Showing 72001 words to 75000 words out of 81312 words
lokaci 'daya yayi wani irin canzawa saidai kuma abin tausayin shine yana cikin wannan halin ne sbd halinda rumanah take ciki.
Gangarowa hawayenta sukayi ta sauke kai ahankali cikin sanyin murya da nutsuwa tace,
Ranar farko dana fara ganinka aranar nafara Sonka maheer ibn abdulshams abdallah,,
Kaine namiji 'daya da zuciyata ke so saidai babban kuskuren danayi shine na nacewa na aureka a tunanina zaka soni wata rana saidai ashe babban kuskure da shishigi nayiwa qaddarar datake jirana..
Kallon cikin idanuwansa dasukai jajir tayi tasaki murmushi mai ciwo tace,
Haryanxu ina sonka maheer abdulshams saidai bazan iya cigaba da zama dakaiba maheer sbd girman soyayyar danake maka bazanso zuciyata ta tsanekaba.
Ayau ina roqonka sbd darajar 'Yayana da soyayyata ka sauwaqemin na samu rayuwar data cancanta dani wannan rayuwar ta gidanka ba tawa bace na tabbatarda tawa tana wani guri tana jirana.
Rintse ido yayi akaro na farko dayaji ruwa sun ciko idanuwansa sbd ita ya girgiza kai yanason magana amma yakasa.
Ta riqo hannunsa tana qoqarin maida hawayenta tace,
Wlh idan nacigaba da zama dukkaninmu zamu cutu qarshe dukkaninmu zamu fada hanyoyinda bazasu amfanemu ba sbd zan iya canzawa na zama wata daban,
Canzawata zatasa ka tsaneni
Tsanata dazakayi zaisa matarka ta canza sbd zata riqa ganin itace abar so nikuma zata riqamin kallon mahaukaciya qarshe dukkaninmu zamu zama abinda bama fatar kasancewa...
Na yarda da aurenka shine qaddarata kuma na karbeta da hannu bibbiyu kuma ina fatar Allah yasa na cinye wannan jarabawar zuwa yanxu sbd zuciyata tafara gazawa dan haka nake roqon alfarma ta qarshe daga gareka dan Allah free me from this relationship
Wlh I'm in so much pain zuciyata zata iya bugawa kowane lokaci please free me maheer.
Girgiza kai yayi yana kallonta da idanuwansa dasuka canza daqyar ya iya furta,
Suhailat I need you in my life please don't.....
Girgiza kai itama tayi kukanta na qoqarin qwacewa tace,
Wlh bazan iyaba maheer,
Wlh mutuwa zanyi I've endured enough,
Duk abinda kamin na yafe maka ina fatar kaima ka yafemin
goodbye yarima maheer abdulshams.
'Daukar abeel tayi ta rungume wani irin ciwo mai zafi nacin zuciyarta ta rintse ido hawaye masu zafi suka gangaro mata tasaka hannu ta goge fice dakin.
Kodata fita palo Carolina da sauran masu hidamarta duk suna tsaye kowanne idanuwansa cikeda hawayen rabuwa da ita.
Kallonsu tayi tareda sakin murmushin qarfin hali ta fice sbd bazata iya cewa komaiba ta nufi sashen rumanah.
Zaune take a palonta tayi lamo ko motsi batayi ta qurawa gefe 'daya idanuwanta dasukai jajir suka bushe dukkanin wani abincin karyawa an Jere mata a gabanta saidai ko motsi batayiba bare takalli abincin gashi har rana tafarayi,
Ganin halinda take ciki yasa dukkanin masu hidimarta da masu tsaronta yau jikinsu asanyaye yake ko babban motsi ba'ayi a sashen tsit kakeji.
Da shaqaqqiyar muryarta datasha kuka tai sallama tashigo palon taganta zaune da alama agurin ta kwana tun jiyan sabd ganin kayan jikinta.
Ahankali taqaraso gabanta ta durqusa ahankali ta dora mata abeel ajikinta.
'Dago idanuwanta tayi a wahalce ta kalleta takalli abeel ta tashi zaune daidai tareda qurawa abeel 'din ido ta 'dago takalli suhailat ahankali ta iya bude baki sbd tsananin nauyi da ciwon kan datakeji tace,
Shine da kansa yace yabaki bayan nima nace nabar miki sh......
Nagode sbd kema kinyi abinda bakowace uwace zata iyaba ciki hardani kuwa sbd bazan ta6a iya bawa kowa 'dana dana haifaba,
Ina qaunar abeel qauna mai tsafta sbd shi 'din 'dan maheer ne kuma ina kallonsa amatsayin jemal dina dana rasa saidai zamansa hannuna bamai yiyuwa bane Allah ya albarkaci rayuwarsa.
Juyawa tayi ta nufi qofa ta fita batareda tasake cewa komaiba sbd batason bayyanarda hawayenta gaban rumanah tabarta da jin cewar kamar itace silar rabuwarsu.
#mamuhgee
[8/6, 1:17 PM] ummul aulad: _*TARAYYA*_
_wattpad@muhgee_
_Haske writers association_💡
*42*
_Not edited_
Kasa motsi tayi tabi bayanta da kallo harta fice ta jima tana kallon qofar kafin ta maido kallonta kan abeel daya farka yana kallon fuskarta ta rintse ido tareda rungumesa tana jin wata sabuwar damuwar sbd rashin sanin abinda yafaru yanxun.
Ahankali ta lumshe idanuwanta mafarkin abbanta datai yau yana dawo mata.
"Ummu-rumanah kibi mijinki a dukkanin umarninsa matuqar basu saba addininki ba sbd shine gatanki kadai yanxu aduniya,
Ki gujewa mulki sbd haqqoqin dubban mutane da bazaki iya daukaba sbd rauninki na zamowa 'ya mace kibarwa Allah komai ki gyara aljannarki."""
Kalaman da mahaifinta ya sanarda ita a mafarki kenan saidai abinda takasa ganewa shine ta yaya zata sauka mulkin batareda ta kawo sauyi da zaman lafiya a qasar ba.
Bude ido tayi tareda jinjina shawararda zuciyarta ke bata dan kawo qarshen komai saidai hakan wani abune mai girma dayakeda matuqar hadari saidai dole zata aikata hakan koda hakan shine ajalinta zatayi dan kawo qarshen rayuwar da alummar qasar suka samu kansu.
Tabbas qaddararta itace ta koro iyayenta daga gida ta kawosu nan sbd gashi abinda yafaru tun qarnikanda ko kakanninta ba'a haifa Ashe tana cikin qaddarar gashi itace zata kawo qarshen abin.
Hawayen tausayin mijinta da 'danta tareda ammy ne suka gangaro mata ta sauke kanta tareda sakin kuka ahankali sbd tasan sune zasufi kowa kukan rashinta arayuwa sbd sune wainda takeda matuqar mahimmanci arayuwarsa ta yanda rashinta zai matuqar ta6a rayuwarsu.
Sunansa ta furta ahankali cikin zuciyarta sbd tasan mutuwarta zata tarwatsa zuciyarsa zatabarsa cikin mawuyacin hali saidai tasan suhailat na nan zata kula dashi.
Miqewa tayi ta nufi dakinta ta kwantarda abeel ta zauna gabansa ta qura masa ido tana fidda sautin kuka ahankali sbd kukane takeyi sosai.
Tana fitowa sashen rumanah kai tsaye shashen ammy ta nufa bata nuna mata komaiba tasanarda ita zataje Mali.
Ammy dake fama da ciwon kai mai tsanani takalleta da idanuwanta ahankali tace,
Allah ya kiyayeki ya hadaki da alkairin dake cikin tafiyar.
Amin ta furta ahankali tareda juyawa ta fice dan dama su amah suna Mali tuntuni da aka fara wainan rudanin.
Motocin dazasu kaita airport na fitowa daga masarautar tasaki wani irin kuka ahankali tareda rintse idanuwanta tana furta Allah yabani juriya da danganar rabuwa dakai maheer.
Suna isa airport basuyi minti ashirin ba suka tashi daga qasar Ethiopia zuwa mali.
Lokacinda ta wuce tabarsa daqyar ya iya fita yabar dakin ya nufi part dinsa yana qoqarin danne halinda zuciyarsa ke ciki amma yakasa saida jiri ya zaunar dashi kan kujera da qarfi ya rintse ido ga mamakinsa saiyaji kamar hawaye na neman zubo masa yayi saurin dafe kansa da hannu bibbiyu jin kamar zai rabe masa sbd yasan bazai ta6a iya cireta aransa ba.
Ahankali ta qaraso bayansa ta tsaya tareda zuba masa ido tana sake danne hawayenta..
Bude idanuwa yayi ahankali sbd he can feel her presence.
Juyowa yayi suka hada ido atake takasa riqe kukanta tafara girgiza kai tareda sakin kukan
Ya ware hannunsa 'daya alamar tahowa garesa da gudu ta qarasa ta fada jikinsa ya rungumeta sbd shikansa yana buqatarta kusa ayanxu.
Kukan datakene yafara bashi mamaki ya 'dago fuskarta ya kalleta atake yaji kwanyarsa ta qarasa hargitsewa ya bude baki zaiyi magana tayi saurin 'dora bakinta cikin nasa tana tsiyar hawaye.
Ahankali tasaki bakinsa tana kallon fuskarsa dake bayyane da damuwa cikin tsananin sanyin muryar kuka tace,
Ina sonka yarima maheer abdulshams,
Kaine farin ciki da rayuwar ummu-rumanah bulama,
Kaine abinda zuciyata bazata iya jure rashinsa ba,
Ina maka qauna mai girma a tun ranardana fara ganinka agabana.,
Wlh bazan taba iya aikata kuskurenda zai nesantani dakaiba bare kwatanta rayuwa babukai..
Kasan mutuwane kawai banyiba a daren ranar daka furta rabuwa dani maheer abdulshams,
Ummu-rumanah bazata iya rayuwa babu kaiba sbd kaine jigonta kuma jagorarta..
Share hawayenta tayi tareda jan numfashi kukanta na rage sauti tace,
Wlh haryanxu zuciyata zafi da takeyi da zancen daka fadamin kana tunanin zan iya rayuwane wlh mutu.....
Maidata yayi jikinsa da sauri ya rungumeta yana girgiza mata kai dan bazai iya ko maganaba.
Qanqamesa tayi tana cewa,
Na tuba ka yafemin.
Dora hannu yayi abakinta yana sake rungumeta ahankali ya furta,
Maheer abdulshams loves you ummu-rumanah bulama.,
Ummu-rumanah bulama kece mahadin rayuwar maheer abdulshams.
Murmushin qarfin hali tasaki ahankali tareda sake kwanciya ajikinsa.
Shiru sukayi dukkaninsu ajiyar zuciyarta kawai ke fita akai akai
Sai kuma shi dahar lokacin tunani da damuwar tafiyar suhailat ne kawai cikin ransa,
Tana buqatar shan iska zai barta tasamu sarari idan yagama da matsalar mineelik ya tabbatarda rumanah ta fita daga cikin wannan masifar zaije yadauketa su koma Georgia gabaki 'dayansu.
A daren ranar nan ta kwana gurinsa tareda abeel saidai kusan dukkaninsu babu mai nutsuwar yin bacci saidai shiru sukayi a kwance kowannen da abinda yake damun zuciyarsa.
Washe gari koda aka tashi aka tararda Allah yayiwa mamani rasuwa
Koda aka dudduba dan tabbatarda meya kasheta aka gano saran maciji ne har guri biyu a wuyanta da gefen hannunta sbd wani irin canzawa da fatarta tayi takoma Kore Kore alamar qarfin dafin macijin mai ha'darine.
Lokacinda Jakadiya ta kawo mata saqon mutuwar suna zaune kan dining maheer na tilasta mata cin abinci.
Kallon Nuratu dake jera musu sauran abincin breakfast din tayi da sauri tareda miqewa tsaye sbd ganin halinda tashiga lokacinda Jakadiya tagama fadar saqon da sauri suka rungume juna nuratu na sakin wani irin kuka ahankali tareda rintse ido tana girgiza kai.
Hawayen tausayin nuratun ne itama suka ciko idanuwanta ta bubbuga bayanta cikin son daure kukanta dake zuwa na tausayin kansu sbd sun tabbata marayu iyayensu dasukazo nan suka haifesu sun rasu sun barsu ayanxu sune kadai 'yan uwan kansu.
Cikeda tausayawa Jakadiya takallesu cikin sanyin murya tace,
Allah ya gafarta mata laifukanta ya sadata da rahamarsa ina miqo ta'aziya ga assultana da 'yar uwarta nuratu akan wannan rashi.
Ganin tana neman rikicewa da kuka yasashi yiwa Jakadiya wani kallo
Atake tayi gyaran murya tana cewa,
Nuratu kizo muje kiyiwa mahaifiyarki addua kafin a fice da ita.
Sakinta rumanah tayi tareda kallon fuskarta tana hawaye tace,
Allah yabaki haqurin rashinta yasakamiki dauriyar yimata addua.
Kallon rumanar tayi sbd jin bata ambatarwa mamanin rahamar ubangiji ba ahankali ta bude baki cikin tsananin sanyin murya tace,
Ina roqorwa mahaifiyata yafiya ki yafe mata sbd qauna da amincin dake tsakanina dake dan......
Kije na yafe sbd qauna da amincin dake tsakaninmu saidai haqqin ran 'yayana data dauka wannan tsakanintane da ubangijinsu shida ya haliccesu.
Ahankali ta furta,
ina fatar Ubangiji ya yafe mata.
Juyawa tayi ta fice rumanah ta juya ta zauna tana qoqarin saita nutsuwarta kartayi kuka saidai Sam takasa sbd duk yanda mamani taqita takashe mata 'dah ita din tatace.
Ta bayanta ya rungumeta jikinsa ahankali yana cewa,
Sorry luv.
Shigewa jikinsa tayi tana daina kukan dan tana buqatar rarrashin gabaki daya ta rasa ina ta dosa da rayuwarta.
Jin tayi shiru yasashi shafa kanta cikin sanyin murya yace,
Allah baya barin haqqin wani akan wani gashinan kin gani.
Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya sbd tunowa da abinda zatai dan kawowa kowa sauqi da qarshen masifar sbd a yanxu abeel dintane kawai ake jira ya gia yahau dan haka bazata taba bari 'danta yahau wannan karagar ba sbd ajikinta tanajin masifa da balain dake cikinta yana yawo cikin jininta ita kadai tasan yaya takeji take daurewa sbd shirye take da yaqar komai akan qarfin soyayyar datakewa mijinta.
Abu taji na fitowa ta hancinta ta taba ahankali tashafo taga jinine da sauri ta goge sbd kar Maheer yagani.
Shigowar ammy yasashi sakinta suka miqe gaba dayansu murya a tausashe suka gaidata ta amsa tana kallon rumanah dataga tayi wani irin fayau kamar ba jini a jikinta ta tsaya gabanta tareda riqo hannunta suka koma kan royal cushions dake palon suka zauna tana kallonta cikeda mamaki tace,
Rumanah ki fadamin gskia lafiyarki kalau?
Gefen Maheer daya kafeta da ido ta kalla ta sauke kai cikin sanyin jiki tace,
Lafiyata kalau.
Girgiza kai ammy tayi tace,
Rumanah wlh bakida lafiya wannan abun na cin jininki duba kiga kina canzawa rumanah karki rufeni kifadamin gskiar abinda kikeji.
Dawowa yayi kusada ita ya zauna yana zuba mata ido cikin tuhuma ya riqo hannunta zai duba tafin hannunta ta zame hannun tareda girgiza kai tace,
Lafiyata klau banajin komai....
Hancinta ya qurawa ido cikin daukewar numfashi yakai hannunsa ya shafo jinin dake gangarowa daga hancin ya kalla jikinsa na rawa ammy ma cikin tsananin tashin hankali take kallon jinin...
Ganin suna kallonta tayi saurin shafowa taga jini sosai ta miqe tsaye wani irin jiri ya dibeta ta yanke jiki gurin ta fadi idanuwanta rufe jinin na sake ballewa daga hancinta.
Cikin masifaffen tashin hankali sukayi kanta ammy tuni tafara kuka tana kiran sunanta
Shikuwa daukarta yayi hankali amatuqar tashe yayi bedroom dinta da ita ya kwantar ya fidda waya atake yakira khaleefa dasu dr abeena tareda sauran manyan doctors nasu.
Tissue yasa yana goge mata hanci saidai Sam jinin yaqi tsayawa gashi tafara wani irin jijjiga a rikice ya qanqameta jikinsa yana kiran sunayen Allah ahankali muryarsa na rawa dan yasan bazai iya kwatanto rayuwa babu itaba.
A gigice dukkaninsu suka iso tareda nurses da duk wasu kayan aikinsu atake suka fara qoqarin tsaida jinin dan maqala mata oxygen sbd numfashinta daya fara mata wuyar ja.
Dafasa khaleefa yayi tareda kallon yanda duk jikinsa ya 6aci da jini cikin kulawa yace,
Kaje daga palo gurin ammy zakafi samun nutsuwar bari mu dubata.
Palo khaleefa ya rakosa ya zauna kusada ammy yakoma ciki shi.
Riqo hannunsa ammy tayi cikin tsananin damuwa da tausayinsa dana abeel dake rungume ajikinta tace,
Zataji sauqi insha Allah.
Jinjina mata kai kawai yayi sbd ko bude baki bazai iyaba bare magana.
Atake rashin lafiyar assultana ya yada koina nan koina gari yafara 'daukar tsit sbd rufe shaguna da kasuwanni.
Acikin masarautar kuwa Sam ba wani dogon motsi tako wane bangare sbd jiran tsammanin farfadowarta.
Daqyar suka samu suka tsayar mata da jinin aka maqala mata oxygen tareda ruwa da sauran abubuwan da suka kamata amma har lokacin bata farfado ba.
Bayan duk sungama abinda zasuyi aka bar nurses uku dan kulada ita suka fice.
Lokacinda yashiga yaga yanda takoma lokaci daya
Ya zauna bakin gadon tareda 'dora hannunsa kan nata ya rufe ido
Shikadai yasan radadi da ciwon da zuciyarsa ke ciki ganinta ahaka.
Ahankali yace,
Tana farfadowa zamu wuce bazan iya zama anan ba kuma.
Dafasa ammy tayi tareda yarda da abinda yafada dan itama tagaji da nan 'din tana buqatar nutsuwar rayuwa kota maida hankali gurin istighfar ga ubangijinta.
Sai tsakiyar dare ta farka tareda bude idanuwanta ahankali ta qurawa masa ido yana zaune bakin gadon hannunsa cikin nata a damke idanuwansa a lumshe saidai tasan ba bacci yakeyiba.
Ahankali ta bude baki da siririyar murya ta furta,
Abu abeel..
Bude idanuwansa yayi da sauri tareda tashi zaune daidai yana kallonta fuskarsa na bayyanarda tsananin farin cikin daya shiga na ganinta.
#mamuhgee.
[8/7, 7:36 AM] ummul aulad: _*TARAYYA*_
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association_💡
*43*
_Not edited_
Murmushin qarfin hali tasaki tareda sake damqe hannunsa dake cikin nata tana kallon fuskarsa dashima ita yake kallo yana yiwa Allah hamdala cikin ransa.
Tashi zaune takeson yi ganin kamar batada qarfin jiki yasashi tayarda ita zaune tareda cire mata cannula dake hannunta ya gyara mata zama sosai.
Cikin sanyin murya da kulawa yace,
Ya kikeji yanxu?
Girgiza masa kai tayi tana kallon fuskarsa.
Jakadiya ce tayi knocking qofar dakin ahankali ta sanarda zuwan sultana.
Zare hannunta tayi cikin nasa tareda lumshe ido sbd yanayin datakeji ajikinta har lokacin.
Cikin nutsuwa ammyn tashigo idonta kan rumanah din
Hankalinta ya'dan kwanta ganin ta farka harta tashi zaune.
Qarasowa tayi tareda miqawa maheer hannu ya kama hannun da hannunsa daya cikin nutsuwa yace,
Ina kwana ya ammy?
Murmushi tayi tace,
Lfy klau..tana kamo hannun rumanah tace,
Ya jikin?
Naji sauqi ammy"""ta fada cikin qarfin hali da danne ciwon datakeji.
Miqewa yayi ya fita yana amsa kiran khaleefa dake kiransa kan maganar test result 'dinta dasuka fito.
Ammy dakanta ta kamata takaita toilet tayo wanka da brush tana fitowa taga doguwar riga mara nauyi akan dressing chair ta dauka tasaka ta shirya tana qoqarin busar da kanta sbd wankan tsarkin datayi na haihuwa ammy tashigo tareda nuratu dake daukeda babban tray Jere da breakfast ta ajiye zata juya rumanah takira sunanta ahankali.
Tsayawa tayi tareda juyowa cikin ladabi
Rumanah ta miqa mata hand dryer cikin sanyin murya tace,
Taimakamin.
Ammy na ganin hakan tasan magana zasuyi ta kalli nuratu tace,
Tayi breakfast.
Jinjina kai tayi alamar tou.
Ahankali take busar mata da gashin babu Wanda yayi magana acikinsu.
Tana gamawa ta daure mata gashin tareda ajiyewa a natse.
Miqewa tayi itama ta nufi inda take sallah tana idarwa ta dawo kan couch din dakin ta zauna har lokacin nuratu na tsaye kanta a sunkuye cikin tarin damuwa da kadaici.
Ahankali takamo hannunta ta zaunar da ita kusada ita ta kalli fuskarta kafin ta sauke kanta itama ta qurawa gabanta ido cikin sanyin murya tace,
Kiyi hakuri nabarki alokacinda kike tsananin buqatata,
Kin kuladani kin tayani kuka kin rarrasheni alokacinda na rasa nawa iyayen saidai ni nakasa miki hakan alokacinda kike buqatar wani ataredake..
Kallonta nuratu tayi hawayen datake riqewa suka gangaro mata tace,
Wlh idan nace miki bana buqatarki ataredani na miki qarya rumanah saidai yanayin rayuwa daya kawo bambamci arayuwarmu ayanxu rayuwarki daban take data baiwar datafi kowace baiwa baqin jini sbd mahaifiyarta data.....
Rintse ido tayi tareda budewa idanuwanta na cikowa da hawaye ta juyo ta kalleta cikin sanyin murya tace,
Ada damuke bayi rayuwarmu tafi kwanciyar hankali da nutsuwa tareda dadin gudanar da rayuwarmu,
Rayuwar bayi wata rayuwace mara yanci amma wlh wani lokacin tafi rayuwa irin wadda nasamu kaina aciki,
Nuratu idan zaka roqi Allah abu ka roqi alkhairinsa sbd wlh rayuwata ina baiwa tafimin kwanciyar hankali akan yanxu.
Gangaro mata hawaye sukayi sbd jin tausayin kanta da abinda zata fada tace,
Nuratu na 'yantaki daga yanxu ke ba baiwa bace kinsamu 'yancinki,
Babu wata rayuwar jin dadi da kwanciyar anan dan haka za'a maidaki gida acan zaki samu rayuwar kwanciyar hankali damukai burin samu idan ni bansamuba zan qoqarta gurin ganin ke kinsamu...
Kallonta nuratu takeyi hawayenta na tsananta gudu tace,
Tare mukayi alqawarin komawa gida.....
Zanzo wata rana nima idan nauyin alummar dake kaina ya sauka
Zanzo idan inada rayuwa da lafiya sbd burinane nima nahadu da dangin iyayena dan haka karkiyi wasa da damarki kice zaki jirani kije Allah zai sake sadamu da yardarsa.
Kuka nuratu ta fashe dashi tana girgiza kai tace,
Bansan ta yaya zan fuskanci mutanen da basusanniba nikadai nace musu dukkanin iyayenmu da sauran danginsu da akaje dasu sun mutu ba...
Itama kukan takeyi sosai saidai bazata iya cewa komaiba sbd wannan shine gatan datasan zata yiwa nuratu takoma gida ta fuskanci sabuwar rayuwa cikin amincin Allah.
Kuka sukeyi sosai na rabuwa da juna daqyar rumanah ta miqe ta bude wardrobe ta dauko wata jaka dake daukeda qatuwar sarqar zinari ta miqawa nuratu tareda juya mata baya sbd kukan datake riqewa tace,
Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi.
Ta baya nuratu ta rungumeta tana sakin sabon kuka tana cewa,
Kisani zan jira zuwanki har qarshen numfashina.
Daqyar suka saki juna suka fito palonta na biyu inda suka tararda ammy da maheer da khaleefa tareda Jakadiya suna jiran fitowarsu.
Fuskokinsu suka bayyanarda halinda suke ciki.
Ya qurawa fuskarta datai jajir ido kafin ya dauke kai