share idon nata a hankali tace "Sai ka bani waya in kira ya Farooq nasan zai turo mana kudi" Yana kallonta yace "Aa, wannan gidan dai nake son shiga in gwada sa'a ta" Ta kallesa zata yi magana ya hade rai yace "Kina bata masa lokaci malama" a hankali ta sauko daga motar tana kallon Khalil hawaye na bin kuncinta, ya daga ma mai bolt din hannu ya ja motarsa ya bar wajen, cikin kuka tace "Toh ni dai da kace ya maida ni in jiraka a can hotel din, in ya so kai kadai sai ka shiga gidan" Wani kallo yayi mata ya nufi gate din gidan da tuni aka bude masa, Ta gefen ido take kallon securities din gabanta na faduwa don wasu dirka dirkan bayin Allah ne, can dai tana ganin Khalil ya shiga cikin gidan ta bi bayansa da sauri, ga mamakinta basu kulle ba suka jira har ta shiga sannan suka rufe gate din, Nihad ta dinga bin makeken compound din me dauke da wani ubansun mansion da kallo, kai kana ganin gidan nan kawai kasan ba karya malam, Compound din kuwa yayi ukun nasu ga parking lot kaca kaca, ko wanne da ride lafiyayye a parke, ita bata ma san ta bayan gidan suka shigo ba, don ta can ne zata ga ainahin kyan gidan, chalet da aka yi can gefe da ta hango kuwa ya kusa nasu main building din, tafiya kawai yake tana binsa zuciyarta na bugawa, but how comes yana ta tafiya kansa tsaye and nobody is even stopping him, taga sun zaga ta baya ya shiga wani stairs wanda aka shimfida ma carpet grass, shi kansa tsakar gidan wajen duk malale yake da Carpet grass din, bude wani kofa yayi bayan sun haura sama sun mike wani babban corridor, ya bude wata kofar duk tana biye da shi a baya a tsorace, ko nisa bata son yayi mata, gaba daya she is really confused at how he is just badging in babu shakka ba komai, ita tsoronta kada a kama su ayi masu dukan tsiya, da ido ta dinga bin parlon da ya shiga tana makale bakin kofa ta kasa shiga zuciyarta na bugawa, Can taga ya shiga wata kofar da sauri ta bi bayansa ko kulle kofa bata yi ba, nan taga kofar da ya shiga wani parlon ne wanda ya fi wanda suka baro haduwa, at this point, she is super confuse, bayan ya isa kofar dakin Maminsa ya juyo yana kallonta, ya fi second goma yana kallonta wanda hakan ne ya kara mugun tsoratata, can kuma babu yabo babu fallasa yace "Zauna nan" Ta kasa zama har taga ya shiga wani kofar, Mami na nan zaune yanda khaleel ya bar ta don ta kasa samun nutsuwa, gani kawai take shikenan kuma baxai sake dawowa ba, gaba daya jikinta a sanyaye yake har zuwa yanzu da ya shigo dakin nata, da sauri ta mike ganinsa with happiness written all over her face ta nufesa kace "U kept to ur promise son, baka wuce awa dayan ba, i was so worried ina ga kamar tafiya ka kara yi...." Yayi Murmushi ya kamo hannunta a hankali yace "Amma bana son ki saka rai da yawa ki sakankance a kan cewar na dawo in zauna Mami, kar ki manta ban san kiran me Abba ke min ba, he might still not be needing me in his house, kilan idan ya gama fada min abinda zai fada xai iya cewa in bar masa gidansa and i don't have choice...." Hawaye ya shiga sakkowa idon Mami tana girgiza kai tace "Baxan yarda da hakan ba this time around son, sai dai duk abinda zai faru ya faru, shirun da nake masu ya zo karshe, baxan sake shiru ba in har yace ka bar masa gidansa for the second time" Shi dai khaleel bai ce komai ba sai kallon mahaifiyar tasa yake cike da tausayinta, kamar yanda take ganin ya rame, shi ma haka yaga ta rame saboda damuwa, Can Mami ta share idonta da sauri tace "Where is the young gal?" Ya kalli kofa yace "She is at the parlor" Mami tace "Ohk" Daga haka ta nufi kofar ta fita ya bi ta da kallo, zaunawa yayi gefen gado ya rike kansa, yasan ko me zai faru baxai samu courage din sanar masu ai Nihad yarinya ce da babanta ya aura masa ba, shi kuma ya amshi auren nata ba don ransa ya so ba sai don ganin girma da mutuncin mahaifinta sannan baxai iya turning down din offer din mahaifinta ba, yasan baxai ta6a fara masu wannan bayanin ba, fadawa saman gadon yayi ya kwanta ya lumshe ido yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mami na fitowa parlor taga Nihad a tsaye bakin kofa tana shesshekan kuka, tun bayan da taga khaleel ya mata wannan kallon sannan ga shiga kofar ya kulle tayi saurin komawa bakin kofar fita parlon ta tsaya zuciyarta na raya mata shikenan babu wani tantama ya kawota ne kawai a gille mata kai ayi kudi da ita, dama masu kudin nan wasun su kowa yasan ai suna yankan kai, to kila mai gidan ya ba khaleel contract din samo masa kan da za a gille shi yasa har ya shigo gidan tare da ita babu wanda ya hanasa, sai ma bude masa kofa da securities din suka yi har da masu gaishesa, irin dai ya saba shigowa gidan kenan, sannan gashi taga kansa tsaye ya taho bangaren nan da ita, wato in da za a gille mata kan kenan, uwa uba tun da suka shigo gidan bata ga ko wani mutumin ba sai securities, Da mamaki Mami ke kallon Nihad ganin yanda take hawaye tace "Subhanallah, Baby are you