Showing 48001 words to 51000 words out of 81312 words
zuciyarta.
Suhailat kuwa sbd yanayin jikinta da gajiya yasa tana kwantawa bacci ya dauketa cikin tsananin gajiya.
Abincin da aka aikawa kowaccensu daga part din sultana zaarah babu wadda tasamu damar ci har gwara suhailat tasha madara mai zafi sbd sanyi datakeji kamar zai kamata.
Rumanah kuwa kwance take tayi lamo cikin zurfi a tunani da tsananin son ganinsa sbd har lokacin takasa daina tuno yanayin dasuka rabu 'dazun hakan na raunana zuciyarta da kuzarinta ahaka bacci yadan 'dauketa tanayi tana farkowa hardai akai asuba tayi sallah takoma ta kwanta nanne tasamu baccin yadauketa sosai.
Qarfe goma ta fito palonta anan ta tararda dining shaqe da kalolin abinci ta kalli qofa kamar tana jiran isowar wani hardai tagaji ta nufi dining tana fidda wani irin qamshi mai dadi.
Fara cin abincinta kenan taji muryar data sakata dakatawa ta juyo da sauri suka hada ido da nuratu dake cikin tsananin farin cikin ganin rumanah din.
Miqewa rumanah tayi zata nufeta Jakadiya data kawo mata nuratu din tayi gyaran murya dole ta tsaya tana kallon nuratu cikeda farin ciki
Nuratu 'dince taqaraso gaban rumanah tana kallon cikinta tana sake bayyanarda farin cikinta zata zube qasa rumanah ta riqota tareda Rungumeta duk da tsinin cikinta baibari sun rungume juna sosaiba.
Cikin tsananin murna rumanah tace,
Tun jiya yakamata ace ke nafara gani da mamani amma shine kikaqi zuwa sai yanzu danace anemoki ina mamani?
Baki washe tace,
Mamani qila wani aiki ya hanata zuwa nima sbd tun jiyan nake yawo a hanyar sashen nan sbd kawai naganki amma bansamu damaba yanxu ana cewa kekenemanmu na aje aikina nazo bakisan yanda na matsu nagankiba rumanah nayi kewarki sosai kinbarni cikin kadaicinki...
Hawaye suka sakata kasa cigaba da maganarta
Rumanah ma hawayen ne suka ciko mata idanuwa ta riqe hannunta tace,
Nayi kewarki nima nuratu saidai bayanda zanyine sbd kinsan da zabi ake bawa mutum nafison zama taredaku duk da ayanxu komai ya canxa arayuwata saidai matsayinku nanan keda mamani bazan ta6a canzakuba arayuwata.
Murmushin qarfin hali nuratu tayi tace,
Mamani bazata taba daukarki ayanda kika dauketaba.
Ni zan cigaba da daukarta matsayin yayar mahaifiyata har qarshen rayuwata bazan taba duba abinda takeminba tunda na saba.
Karkice haka rumanah sbd yanxu akwai banbanci bazanzo na rasataba sbd yi miki wani abu yanxu daidai yakeda rasa rayuwarta.
Karki damu da wannan yanxu zo muci abinci tare nayi kewar hakan sbd bansaniba kozan sake samun irin wannan damar tacin abinci tare dake.
Zama sukayi a babban dining din mai kujeru goma sha biyu nuratu na 'dar 'dar rumanah najanta da magana sbd tasaki jikinta ahaka sukaci abinci nuratu taci abinda takeso ta qoshi suka nufi palonta na qurya nan suka fara fira
Nuratu takalli cikin rumanah dayayi mata kyau matuqa musamman sbd bai sakata qiba ba tsawo yayi sosai.
Murmushi tayi cikin kulawa tace,
Nayi farin cikin ganin rayuwarki ta canxa rumanah gashi zaki haifar mana 'yaya jinin sarauta.
Kallonta rumanah tayi tasaki murmushi kawai sbd tunaninta ba akan firar tasu yakeba.
Agurinta nuratu ta wuni sai tsakar dare ta tafi koshi da sharadin gobe Jakadiya zata saka acanza mata aiki adawo da ita gurinta.
Mamani kuwa sunyi jiran zuwanta harsun gaji bata zoba gashi dokace akan rumanah bazata fita koinaba idanba da qwaqwaran daliliba harsaita haihu.
Washe gari aka dawo da nuratu aiki gurinta duk yanda taso hanata aiki tabarwa sauran kuyangin qi tayi saidatayi.
Kowace safiya da maraice sai Ammy ta Aiko mata da madara mai zafi itada suhailat harsukai kwana uku inda tun tana dannewa harsaida damuwarta ta daqushe kuzarinta matuqa dan ita kadai tasan halinda zuciyarta take ciki na rashin ganinsa gashi da alama bazata sake ganinsa ba saita haihu qila hakan ke sata kwantawa tayi kukanta sbd ji take nutsuwarta na neman gagararta abincima tun nuratu na iya yinta dan ganin taci har abin yafi qarfinta ta sanarda Jakadiya rashin cin isashen abincinda rumanar keyi.
Lokacinda Jakadiya taje ta sanarda ammy hakan yarima na tareda ita bai 'dagoba amma ammy kallo 'daya tayi masa tagano halinda yake ciki musamman dama tana lureda shikansa miskilanci da mulkine yahana agano halinda yake ciki na rashinta.
Jakadiya tayiwa wani irin kallo nan take tagano me take nufi ta gyada kai ta wuce zuciyarta fal tsoro da mamakin irin sonda yarima kewa rumanah haka ta wuce taje kitchen ta bada umarnin ayi dukkanin girkinda akasan yarima maheer naso a shirya a palonsa na musamman zaici abincin daren tareda matansa.
Da daddare koda Jakadiya tazo kiranta cin abinci cikin yanayi na rashin walwala tace batajin dadin cikinta bazata iyacin abinciba yanzu sai zuwa anjima.
Ba musu Jakadiya ta tafi
Koda yafito cin abincin cikin wata irin shiga ta musamman ta kayan shan iska qamshinsa na fita ahankali.
Suhailat dake zaune da cikinta ya kalla cikeda kewarta da tausayinta ya ware mata hannu ta taso ahankali tashige jikinsa ta rungumesa tareda sakin ajiyar zuciya.
Cikin kulawa ya dagota tareda kallon fuskarta da cikinta ya shafi fuskarta ahankali yace,
Hey hw are you?
Murmushin mai ciwo tasaki na qarfin hali tace,
Lafiya klau I missed you""ya fada tana zamewa daga jikinsa ta zauna kan dining sbd ita kadai tasan me ta hango a cikin idanuwansa.
Zama yayi yana sake kallonta ganin jikinta yayi sanyi lokaci 'daya duk saiyaji lissafinsa na sake kwancewa abincin gabaki daya yafita ransa.
Itama abincin fita ranta yayi saidai hakanan ta tsakuri kadan taci ta miqe tazo tayi kissing forehead dinsa tace,
Gud night""ta fice tana mayarda hawayen idonta.
Harta fice bai motsaba sbd damuwa da takaicin kansa dayaji akaro na farko.
Saqone yazowa Jakadiya daga yarima maheer cikin gaggawa ta nufi sashen rumanah ta bada umarnin duk wata baiwa dake sashen rabarshi cikin mintuna biyu kacal.
Babu 6ata lokaci dukkaninsu suka watse bayan koina yadauki sabon qamshi sai masu tsaron qofar shigowa ne kawai.
Kwance take lamo bakin gado idanuwanta a rufe tayi nisa cikin tunani.
Ahankali taji qamshinsa yana shiga hancinta ta bude ido tareda lumshewa zuciyarta na sake shiga damuwa sbd tasan har abada bazaizo sashentaba sbd atarihin sarautar mineelik ba'a taba yin sarki ko yariman dayaje 'dakin matarsaba saidai ita taje to mezaisa shi yazo gurinta.
Shafo fuskarta yayi ahankali cikeda kulawa yana kallon kyakkyawar fuskarta tayi saurin bude idanuwanta dasuka ciko da hawayen ganinsa saita samu kanta da mayarda idanuwanta ta rufe.
Rintse ido yayi cikeda mamakin kansa ya kamo hannunta ya riqe cikin nasa murya qasa qasa yace,
Are you angry?
Bude ido tayi takallesa sbd bata taba tunanin zai kulaba harya tambaya.
Idonta dake kansa yakalla yana sake matse hannunta cikin nasa yace,
Tashi zaune.
Ba musu ta tashi zaune ya saki hannunta ya fito palo tabisa da kallo zuciyarta na qara mutuwa a sonsa,
Jin soyayyarsa takeyi har cikin jini da ruwan jikinta kowane bugawar zuciyarta da sonsa take fita tana fata da roqon Allah yasa kar soyayyarsa tasakata kaucewa hanya takoina koda kuwa sonsa da kishinsa zasu kasheta.
Jakadiya na ganin fitowarsa tayi saurin qarasowa tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik akwai abinda ake buqatane?
Hannayensa ya zuba cikin aljihun wandonsa cikin wani irin miskilanci yace,
Ahado abincin cin mutum biyu.
Cikin qanqanin lokaci ta dibi abincin cin mutum biyo ta jero a tray takawo masa ga mamakinta hannu yasa yakarba ya juya dakin yabarta da baki sake sbd tsananin mamaki.
Duk yanda yaso tasakar masa fuska qi tayi yasamu ya lalla6ata taci abincin ganin shi baici ba yasata daukar abincin itama ta basa babu musu yaringa ci harsaidata kwatanci ya qoshi ta ajiye tana kallonsa da mamaki yadauki tray din yamiqawa Jakadiya dake palo ta fice da kayan.
Brush yakaita har toilet tayo suka dawo ta zauna bakin gado ya zauna kusada ita tareda kallon fuskarta dahar lokacin take kadaran kadahan duk saiya rasa me ke masa dadi baimasan mezaice mataba sbd baisan menene yake faruwaba gabaki daya ta qarasa dame masa lissafi ya dafe goshinsa tareda rintse ido ya bude ya miqe zai tafi kawai yadawo yajawota jikinsa ya rungumeta batareda yace komaiba.
Rungumesa itama tayi tareda barin hawayenta datake riqewa suka gangaro tana sake qanqamesa.
Tun jekadiya na jiran fitowarsa harta gane ba fitowar zaiyiba tabar palon takoma palon farko ta dasa sabon jira.
Tunda tabaro gurinsa mararta tafara ciwo ahankali tana shiga bedroom dinta takwanta tana qoqarin danne ciwon datake ji amma alamarin yafara qarfafa kafin tayi wani yunquri ciwon mara ya taso mata gaba 'daya gashi cikinta yanxune yashiga cikin wata na bakwai.,
Cikin qanqanin lokaci ta tabbarda naquda ce ta taso mata mai tsananin azaba sbd bata taba jin irin wannan ba a duk haihuwarta tun tana boyewa tuni yaci qarfinta koda Carolina taji kamar nishinta a dakin da sauri ta fita zuwa neman mutane duk da dare ya tsala sosai har anyi kiran farko.
Asubar farin yabaro part din yakoma nasa ita kuwa zazzabi ne mai qarfi ya rufeta bayan wankan datayi da asubar amma bata nuna masaba saida ya fice takwanta tana rawar sanyi mararta na mata ciwo ahankali.
Qarfe takwas na safe ta shirya daqyar tana daddaurewa sbd ta masa alqawarin zuwa gurin ammy yin breakfast su hadu acan.
Nuratu na lureda kamar batajin dadi amma tayi shiru sbd ganin kamar batason yin ko magana suka fito suka nufi sashen sultana ana biyeda ita bayi kuwa sai zubewa sukeyi suna bata hanya cikin tsananin girmamawa.
Jakadiya nacan tareda masu karbar haihuwa sashen suhailat hankulansu duk atashe sbd haihuwar tazo mata da gardama matuqa
Shikansa lokacinda labarin ya iso masa hankalinsa ya tashi dan haka ko gurin ammy bai nufaba ya kira doctors din dake karbar haihuwar kasancewar yasansu duka matane suke karbar haihuwa a masarautar in brief sukai masa bayanin haihuwa ce zatayi ta wata bakwai kuma tazo da gardama sosai.
Kafin su isa sashen ammy ta lurada akwai abinda yake faruwa a masarautar sbd koina yayi tsit babu dogon motsi nuratu ce ta sanarda ita suhailat ce ke naquda.
Faduwa gabanta yayi zuciyarta na cikeda mamaki da tausayin suhailar da ita kanta batace komaiba sai sanyi da jikinta yayi tana mata fatan haihuwa lafiya.
Cikeda kaduwa da rashin sukuni ammy ta kalli Jakadiya tace,
Ya Allah karabasu lafiya saidai ina cikin damuwa da fargabar yaya haihuwar rumanah zata zo itama Allah kadai yasan mezata haifa.
Numfashi mai qarfi da sanyin jiki Jakadiya tasaki cikin rashin sanin abinyi itama tace,
Mafita 'dayace itace idan har anason sirrin mutuwar iyayen rumanah yazamo sirri daga gareta muyi adduar kar asamu namiji daga gareta idanma ansamu namijin mutuwarsa itace mafita.
Kallonta sultana tayi da sauri tana sake shiga rudu tace,
Mutuwarsa na nufin qarasa bankado komai Wanda kinsan hukuncinda zamu fuskaanta agun sultan zaifi musan hanyarda zamubi musan wannan sirrin yacigaba da zama sirri kamar yanda sultan yafada tun farko...
Saidai kuma zuciyata na quna da fargabar yanda zan fuskanci rumanah ranarda tasan mune sanadin mutwar iyayenta....
Da qarfi ruwan haihuwa suka 6alle mata lokaci 'daya sbd masifa da tashin hankalinda tashiga lokaci 'daya
Cikin tashin hankali suka juyo cikeda mamaki da tashin hankalin abinda taji kafin suyo kanta ta durqushe agurin cikin tsananin azabar ciwon mara nan take naquda mai qarfi ta taso mata.
#mamuhgee.
[7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_*
_wattpad @mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*32*
Not edited
_A gagguce_
Dafe cikinta tayi cikeda tsananin azaba da wani irin juyi da cikin keyi mata.
Arikice Nuratu ta riqota tana kiran sunanta cikin tsoro da tashin hankali
Su ammy atare sukayo kanta cikin sobon tashin hankali da fargaba
Ammy ta riqota tana kiran sunanta cikin damuwa take kiran sunanta.
A gaggauce suka kamata sukai sashenta da ita inda tun kafin su isa ta qarasa rikicewa sbd azabar naqudar.
Cikin gaggawa Jakadiya ta isa gaban sultan dake zaune cikin royalhall suna jiran haihuwar suhailat ta zube qasa kanta qasa ta sanarda shi ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan.
Da wani irin kallo ya dubeta zuciyarsa na shiga wani sabon farin cikin sbd yasan cikinsu biyun dole asamu namiji insha Allah.
Wani murmushi yasaki na qasaita cikin nuna isa yace,
Kije idan akasamu namiji a mineelik yau namiki na miki alqawarin dukiyarda bazaki iya qirgata da kankiba sai antayaki.
Cikin fargaba tayi godia ta fice hankalinta tashe sbd daga ita har sultana a gigice suke basa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali sbd fargabar haihuwar rumanah dakuma babban sirrin dataji Wanda basusan ta yaya zasu fara fuskartartaba saidai abinda suka sani kome zatayi wannan sirrin bazai fadu garetaba babban tsoronsu da tashin hankalinsu kar Maheer yaji wannan alamari.
Kai tsaye sashen yarima ta nufa lokacin yana zaune palonsa na farko zaune ya dora qafafunsa kan table din dake gabansa ya rufe idanuwansa kallo daya zaka masa kasan kadaici yake buqata baya buqatar hayaniya sbd yanayin naqudar suhailat dayake cinsa musamman yanda yasan ta wahala haihuwarta ta qarshe gashi yanxu har lokacin bata haihuba yana iya sensing azabar datake ciki.
Gabansa Jakadiya ta tsaya tareda rusunawa cikin jimami tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik uwardakina ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan..
Idanuwansa dake rufe ya bude ahankali ya zuba mata suna sake canxawa sbd dama tuni suka canxa sbd zaman jiran na kashesa.,
Miqewa tayi ta fice jikinta a sanyaye sbd gabaki daya ta rasa nutsuwarta jitake kamar zata zauce sbd fargabar tashin hankalinda zai biyo baya idan rumanah ta haihu ta tambayi abinda taji ayau din.
Wayarsa daya kashe ya dauka ya kunna tareda kiran Dr ammenen muryarsa na bayyanarda tsananin damuwarsa da tashin hankalinsa yace mata tabar Dr noorah da nurse agurin suhailat taje gurin rumanah takuma babbatarda tana basa bayanin komai harta haihu idan kuma taga da damuwa takirasa kawai zaizo yakarbi haihuwar da kansa duk abinda zai faru yafaru.
Aje wayar yayi zuciyarsa kamar zata buga,
Yanxune yake sake takaicin haihuwarsu anan sbd acan shine zai karbi haihuwar kowaccensu da kansa musamman ita datake ta farkonta tana tsananin buqatarsa.
Dafe goshinsa yayi ya miqe yayi ciki ganin kamar zai iya rasa hakurinsa yaje musamman dayaga anfara jan lokaci babu wadda ta haihu.
Duk iya galabaituwa kowaccensu ta galabaitu sbd kowacce gadan gadan naqudar ta taso mata babu sauqi,
Duk Wanda ke cikin mineelik hankalinta a tashe yake tsit koina ana jiran tsammani
Sultan ma wannan karon saida hankalinsa yatashi shi fargabarsa kar doguwar naqudar tasa a rasa 'yayan dake cikin.
Ammy duk inda nutsuwa da kwanciyar hankali suke basa tareda ita ko zama takasayi addua tajeyi tana qarawa musamman datake jiyo irin azabarda rumanar ke ciki sbd tana palo suna ciki tareda masu karbar haihuwar.
Zufa mai zafi Jakadiya ta sharce lokacinda Dr ammenen takalli nurse tace,
Get ready ga babyn nan fitowa yanzu Ku kawo komai kusa.
Zufa Jakadiya ta gogewa rumanah data fice hayyacinta cikin tsananin tausayi da tashin hankali take mata sannu.
Cikin wata irin rikitacciyar azaba tayi wani irin nishi mai qara Atake baby ya fado Dr ammenen ta qarasa jawosa tareda yanke uwa ta 'dagasa sama ya buga wani irin kukan jarirai babu qaqqautawa.
Kadan yarage Jakadiya bata fadawa rumanah ba sbd rudewa da ganin abinda aka haifa.
Miqa mata shi Dr tayi jikinta na matuqar tsuma ta karbesa aka nado cikin farin zanin auduga mai tsananin laushi ta qura masa ido tana jera ajiyar zuciya ba qaqqautawa.
Wata sabuwar azaba ta tasowa rumanah cikin tashin hankali Dr takalli cikinta tana cewa nurse wani babyn na zuwa.
Jiki na rawa Jakadiya ta fito ammy data jiyo kukan jariri ta matso bakin qofar jikinta na 'dan rawa zuciyarta kamar zata fado sbd bugawar datakeyi a qofar sukayi karo da jakadiya hannunta na rawa ta karbi jaririn tana qoqarin budewa taga menene cikin rawar murya Jakadiya tace,
NAMIJI NE.
Da sauri ammy ta dago ta kalleta tareda hadiye yawu ta qurawa yaron ido jajir dashi babu inda ya dauko rumanah Sak maheer ne saitaji bazata iya cutatar dashiba.
Nurse ce tazo ta karbesa sbd aankeshi dazasuyi su kintsashi kafin dayan babyn yafado sbd naqudar takoma qasa tsananin wahala take sha ko ayanxun.
Jiki na matuqar 6ari Jakadiya ta isa qofar sashen maheer tun a qofar ta zube tareda 'daga murya tace,
Allah yataimaki uban magajin mineelik ummu-rumanah tasauka lafiya ansamu magajin mineelik da yardar Allah.
Zabura yayi daga kishingiden dayake yana sakin ajiyar zuciya da qarfi yana rufe ido sbd zaman jiran dayake shine abu mafi azabtuwa a tsawon rayuwarsa ayau ya raina zamtaowarsa likita tunda bai taimaki matarsaba lokacinda takeda tsananin buqarsa.
Fitowa yayi cikin wata irin qasaita hannuwansa zube a aljihunsa ya tsaya nesa da jakadiyar yana kallonta kamar tana daukeda abinda aka haifar yace,
Kije ina miki albishir da zama jakadiyar magajin mineelik tareda kyautar werik'i(gold)
Murna fal cikin ranta tace,
Ameseginalehu(godiya)
Miqewa tayi zata fita abakin qofa taci karo da 'yar saqo daga sashen suhailat ta durqusa qasa cikin girmamawa da rawar jiki tace,
Gimbiyar yarima ta sauka ansamu NAMIJI saidai likita tace sanarda yarima bazata sake haihuwaba mmahaifarta tasamu matsala wannan itace haihuwarta ta qarshe.
Zaro ido Jakadiya tayi cikeda tsananin mamaki da farin ciki tareda tausayin suhailat tajuya takoma gurin maheer tasanar dashi atake ya sake lafta mata wata kyautar zuciyarsa na harbawa da qarfi
Ya zauna ahankali tareda lumshe ido yana yiwa Allah godia.
Koda Jakadiya takoma sashen rumanah haihuwar tazo gadan gadan nan wani babyn ya fado Dr ta ciresa nanma sukaga namiji atake aka shiryasu jikin Jakadiya babu inda baya rawa ta zube gaban sultan kanta qasa cikin tsananin farin ciki tace,
Allah yataimaki kakan magajin mineelik ummu-rumanah ta sauka lafiya ansamu 'yan biyu duka MAZA sai gimbiyar yarima itama ta samu 'da namiji
Ina yiwa sultan farin cikin ganin wannan rana mai tarin cikar buri da biyan buqata,
Ayau mineelik ta samu qaruwar 'yaya uku uku duka maza ina sake taya sultan murnar ganin wannan rana.
Wani irin murmushi yake fitarwa mai bayyanarda farin cikin da zuciyarsa ke ciki bamai misaltuwa bane
Dukkanin Wanda ke royalhall din farin cikine mai tsanani a fuskarsa nan take aka buga bell din mineelik aka sanarda haihuwar magajin mineelik atake labarin farin cikin ya bazu koina Ethiopia ta dauka kowa farin ciki yake da wannan burin na qasar daya cika.
Dayake ba qaramar wuya dukkaninsu suka sha ba ana kimtsasu sai bacci banda rumanah data rufe idone kawai zuciyarta cikeda tashin hankali da fargaba tareda baqin cikin abinda kunnuwanta sukaji mata ammy na fada da bakinta.
Hawayen idonta suka gangaro batareda tadamu da gogesuba ta bude idanuwanta dasukai ja hawayen nacigaba da 6alle mata.,
Idan kunnuwanta sun jimata daidai ammynta ke fadar sune suka kashe mata iyaye kenan ba mutuwar Allah sukayiba qarfi da yaji aka rabasu da rayuwarsa,aka rabasu da 'yarsu,Ashe shiyasa aka 'yantasu???
Girgiza kanta tayi hawayenta na tsananta tace,
Ammy bazatayi hakaba nice banji daidaiba,ammy bazata iya kashe kowaba bare iyayena.
Sakin siririn kuka tayi tareda kifa kanta a pillow.
Suhailat kuwa bacci tayi sosai sbd ta galabaita fiyeda yanda ta tsammata saidai tana haihuwar taji batajin komai.
Lokacinda aka kaiwa maheer yaran duka yana tareda khaleefa daya iso ranar khaleefa ne yakarbi sauran biyun maheer kuwa Wanda aka fara