Showing 120001 words to 123000 words out of 204120 words

Chapter 41 - Gurbin Ido Book One Complete Hausa Novel

ya soma rage suit din jikinsa,sannan ya danna alamar kore na amsa kira,ya kuma dora wayar saman qawataccen dressing dinsa ya sanyata a hands free.



A kasalance yayi mata sallama,saidai yanayin yadda ta amsa sallamar yaja hankalinsa,har ya maida dubansa ga madubi yana kallon kansa da kansa,tare da jiran jin abinda zata fada



"Kana jina jafaru?" Ta fadi a kausashe kuma kanta tsaye,idanunsa ya lumshe ya kuma bude duk a kusan lokaci daya sannan yace



"Ummm"



"Idan kaga ma ba zaka amsa ba duk bazanyi mamaki ba,tunda dai xuwa yanxu wuyanka ya isa yanka,sannan kayi sama da haka ma......inason a gobe kafin ka wuce wajen neman kudin daka maidashi ibada sama da komai,ka tattaromin kan matanka ka kawomin su dakai kanka,dukkanku inason ganinku" qit ta kashe wayarta,sai ya aza idanunsa akan wayar tasa ba tare da yace komai ba,kwanyarsa na masa bita yanayin sautin muryar anni da kuma abinda tace masa goben yayi



"Matansa?, what's happening?" Ya yiwa kansa tambayar da bashi da amsarta,sai kawai ya zabi jefa damuwar samun amsar tambayar a bayan damuwoyinsa,ya dage kafafa in i don't care manner,yaci gaba da zare kayan jikinsa ya kuma wuce toilet ya hada ruwa me zafi yayi wanka,wannan kusan dabi'arsa ce,ba kowa ne zai iya wanka da ruwan da yake wanka dashi ba saboda yayi zafi da yawa.



Daya fito yana sharce sassalkar sumarsa dake jiqe da ruwa,qugunsa daure da towel wanda ya bayyana dukka wata kyakkyawar qira ta jikinsa,gefe guda maganar anni na dawo masa,sai ya janyo wayarsa a hankali sanda ya tuna voice note din da amna tace tayi masa ta wayar khadim,ya lalubo number dinsa ya shiga,ya kunna na farko yana samun waje ya zauna yana ci gaba da goge jikinsa.



A hankali tsadadden murmushin nan nasa ke fita a fuskarsa,abune me mugun wahala ka ganshi ga fuskarsa,duk da yadda yake qara masa mugun kyau,sai daya gama ji tsaf sannan ya jawo wayar yana kasheta,can qasan ransa yace



"You deserve my time amne na,i promise you,i will make you happy ending month in sha Allah".



Sai daya gama shiryawa sannan ya tuna bashi da abinda zaici,ya sani yau baba tabawa ta koma gida,it means zaici gaba da bulayin neman abinci?,anya ba cook zai dauko ba kuwa ya aje cikin gidan?,sam ba girmansa bane a dinga ganinsa a eatery da sunan siyan abinci,bayan yana da komai,Allah ya mishi komai,yana da arziqin da idan abincin wata qasar yakeso yaci kullum to fa zai sameshi,sai ya miqe yana fita zuwa ga fridge din falonsa ko zai zamu wani abu da zai iya ci,gefe daya yana tunanin yadda zai gaya musu su shirya goben zasu wajen annin.



**********Karfe goma na safiyar washegari,wata safiya da aka tashi da haduwar gajimare wanda me dan duhu,cikin abubuwan dake alamta fara saukar damuna kowanne lokaci daga yanzu.



Tsaye a gaban daya daga cikin motocin dake fake a harabar gidan yake,sanye da wata shadda sky blue me matuqar kyau da daukan hankali,anyi mata dinkin zamani wanda ya dace da yanayin qirar jikinsa,ya kuma tafi da structure na jikinsa a matsayin cikakken namiji da ya amsa sunansa,mai haiba cikar kamala da kuma zati.



Qarasowarsa wajen kenan,cikin hanxari drivernsa ya fito yana karbar jakar hannunsa,gami da qoqarin bude masa seat din baya kamar yadda suka saba duk sanda xasu fita.



Hannu ya daga masa ya qarasa cikin coolness dinsa ya sanya hannu zaya bude gidan gaba,a dai dai lokacin ta qaraso cikin shigar wata irin gown da aka mata wani dinki,kanta yane da qaramin mayafi,yayin da fuskarta ke dauke da wani makeken sun glasses da yayi shigen kala da kayan jikinta,wani babban bangul ne a hannunta ke zobe guda daya,sai hig hill shoes data sanya a qafarta,mahadin figigiyar hand bag dinta,ta fito a unaisarta sak,unaisar shekarun baya,diyar gidan minister,shigarta gaba daya batayi kama da shigar wadda zata gidan surukanta ba,ga mutumin da ya fara ganinta yanzu,zaiyi zaton wani taro daya shafi siyasa ko kuma jiga jigan 'yan boko zata je.



"Good morning" ta fada cikin salo,idanuwanta na kan ja'afar,wanda tuni ya bude gaban motar yana yunqurin shigewa



"Morning" ya amsa mata a taqaice,sannan ya zura jikinsa a hankali kafin ya dauke qafafunsa dake saye cikin wani lafiyayyen half cover shoe na kamfanin louise vuitton,hannunsa dake daure da wani lafiyayyen gogon kamfanin Blancpain ya zura da niyyar rufe murfin motar,unaisa tabi hannun da kallo bayan ta gama qarewa takalminsa kallo,take ta sake sallamawa,da gasken gaske dan gayu ne shi din na qarshe,wanda yasan sirrin kwalliya tare da ta'ammali da designers kayayyaki,bata sake cewa komai ba itama,saiya bude back seat amma ta saitinsa ta shige,tana dora idanuwanta kan fuskarta da take iya hange ta madubin gaba,wanda tuni ya bude news paper ta safiyar ranar da drivern sa ya miqo masa,yawanci dukka safiya yakan dudduba jaridan data fito a safiyar,musamman page din da suke wallafa al'amuran da suka shafi kasuwanci.



Tana so ta tambayi wanda suke jira amma wani irin kwarjininsa daya cika motar ya hanata cewa komai,sai ta fidda wayarta ta bude watsapp dinta,ta hau turawa anty talatu saqo,abinda ya dan janye hankalinta kenan,saboda maganar da suke da anty talatun nada matuqar muhimmanci.



Karo na uku kenan ya daga kansa yana duban hanya da niyyar idan bata fito ba zasu wuce kawai,ta biyosu daga baya,har yadan fafa hasala,saidai bai nuna ba kamar yadda ko sau daya baiyi qorafi ba,kasancewarsa mutum ba mai yawan magana ba,saidai a cikin sa'a ya hangeta tana tahowa.



Glass din fuskarsa da yakanyi amfani dashi lokaci lokaci ya zare a hankali tare da qoqarin kau da idanunsa daga sashen da take tahowan,bawai don yana tunanin tana ganinsa ba,a'ah......daya daga cikin dressing na shaheeda tayi,dressing din da kusan zai iya cewa ita daya ce macen da yasan tana yinsa,kuma har yau shi dai bai sake ganin wata da irin shigar ba sai ita....bai sani ba,ko don idanun gaske dana zucin ma gaba daya tare da hankalinsa kacokam basa tare da kowacce mace?.



Shigar lafaya tayi blue black me adon gold a jiki,ko ba'a fadi ba kalar tana daya daga cikin kalolin dake haska farar fata ainun,rashin sabo da yanayin shigar ya sanyata take jin kamar zata harde,wannan ya sabbaba mata taku cikin nutsuwa da takatsantsan,abinda ya zame mata kamar ado,kamar wadda ke yin tafiyar da gayya da kuma wata manufa ta daban.



Dukka cikin sakannin da basu haura goma ba ya gama kallonta kafin ya zare idanunsa ya maida kan news paper din nasa,dai dai lokacin da ita kuma unaisa ta daga kanta da xummar gyara zamanta,idanuwanta sukayi kyakkyawan ganin da ya sanya tunaninta qwacewa na wasu daqiqu



"Damn it" ta fada can qasa,tana jin wani abu me qarfi yana fusgarta,kishinta ya soma huda zuciyarta yana ratsata da gasken gaske,bata iya dauke idanuwanta ba,har zuwa sanda ta iso dab da motar.



Batasan waye da waye a ciki ba,don haka tadanyi knocking kadan,drivern ya motsa da niyyar fita ya bude mata kamar yadda ya yiwa unaisa,sai ya cira kansa a hankali daga cikin news paper din



"Ummm ummm", ya fadi a taqaice,sai ya waiwayo ya kalleshi,yayi masa alama da ya zauna,a ladance ya amsa masa,ya ajjiye news paper din,sannan ya kama handle na motar ya bude,ya zuro qafarsa waje guda daya.



Kusan a tare suka hada idanu ita dashi,dukkansu cikin gaggawa kowa ya killace ganinsa,cikin dakakkiyar muryarsa ya magantu



"Bana iya zaman jiran kowa....wannan ya zama shine lokaci na qarshe da zaki aikata hakan" ya qarashe fada da muryar warning gamida da kausasa maganar tasa.



Sauka idanuwanta sukayi kan unaisa,wadda tadan rage glass din xuwa qasa kadan saboda ta samu damar jin a inda zasu fada,ita unaisar ke kallo,sai da suka hada idanu kuma sai ta tabe baki ta kuma janye idanun nata daga kansu ta mayar ga wayarta,a hankali maimunayu ta dauke idanunta daga wajen itama,tana jin yadda idanun nata suka cika da qwalla,cikin muryar nan tata dake cike da rauni....wadda ga wanda bai snata ba zai kira hakan da zallar shagwaba tace



"Kayi haquri" lafazin suka fita da sanyi da kuma zaqun muryarta,bashi ba,hatta da unaisa sai da salon da tayi maganar yaja hankalinta,ta sake maida idanunta kanta ba tare data shirya ba,tana jin kamar ta samu abu ta boye maimunatun,idanu su daina kaiwa zuwa gareta.



Sai daya lumshe idanunsa kana ya bude duka kusan lokaci guda,ya sake zube dubansa akan fuskarta,yana kallon yadda idaninta keta qyalli saboda ruwan hawauen da sukayi guzuri,yana mamakin saurin kukanta....me yasa ita din bata da tsayayyar zuciya,saurin bada haquri saurin kuka da kuma shagwaba kamar wata yayayya.



Qaramin tsakin da ita daya ta iya jinsa yaja yana maida jikinsa cikin motar



"Shiga mu tafi" ya fadi s gajarce,sai tasa hannu ta buda murfin motar ta kuma shiga bakinta dauke da sallama,driver ya amsa,yayin da da bakin J din yadan motss kadan alamun amsawa,ta fannin unaisa kowa ko uffan bata ce,can qasan ranta a mugun quntace.



Kaf maganganunta na jiya bata ga inda ta sanyo maimunatun a ciki ba,don me xa'a tafi da ita,ta maslahar aurenta ita daya kawai takeyi,bata qaunar ganin kowacce mace ta giftawa wannan buri da muradin nata.



Sosai qamshinta ya cika motar,har yaso yayi gogayya da nashi turaren,ya rufe news paper din a hankali ya ninketa gida biyu yana jan numfashi sosai wanda ya cika da qamshin nata,yana fesarwa kiran anni na shigowa wayarsa,ya dubi fuskan wayan bayan yayi kamar bazai dauka ba



"Am on my way" ya fada a taqaice,ya zame wayar daga kunnensa ya maidata inda ya dauko ya ajjiye,gefe daya na zuciyarsa yana cike da mamakin kiran meye haka anni ke masa da har ta qagu su iso,tabe bakinsa yayi,baisan da wacce rigimar zata zo masa yau ba,don bata rabo da rikici,amma koma dai meye...... he's ready akan duk wata rigima da takeji da ita,don yayi mata iya abinda zai iya,duk da ransa da zuciyarsa basa so.

[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 52

Fuskar anni kadaran kadaham sanda yake gaidata,duk da ba wani kallonta yayi can can ba,amma kuma jiki da zuciyarsa sun gaya masa lallai akwai wata a qasa,maida idanunsa yayi ga haj munubiya,matar da tun da can ba wani yi masa tayi ba,dama babu wani jituwa sosai a tsakaninsu,duk da ba wani abu bane yake shiga tsakaninsu ba,amma jininsu bai hadu ba.

Tata gaisuwar mai guda daya ya miqa mata,ta amshe da sauri tana cewa

"Lafiya qalau manya,ya ayyuka ya iyali?"

"Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice idanunsa akan qafafun anni dmda aka shafawa magani,ta kuma miqesu,da alama ciwonsu ya motsa

"To Allah ya taimaka,ya kuma dafa mana" bai maida hankali kan amsa addu'arta ta qarshe ba,cikin muryarsa me taushi da wani lokaci kan fito da wani amo da nauyi yace

"Anni,har yanzun duka tarin magungunan da kike amfani dasu basa aiki?" Dan duban qafar tayi kafin ta maida dubanta gareshi

"Abunne kasan dacewa ne,anata yi dai,sai sanda Allah ya dauke"

"Bare ciwo,kasan idan ya hadu da girma sai haquri" haj munubiya ta tsoma musu baki,ba tare da yabi ta maganarta ba ya zaro wayarsa,ya budeta,yayi kiran waya sannan ya sanya ta a kunne.

A hankali ya fara magana cikin yaren da maimunatu taji yana magana dazun,sai kuma yadan miqe a nutse yayi gaba dasu kadan can wajen dining din annin yana ci gaba da yin wayar,dai dai lokacin da khalid yayi sallama cikin falon.

Kan maimunatu idanunsa suka fara sauka,zuciyarsa tadan motsa,ya dan kafeta da idanu yana qarasowa cikin falon,sanye da qananun kaya,ya cusa hannunsa guda daya a aljihun jeans dinsa,daya hannun kuma riqe da key din motarsa yana dan kadawa

"Har ka dawo?" Haj munubiya ta fada,don ba haka taso ba,bataso dawowarsa a yanxun ba,saboda tana son fara aiwatar da shirinta,maganarta tasa ya dauke dubansa ga maimunatun zuwa kanta

"Eh,naji kince sauri kike ko?"

"Eh.....bawai wani sosai ba,dama abinda yasa nace kayi saurin kazo mu wuce,hafsat tacemin zata shiga makaranta,to kuma yanzun naga tex dinta ta fasa fitar,kuma na dan kwana biyu ai banzo gidan ba,ya kamata nadan zauna kadan mu gaisa sosai,don ko wajen yaaya marwan din ban shiga mun gaisa ba" anni dake sauraronta baki ta tabe tana kauda kanta gefe,a dan zuwan da take jifa jifa bata taba ganinta ta shiga sashen marwanun haka siddan ba,saida dalili,saboda haka kawai ta dorawa aishatu amma tsangwamar da babu dalili,face zallar faccalanci,amma yau abun mamaki wai ita ke zancan bata shiga sun gaisa ba,kafada ya daga yana maida kallonsa kan maimunatu kamar da ita suke maganar

"Well.....shikenan,zan koma ni,driver ya maidake gida kenan?"

"Eh zan kirashi,ko zuwa azahar ne sai na koma".

"Ina kwana" maimunatun ta fada sanda ta fahimci sun gama maganar,fadada fuskarsa yayi da fara'a yana amsa mata tare da tambayarta gida da kuma karatu,sai tayi mamakin yadda akayi yasan tana makaranta,amma tadai amsa masa da

"Alhamdulillah" dai dai sanda ja'afar ke saukowa yana shigowa cikin falon,idanunsa duka akan khalid din,tunda ya shigo yana karance dashi,yana ganin kuma kome dake wakana cikin falon,wani dan zafi yake ji a qirjinsa da baisan dalili ba.

Waiwayowa khalid din yayi sanda yaji muryarsa yana fadin

"I will call you back later" cikin wayar,sai ya tako a hankali yana miqa masa hannu cikin sakewar fuska,ja'afar na daya daga cikin mutanen da yake burin inama ace shine su,abubuwa da dama masa suna burgeshi,saidai girman kan da yake dashi yasa yake dannewa tare da hudubar haj munubiya dake nuna masa cewa gaba yake da ja'afar din a wajenta,kada ya sake ya nuna masa shine sama dashi.

A daqile ya bashi hannun sukayi musabaha,haka kawai yakejin zafin har yanzun a cikin ransa,idanuwansa kuma ya kasa kaudasu tsakanin maimunatu dake zaune properly waje guda,bata ma san meke faruwa ba,don dukka idanunta ta tattarasu kan wayarta ne

"Ba zaki sake amfani da kowanne irin magani ba,nayi magana da wani qwararren asibiti a turkey,zan qoqarin nema miki visa in sha Allah" ya fada muryarsa na dauke da wani irin amo kamar wanda yake fushi.

Sak hajiya munubiya tayi,cikin ranta tana debowa ja'afar tsinuwa,dan rawar ganin da yaronta yakeyi take taqama dashi,iyayensa maza ke yabonsa yana kula da mahaifiyarsu shine wannan shegen yaron me kafirin izza da jin kai zai soke?

"Amma.......naga a nan akwai likitan da nake turata abuja tana gani" khalid ya fada yana jin ba dadi cikin ranshi,kai tsaye ya kalla khalid din

"I know......."ya bashi amsa,gyara tsaiwa khalid din yayi,yana jin shima namiji ne kamar ja'afar din,kuma yana da say akan annin kamar yadda shima yake ganin hakan

"To inaga a barta zuwa wani lokaci mana"

"Ciwon yaci gaba da cin jikinta har sai ta daina tafiya?,banga wani ci gaba ba" ya fada hakan bayan yaja dan qaramin tsaki.

Idanu anni ta zuba masa tana karantarsa tare da son lalubo dalilin wannan fushin da kuma inda ya deboshi bayan ba haka ya shigo ba,dole ta tsoma baki,don kada ja'afar din ya sake fadin wani abu da bazaiwa munubiya dake zaune tana kallonsu dadi ba,batason kuma wani sabani ya dinga giftawa tsakanin jikokinta,bata jina da kashe case din khalid din da hisham ba,kada kuma wata sabuwa ta danno kai

"Shi ciwo fitarsa aisai a hankali,kuma shima likitan inajin dadin maganinsa sosai,kwana biyu ne da naqi komawa lokacin da yace abun ya dawomin" bai sake cewa kowannensu komai ba,sabida ya riga daya qudurce a ransa abinda yayi niyya,bazai kuma fasa ba.

Sallama khalid din yayi musu,sai haj munubiya ta miqe tabi bayansa,don tana son tace wani abu dashi,tanason kuma kafin taje ta dawo su gama abinda zasuyi itama ta dora nata

"Bari na shiga mu gaisa"

"To" anni ta bita dashi,don dama wajen takeson ta fita ta basu.

Falon ya dauki saiti shuru ba wanda yace komi,cikin zuciyar unaisa fal haushi,ita ba wannan ya fiddota gida ba,so take kawai a fara maganar da data tarasun.

Duban unaisa anni tayi,tana sane tace

"Shiga kitchen unaisa ki hadowa mijinku abinci" don ta sani sarai bai karya ba,don ba sanin jiya ko yau ta yiwa ja'afar din ba,kai ya girgiza

"Coffee kawai is okay" ya fadi a hankali yana rage kaifin idanunsa,har yanzun yana jin ransa yana suya.

Haushi ya sake qume unaisa,itakam meye hadin zuwansu nan da shiga kitchen ne?,ita tsakaninta da coffee ai saidai tasha,batasan takan yadda zata hadashi ba,to amma ba yadda zatayi,sai ta ajjiye maqallaliyar jakarta ta miqe ta nufi inda anni ke nuna mata.

"Bakwa bawa mijinku abinci ne maimunatu?" Anni ta jefa mata tambayar kai tsaye,sai maimunatun tadan rude, saboda bata tsammaci zuwan tambayar a sannan ba,ta daga kai ta kalli anni,sai kuma ta mayar ta sunkuyar ba tare da tace mata komai ba,ta yaya zata amsa mata?,tace mata batasan lokacin tashinsa da fitarsa ba?,ko kuwa tace batasan dawowarsa da lokacin buqatar abincinsa ba,ajiyar zuciya annin ta sake ta share maganar itama bata sake cewa komai ba.

Bata jima ba ta dawo dauke da mug a hannunta,ta ajje masa a gabansa tana sauke numfashi,sannan ta koma inda ta tashi ta zauna tana baza kunne.

Kurba daya yayi masa daci ya gauraye masa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login