Showing 126001 words to 129000 words out of 135959 words

Chapter 43 - Namijin Zuma Book 1 Complete Hausa Novel

tasan meke cinta, bakin ciki da bakin kishi kawai ke ranta kmr zata hadiye zuciya haka takeji a ranta. Ta karasa ta zauna kujerar 2ctr dai-dai tana zama Aeezad ya sako Kai falon, sanye da jallabiya baka, idanuwansa suka sauka kan nabeelah wadda tayi kyau harta gaji da kyau, ga kyallin jego Tana tayi, kuma kayan datasa sun mata kyau sosai shima kuma sun masa, nonuwa tinjim tinjim ana ganinsu a bayyane, seda ya hadiye yawu ya shaki zallar kamshin dake tashi a falon na zallar turaren kamshi na yan chard. , haka kawai ya tsinci kansa da kasa dauke ido a kanta yau, duk yadda yakaiga SO ya dauke idanuwansa a kanta ya kasa, nan da nan kwad’ayinta ya taso masa ya tokare masa mara, seda burarsa da yan golayensa suka amsa, ba karamin kewarta yakeyi ba, ya tabbatr duk randa yajisa a gindinta seya kusa zaucewa dan dadih, sannan ba karamin ci ze masa ba. “Allah de yakai damo ga harawa…” ya fadi a zuciyarsa se hadiyar yawu yakeyi Kai bakace wai ya tabacin ma gindi a rayuwarsa ba.



Ba editing 🥹 ngde masu gaidani da jiki wasu charts yayi yawa na kasa amsawa amma ina godiya, Ina sassa muku Albarka masoyana Luv u All. 💖


This book is 1k 08101626484.
NAMIJIN ZUMA



52….


Karasowa yayi zauna kasa idonsa na kanta, ya gaza ko kyaftawa., ya gaida ummih ta amsa kanta na kasa, sam batasan zama a gidan suna hada ido da siriki kunya takeji sosai, tinda aka gama suna, ummih taso ta tafi Big hajiya ce tace bazata tafi ynzu ba gaskiya se yara sunyi kwari, hakanan dole ta hakura amma Tana cikin kunya gaskiya kodan ganin Aeezad be iya boye komi a kan nabeelah ko a gaban waye,. Zaman unmih a gidan yayi Amfani sosai ba karamin gyara nabeelah takeyi ba, da kayayyakin mata masu gyara martaba, Wanda ta siya daga Saadatubintuabdullahi, Aunty hafsat ma ba a barta a baya ba, tanata kawo ma nabeelah kayan gyara Kuma tana using, big hajiya ma ba a batta a baya ba gun gyara Me jego duk Wani Abu data sani tana hadawa ta bawa nabeelah, kowa ya fahimci zalamar Aeezad.

Tinda yashigo Ko Kallan inda yake nabeelah batayi ba, ta hade rannan kmr an aiko mata da mutuwa, ta hade fuska tayi kamar ma batasan da zamansa ba, idanuwanta na kan TV,. “Amshi yarki ki bata Nono…” Cewar big hajiya da tayi maganar da nabeelah, Tana miko mata Manaal wadda ke shirin kuka, se mutsu-mutsu take Tana neman nono. Amsar yar nabeelah tayi still ko Kallan Aeezad batayi ba ta ciro Nono tasawa yar a baki seda Aeezad ya hadi yawu, yaji daman a bakinsa nabeelah tasa nonon. yabi farin nonon nata da ido, ya kula da yadda nabeelah keta daurewa, Gashi ko gaidasa batayi ba, tana gaidasa inde yashigo koda yake fushi da ita, shide yasan be mata komi ba, hasalima ita ta masa lefi. Big hajiya da take jiran shigowarsa ta fara sirfago masa matsifa. “Kai ashe yau Matarka zata tare amma baka gayawa mutane ba? Saboda rainine ko wulakanci? Kodan duk cikinmu ba wadda ta isa ka gayamata ne bansani ba…amma ai yaci ace ka gaya ma matarka shedhanu na tafe saboda mu killace yaranmu da Addu’ur’i, da uwar yaranma…” Aeezad ya dawo da dubansa kan big hajiya, ya fahimci me take nufi, yace “Wallahi Nima bansan da dawowarsu ba jiya daddy ya sanar Dani da daddare, shiyasa ban sanar ba big hajiya, ayimin hkri…” “Ahhh Lallai kace aikin sanusi ne, zezo ya sameni, ,,,amma Meyasa tadawo gidannan bayan ga gidaje dayawa ai daka bata wani ta koma can, gaskiya ni bnji dadin dawowarta nan gidan ba…” Cewar big hajiya. Aeezad yace “Wlhi Nima hakan naso , Amma daddy be yadda da hakan ba, kawai de Banda yadda zanyi ne…” nabeelah ta tabe baki Tana gyara kan Manaal dake cikin hannunta, ta gyara mata nononta dake cikin bakinta, a zuciyarta ita kadai tasan me take Ayyanawa. Big hajiya taja kwafa tace “Toh ai shikenan, inta dawo da zaman lafiya se a zauna, in kuma da tashin hankali ta dawo gaskiya sede ka kuma sakinta domin kuwa bata isa ta fidda me yara ba a gida, kuma uwar gida , ynzu nabeelah itace uwar gida tinda ita naeema ai Auren kome ne…iskancin da tayi ada taci lafiya ita da uwarta yanzu basu isa ba wlhi…” Aeezad de yanajin big hajiya amma bece komi ba. Ummih ce tace “Insha Allahu zasu zauna lafiya …” big hajiya tace “Allah yasa…” Aeezad da ummih suka amsa da Amin. Seda nabeelah ta kallesa ta kulama se wani murna yakeyi sbda matarsa ta dawo. “Seka hadasu ka musu natsiha kuma ka fitar musu da kwana,mude karka kawo mana ita Nan, kar Azo a zuba mana Wani asirin…” Cewar big hajiya. Aeezad yace “toh insha Allahu…” Mikewa nabeelah tayi da Manaal a hannunta sbda ta gaji da zaman falon, gabaki daya batasanma ganinsa ko jinsa. “Hajiya kawata manaal tayi bacci kou ?” Big hajiya ta tambayi nabeelah dake shirin barin falon da Manaal a hannu wadda tayi bacci tinda ta Kama Nono ta tsotsa tayi bacci. “Eh tayi bacci..,bari ma in kwantar da ita…” Cewar nabeelah data juya ta nufa bedroom dinta, Aeezad yabi manyan duwawukanta da kallo , se yaga ma kmr da gangan take kada masa su, ta kuma cika fam kmr zata fashe, duwaiwukanta sunyi taf-taf, tako ina ta cika ta batse. “Inside ma nasan ta kuma dadih…” ya fadi a ransa yana hadiyar yawu. Ya amsa babys dinsa dasuke hannun ummih da big hajiya idonsu biyu su basuyi bacci ba. Ya rungumesu jikinsa ya musu Addu’ur’i shi inde ze daukesu toh seya musu Adduah dasa Albarka kullum. “Akwai abinci yunwa nakeji?” Aeezad ya tambayi big hajiya. Big hajiya tace “Akwai Matarka ta dafa ka isa dinning Kaci…” AEEEZAD ya Mikama big hajiya wadda ya amsa a hannunta ya mikawa ummih wadda ya amsa a hannunta. Ya nufa dinning ya zauna ya zuba abincin tuwon Semo ne da miyar yauki, ya fara ci yana santi, ba karamin mugun dadih tuwan yayi ba,Daman yasan mommy da iya girki. Yanacin abincin yana tunanin meyayi ya batawa mommy rai ya ganta a mood din dabe Saba ganinta ba, kuma shi yasan be mata komi ba, haka kawai se yaji duk mood dinsa ya cunkushe zuciyarsa tayi ba dadih. A haka ya gama cin abincin ya tashi, ya kara daukar yaransa ya Gansu kana ya badasu ya fice a part din, zuciyarsa na kwadayin sake ganinta ji yakeyi kmr ya bita dakin ya sake ganinta yau kyaun data masa yayi yawa tajima bata masa kyau ba kmr na yau, ga Abubuwa sun cika fam, ta sake kiba, Kuma ta sace daga kibar ciki, yau kimanin kwananta talatin da aka mata CS. Yana fita daga part din nabeelah, haka kawai ya tsinci kansa dasan zuwa part din naeema. Direct kuwa part din naeemar ya nufa, a falo ya taddata ba kowa, tini an gama mata kulle kulle an batta ita kadai, yan kawowar tata sun watse, bayan sun gama habaice habaicensu, sede sunyi a banza sbda ba Wanda yaji, su ko irin zuwa part din uwar gida basuyi ba sunce sun kawo amana, Ina, sbda da tiririnsu suka dawo,. Sanye na'eema take da wasu shaggun Kaya wad’anda marabarsu da babu kadan ne,riga da wando ne irin masu bin jikinnan, Kuma masu sajewa da Skin. Yana daura idanuwansa a kanta ya kumajin shaawarsa ta kuma tashi, amma Sam sede yaji a zuciyarsa nabeelah yake bukata ba ita ba. Ta gaidasa cikin makirci. Ya amsa yana binta da kallo se Kara kwarkwasa takeyi, a zatonta ko Kallan da yake mata hkn na nufin tayi masa kyau ne. “Kamshin meye wannan? Banasan wannan kamshin gaskiya….wani irin kamshi nema wannan tukunna?” Ya tambayeta yana yatsinar fuska yana kara sinsinar kamshin falon nata, Sam be masa ba. Tinda ya shigo part din wani kamshi mara dadih ya bigesa, kawai se yaji a ransa yafisan kamshin part din nabeelah, kamshin part dinta na kwantar da hankali Amma Wannan na part din na'eema daga masa hankali yayi. Naeema ta rasa me zatace masa sbda turare ne dasuka amso takanas a kasar china a gun boka ta turara gidan dashi, bokan ya tabbatar musu da in Aeezad yaji kamshin turaren tabbas zata mallakesa, batasan kafin Yaa shigo seda yayi Addu'ah ba, Kuma Addu'ah takobin muminine. “Tinda kamshin be maka ba bazan kara sawa ba, turaren wuta ne…ka karaso ka zauna mijina…” Cewar Naeema da tayi mgnr ba laka a jikinta Tana ganin da wuya ma in turaren zeyi tasiri a kansa, amma ko wannan beyi ba, tanasa ran na jikinta zeyi tasiri a kansa, wuyarta de ya kusanceta, nan haka a shirye take tsaf, har na matsin ta matsa a jikinta, wanda boka yace daya sadu da ita inde ya kawo a farjinta toh ta mallakesa da maniyyinsa ya hade da asirin shikenan ta kamasa ram a hannu.ta daura damarar yau ko be nemeta da saduwa ba ita zata nemesa. Aeezad de ya bita da ido yaga se wannan abubuwa takeyi abinda bata saba masa ba, seyayi tunanin ko ta fara zama karuwa karuwane, bazeyi mamaki ba sbda yawan duniya ba inda bataje ba, ba fitar kasashen waje, shi baya zargin na'eema da zina sbda a farko Daya Aureta shiya fara kusantarta. “Bazan iya zamaba gaskiya,,,bansan kamshin dake part dinnan ki biyoni part dina, inasan mgna dake...” yana fadar hakan ya juya ya bar falon ya fice, direct part dinsa ya nufa, haka kawai ya tsinci kansa da nadamar ma dabeje part din ba, sbda kamshin part din nata ciwon Kai yaso yasa masa. Yana zama a falonsa ya lalubi wayarsa ya kira lambar nabeelah Tana kwance kan gadonta, tinda ta shiga dakin ta kwantar da manaal ta kwanta ta rasa abinda ke mata dadih, ji takeyi daman bata gidan yau naeema ta dawo gidan, kmr zatayi kuka haka takejin zuciyarta gabaki daya zuciyarta bata mata dadih. Wayarta dake kan gadon tayi ringing tin kafin ta dauka ta gane Aeezad ne sbda ringin tone dinsa ma daban yake ita tasa da kanta,. Tanaji ya mata kira uku bata daga ba kuma batajinma zata daga ko kira Dari ze mata, kawai ma se tasa wayar silent sbda kar karar wayar ya tasar mata da yarinya. Duk kiran da yake mata yasan tana gani amma taki dauka, se yaji hankalinsa ya tashi. Ya mike ze bar falon naeema tashigo ya bita da ido, da kayan daya sameta falonta dasu tazo ba ruwanta da kunyar ma’aikata. “Ke haka kika keta masu aiki tsirara!” Ya fadi cikin tsawa. Naeema tayi kasa da kanta kawai ba tare datace komi ba. Kwafa yaja yace “look tin wuri ki gyara, Bazan dauki halinnan ba…abinda kkmn a farko ynzu bazan dauka ba, sbda bake ke Aurena ba nike Aurenki ynzu baku isa ku juyani ba keda uwarki, jiya ba yau bane,,,” yana gama fadar hakan ya fice a falon naeema ta isa kujerar 3ctr ta zauna a zuciyarta tanaji zata jure komi daze mata tasan kafin ya shigo hannu ne daya shigo shikenan, amma fa tasan zatasha whla, dukya chanza mata ba kmr Ada ba, kalamansa na ynzu ma sun bata haushi da mamaki, batasan duk abinda zasuyi yadinga Sako uwarta ciki.

Yana shiga falon gidan yaga Aunty hafsat tazo da yaranta , zuwan Aunty hafsat dinne yasa nabeelah fitowa falo, Tana ganin yashigo ta mike ta bar falon ta koma bedroom , Aunty hafsat da ummih sun kula da saboda zuwan Aeezad ne yasa ta koma daki, shima kansa gogan ya kula da hakan. Gaisawa sukayi da Aunty hafsat, ta masa Allah yasa Alkhairi sbda big hajiya ta shaida mata naeema tadawo gidan. Ba tare daya amsa ba ya nufa dakin Aunty nabeelah gabaki daya hankalinsa ya tashi Dazu ma yasan sbda shi ta tashi a falo ynzu ma haka, wato batasan ganinsa toh meya mata be sani ba?. Hankalinsa yafi na barawon asubah tashi, duk yabi ya rikice a lokaci kankani, da kyar yake hadiyar Yawun bakinsa. ya turo kofar dakin yashigo zaune ya sameta gefen gado, kallo daya ya mata yashiga hankalinsa sbda ta hade rai ba Alamar wasa, Sam be saba ganinta hk ba, Nan hnklinsa ya kuma tashi. Hankalinsa in yafi dubu seda ya kuma tashi ya karaso ya zauna kasan kafafuwanta, shi tsoronta ma yakeji, yau kawai duk yabi ya shiga taitayinsa. “Ina wuni mommy…” ya gaidata cikin rudewa, ya rasa ma yazeyi. Ko uffan batace masa ba se tayi ma kmr batasan da halittarsa ba. Yayi kasa da kansa ya kasa ma kallanta sbda fuskarta tsoro take basa. Ci gaba yayi da magana a daburce lokaci kankani yazama kmr bashi ba, tsoronta ma yakeji Wallahi. ”mommy naga kmr kina fushi ne Dani? Koda kikaga ni ina fushi wallahi na hakura ma yanzu…kawai mu koma normal in saboda ni ina fushi kika dau fushi toh kiyi hkri pls ni na hakura, rayuwata zata shiga garari in kina fushi Dani mommy, ki rufamin Asiri….” “Kadan ka gani…” ta fadi a ranta a fili batace uffan ba. Harya gama sambatunsa ya mike tsaye ya kalleta yace “Ko zaki samu zuwa part Dina, inaso ne in muku natsiha keda naeema, sannan a fidda kwanakin dazan dingayi a gun kowacce…” “bazanje ba, kaje na bar mata Kai duka, kwananka a gurina bana bukata, wlhi na bar mata kai ka dawwama a gunta, tinda kaje ka dawo da ita danta baka gindi aise kaje kayita ci wlhi nide jikina yazama haramiyyarka, kaje gunta, ko Ka kwana guna ba abinda zakamin, banaso…” tayi magana kishi fal muryarta da fuskarta. Idanuwa yafita dashi bata taba masa mgna da muryar data masa yau ba, nan da nan ya fahimci Azababben kishi ne ke damunta. “bazan yarda ni ki barwa Wata niba... duk duniya ba macen dazata iya Dani mommy seke…bazan iya rayuwa ba tare dake ba wallahi mommy, dan Allah ki rufamin asiri Karki dagamin hankali,,,in wani abun ma miki ki gayamin dan Allah wlhi zan tsugunna in baki hakuri kuma bazan kara ba insha Allahu, bacin ranki bazarana ce ga rayuwata…” ya karashe kmr ze fashe da kuka, ji yayi duniya ma bata masa dadih saboda baya dadih da ita, yanzu yanzu duk ta chanza masa yau kawai amma ji yake kmr sunyi shekara a haka, dukya rikice. Komawa tayi ta kwanta yaga Alamar bata niyyar tashi, ya dinga bata hakuri amma Sam taki bi ta kansa dole ya fice a dakin bayan ya jima sosai. Ko sallahma bema kowa ba ya fice a falon, Fuskar nan tasa shima ba Annuri, ya nufa part dinsa. Har ynzu naeema na nan, taji haushin jimawar da yayi be dawo ba, kuma tasan part din nabeelah yaje. “Jeki part dinki, Wani time nayi mgnr…” ya fadi fuska ba Annuri ta bude baki zatayi mgna ya daka mata tsawa “Ki tafi part dinki nace!!” Dole naeema ta fice a part din amma ba haka taso ba, wato dai yau ba nasara. Haka ta koma part dinta zuciya fal bakin ciki.
Zirya Aeezad yashigayi a falonsa yana tunanin shi toh meya ma nabeelah haka ta dauki wannan zafin dashi? Shi se yanzu ma yake nadamar fushin daya mata, seda ya jima a tsaye yana nazari kana ya fara tunanin kode kishi ne ke damunta? Dantaga naeema ta dawo Gidan, kila tanasha koshi yaje ya dawo da ita, amma kuma ai yayi ma big hajiya bayani ai kuma tana falon. Ya fahimci wannan ne matsalar sbda a kalamanta ma ya fahimci hakan. Komawa part din yayi kmr wanda aka mintsila, ko sallahma beyi ba ya shigo sede big hajiya da ummih da Aunty hafsat da bata tafi ba har yanzu, suka gansa tsundum a falon. Dakin nata ya nufa, ya taddata kwance idanuwanta rufe Amma ba bacci takeyi ba Tana tunanin rainin hankalin da Aeezad ke mata ne kawai, tanajin shigowarsa kuma tasan shine ta hanyar kamshin turarensa, taki bude idonta. Yasan ba bacci takeyi ba ya tsugunna yace”nasan ba bacci kkba mommy…In dan dawowar naeema ne kk chanza wlhi bani nace ta dawo ba, dan Allah ki rufamin asiri gabaki daya duk kin dagamin hankali, ko miyau da kyar nake hadiyewa, ki temakeni yadda Allah ya temakeki mommy..” nabeelah ta tabe baki , batace masa komi ba, harya gama maganganunsa ya gaji ya tashi ya fita ya koma part dinsa, duk yabi ya fita hayyacinsa dayazo fita se binsa da ido kawai su Aunty hafsat da big hajiya da Ummih sukayi gabaki daya ya susuce. Haka de ya kwana yana shige da fice a part din ranar ummih ta fahimci ba lafiya ba. Big hajiya kam seda ta masa magana tace yadena musu shige da fice ya barsu suyi bacci, amma Sam beji ba, sede ya shigo yaga nabeelah da yaransa ya fice. Da Asubahi yana idar da Sallah daga masallaci nan yayo kmr mahaukaci ya tadda nabeelah da big hajiya suna lazimi suma jam’i sukabi da masallaci ynzu suka idar da sallah. Ko kallansa nabeelah batayi ba, Balle taji tausansa, bazama taji tausansa ba, jiya ko bacci batayi ba sbda Azabar kishin dake cinta, tasan dakin naeema ya kwana, dukda Rabin darensa a nan part din yayi amma tasan komawarsa ai dole zasuyi wani abu da naeema yadda yake a hannun nan, zuciyarta ta bata tabbacin ai dole ma zeyi wani abu da naeema tinda daman dan yayi wani abun da ita ya dawo da ita, amma shine yazo yake mata kalaman yaudara in banda beda kunya shi har yanada bakin gaya mata wani abu. Bayan sun gama lazimin ta gaida big hajiya, idan big hajiyar yasa ta gaidasa ya amsa Cikin hanzari kmr yana jira ya gaida big hajiya ta amsa Tana tsuresa da ido se Kallan nabeelah yakeyi, ita kanta big hajiya ta fahimci ba kalau yake ba gaskiya. Nabeelah ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login