Showing 51001 words to 54000 words out of 81312 words
haihuwa ya karba akaro na farko dayaji jikinsa yayi sanyi sbd soyayyar yaron dayaji shima yau yahaifi magajin kansa bama na mineelik kawaiba.
Qura masa idanuwansa yayi ganin yaron shine Zak sai lips din mahaifiyarsa daya dauko ya sa hannu ahankali ya shafo lips din tareda sakin wani irin murmushi qasa qasa yayiwa yaron addua kafin ya furta,
ABEEL HASSAN.
Kallonsa khaleefa yayi cikeda farin ciki ya maimaita sunan yana jinjina kai kafi ya karbesa ya miqa masa babyn suhailat da ba'ason motsasa sosai.
Qura masa ido yayi cikeda tausayinsa da qaunarsa mai qarfi shima shiya dauko Zak saidai zamansa qarami sosai yasa yafisu haske.
Addua yamasa sosai cikin rada rada ya furta,
Jemaal.
Koda ya karbi Hussain din abeel abrar bayan yamasa addua ya rada masa,
ABEEL HUSSAIN
Koda aka kaisu gurin sultan kowa saida yatabbatarda yau ranar daban take arayuwarsa ya 'dagasu daya bayan daya yayi musu addua kafin aka sanar dashi sunayen da yarima maheer ya rada musu sultan mai damuba sbd ayau angama masa komai arayuwa ya 'daga abeel cikin babbar murya yace asanarda kowa ga magajin mineelik ABEEL HASSAN.
Atake akaje dakin tarihi aka saka sunansa da sunan mahaifiyarsa nan aka fara shagulgulan haihuwar.
Har dare ammy bata samu ganin rumanah ba sbd tunda tayi wanka take rufe a dakinta tace bata buqatar kowa Hutu take buqata.
Lokacinda aka kawo mata yaranta qura musu ido tayi hawaye na gangaro mata sbd idan bar aka iya raba iyayenta da ita za'a iya rabata da 'yayanta saidai batajin hakan zata iya yiwuwa koda zata rasa rantane.
Rungumesu tayi tareda rufe ido qaunarsu data mahaifinsu na shigarta tako ina.
Da daddare lafiyyan abinci kala kala aka aika gefen kowaccensu aka jera.
Duk yanda Jakadiya da ammy sukaso ganinta qin bari tayi ta dasun shigo zata rufe ido tana bacci idan sun fita zata cigaba da kukanta.
Kukane takeyi na rashin Sanin abinyi sbd ko ganin kowa batason yi.
Lokacinda labarin haihuwar tasamu adama da 'yar dakinta mamani kadan yarage adama bata yanke jikiba mamani kuwa kasa daurewa tayi saidatayi kuka taji sauki sauqi cikin ranta.
Koda aka kawo mata yaran saka musu albarka saidata kai zuciyarta qololuwa gurin bugawa kafin ta iya kallonsu idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki tasaka musu albarkar dole.
Suna fita ta miqe batareda takalli mamani dake matsar hawayeba cikin tsananin tashin hankali tace,
Duk yanda za'ayi ayi yaran nan bazasukai ranar sunansuba batareda sunbar duniyaba kije yanxu ina buqatar kadaici gobe zan fada miki abinda zakiyi sbd inason alhakin mutuwarsu ya rataya akan kakarsu da jakadiya sbd inason qulla gaba mai tsanani tsakaninsu da yarima tareda matansa kuma inason sultan ne da kansa zai yankewa sultana hukuncin kisa ta yanda abin zai riqa bibiyarsa yana damunsa da haka zansamu sauqin aikina akansa.
Acikin daren yakira suhailat yaji yajikinta tareda jemaal duk da khaleefa yadubasa sosai yafadi dokokin daza'abi kafin suna shi dole za'a koma Georgia dashi sbd yanayinsa acan za'a fara kula dashi.
Duk yanda yaso ganinta yasan abune mai wuya saidai kuma bayajin zai iya bacci bai dubotaba bayan baqar wahalar dayasan tashiga yau gurin haihuwa saidai koda ya aika asanarda Jakadiya taje tayi ma sashen isonsa ta sanardashi har lokacin bata fitoba taji jiki sosai hutawa takeyi haka ya hakura saidai asubar fari ya isa dakinta lokacin tana zaune bakin gado tasaka yaran agaba hawaye nabin fuskarta.
Qamshinsa yasata rintse idanuwanta hawayenta na sake gudu.
Zama yayi kusada ita tareda riqo hannunta baice komaiba ya kwantarda kanta jikinsa sai kawai tasaki kukan datake ruqewa ahankali
Cikeda mamaki da damuwa ya kalleta zaiyi magana ta zame daga jikinsa tana tsaida hawayenta cikin dasashiyar murya tace,
Kaina na ciwo ina buqatar hutawa.
Da mamaki yakalleta saidai baice komaiba ya miqe ya fice
Ta saki sabon kuka cikin rashin Sanin abinyi.
Duk inda hankalinsu ammy yake yatashi dashi kansa maheer din sbd kwana uku da haihuwar ko kadan rumanah takasa bari ko 'dayansu ya ganta duk wani tashin hankali suna ciki
Ta hargitse tarasa abinyi gabaki daya ta birkice shikansa ta hanasa ganin kanta bare yasan meke faruwa babban tashin hankalin daya riskesu shine sanarwar da akayi za'a bawa uwar magajin mineelik kujerarta ta uwar sultan.
Sam ammy ta rasa ina zata saka kanta shikansa baya cikin nutsuwa sbd bazai taba bari ta karbi sunan uwar sultan ba gashi dole zata karba itace zata bawa duk Wanda takeso riqon kwarya.
Yau kwanansu biyar da haihuwar dukkanin yaran suna sashen ammy tun safe.
Tunda sukazo abeel hassan ke kuka sosai anmayardashi gurin hamaifiyarsa saima qara birkicewa da yayi nan hankula suka tashi tuni sultan yasa atara duk masu magani da likitocin mineelik amma sai qara rikicewa yakeyi nan hankalin rumanah itama yayi masifar tashi ta rikice.
Cikin tashin hankali suka dunguma zuwa royalhall inda ake duba yaron kowa hankalinsa atashe yake.
Kallo daya yayiwa rumanah yaji lissafinsa yasake kwancewa kafin yayi wani yunquri sarkin gida yossouf Kaleb yashigo jikinsa na matuqar rawa ya zube gaban jakadiya yayi mata magana qasa qasa hankali tashe jikinsa na wani irin mazari.
Zaro ido Jakadiya tayi cikin sabon tashin hankali jikinta yadauki muguwar rawa kowa hankalinsa nakanta anajiran jin saqon menene
Ta zube gaban sultan tareda sauke kanta jikinta na tsananta rawa cikin muryar tashin hankali da tsananin fargabar rasa rayuwarta tace,
Allah yataimaki sultan ina cikin baqin cikin sanardakai ankama baiwa mamani da dafin baqin maciji tabawa abeel Hussain da jemaal antabbatarda sun rasu saidai ankamata.
Rumanah dake zaune ta miqe a firgice jikinta na rawa saidai ko daga qafa batayiba ta yanke jiki ta fadi agurin.
Cikin tashin hankali yayi kanta kai tsaye yadauketa yabar palon su ammy na mara masa baya hankali tashe musamman sultana da a sashenta suke shaf tashin hankalin abeel hassan yasa suka mantasu acan.
Sultan kuwa numfashi ya sauke cikin wani irin yanayi ya miqe tsaye idanuwansa na canzawa.
Suhailat na zaune tana shan magani daqyar sbd ciwon ciki da jirin datake fama dashi tun safiyar yau din
Jakadiya ta shigo mata.
Murya na rawa tace,
Ina neman afuwar saqon baqin cikin danazo dashi Allah yakarbi ran jemaal........
Bata qarasaba suhailat ta miqe tsaye atake jini ya 6alle mata ta yanke jiki ta fadi.
#mamuhgee
[7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*33*
_A gaggauce_
Cikin tsananin tashin hankali Jakadiya tasa akayiwa Dr ammenen kiran gaggawa koda ta iso itama hankalinta tashe yake da jin abinda yafaru atake suka fara qoqarin tsayar da jinin daqyar yarage zubowar sosai saidai bata farkaba sbd allurar dasukai mata sbd jininta yayi matuqar hawa mai muni idan ta farka awannan halin zata iya samun paralyz.
Sai bayan sunbaro gurinta aka sanarda maheer abinda yasameta lokacin yana qoqarin ganin rumanah ta farfado sbd duk iya abinda zaiyi ta farfado yayi bata farfadoba tashin hankalinda yake ciki yanxu yafi kowane tashin hankali na rayuwarsa,
Rasuwar yaransa gakuma halinda rumanah take ciki yanxu kuma ana fada masa suhailat ma...dafe goshinsa yayi tareda fitarda numfashi mai qarfi da zafi idanuwansa na sake canzawa.
Ammy sbd tashin hankalinda take ciki ko tsayuwa sosai bata iyayi tsaye take gaban gawarwakin yaran a palonta kallo daya tayi musu ta dauke kai hawaye na ciko idanuwanta sbd ganin yanda kalar jikinsu takoma mai duhu sbd dafin daya shiga jini da jijiyoyinsu sosai.
Zaman dirshan Jakadiya tayi tareda dora hannu 'daya akai tana jinjina wannan baqar rana data zo musu koda suke tsananin buqatar haihuwar maza gashi ansamu mazan amma tun ranarda aka fara naqudarsu masifa tafara saukar musu saidai wannan masifar dasuke ciki yanxu mai hadari ce sbd koda misali sunanka yafito cikin wannan zancen mutuwace hukuncinka..
Jikinta na rawa ta miqe ta dauki gawar su biyun ta nufi fada qafafunta na wani irin rawa daqyar ta iya kai kanta gaban sultan ta zube tareda shimfidesu ahankali tana furta,
Tuba nake da kawo mugun gani gaban sultan da muqarabansa.
Kallo daya yayiwa likitan gargajiyansu ya taso yazo gaban yaran ya durqusa yadauki abeel Hussain yadubasa tareda zura hannu cikin bakinsa ya Ciro yakalla ya kalli sultan ahankali ya sunkuyar dakai ya girgiza kai alamar yariga ya rasu.
'Daukar jemaal yayi yaduba shima ya tabbar musu da yarasu.
Atake sultan yakalli kaleeb cikin zallar 6acin rai da nuna ikonsa yace,
Akai mai laifin kurkuku mafi tsanani ahadata maciji mafi hadari har zuwa gobe kafin tafadi Wanda yasata sbd bayin kantabe batada isar dazata iya yiwa ko bawan mineelik kallon banxa bare iya kashe jinin sultan.
Cikin zaquwa kaleeb yace,
Angama sultan...ya fice yana kwatanto irin azabar dazasu ganawa mamani.
Cikin wani irin mummunan yanayi na firgici da tashin hankali ta farka tareda miqewa zaune jikinta na bata irin rawa tafara qoqarin tashi yayi saurin riqeta yana son kallon cikin idonta amma taqi tsayawa gabaki daya bata cikin hayyacinta fixgewa takeyi da qarfi yasake riqeta tareda girgizata da qarfi yakira sunanta.
Tasaki wani irin kuka mai qarfi tareda fixgewa daga jikinsa ta zube qasa tafara kuka sosai tana qanqame jikinta sbd wani irin ciwo da ra'dadi mai zafi takeji cikin ranta kamar zuciyarta bazata iya daukaba.
Sake riqota yayi ya rungume jikinsa da qarfi duk yanda taso qwacewa kasawa tayi tacigaba da fidda kuka mai radadi.
Wani irin ciwo da baqin ciki takeji na cin zuciyarta numfashinta har sarqewa yakeyi gurin kukan.
Kasa magana yayi sbd radadin da zuciyarsa ke ciki na rashin 'ya'ya biyu lokaci 'daya dakuma ganinta cikin wannan halin.
Ammy kallon Jakadiya tayi idanuwanta na qoqarin boye qwallarta tace,
Ya akayi mamani tashigo nan harta bari aka kamata domin na tabbarda tana sane tabari aka kamata akwai abinda take nufi da hakan Wanda shine tashin hankalina.,
Meyasa bata kashesu a dakunan uwayensuba sai agurina?
Innalillahi, allahumma ajirni fi musibati
Wannan wace irin masifa ce mai wuyar cinyewa.
Cikin sanyin jiki a raunane Jakadiya tace,
Alqawarin Allah ne zai tabbata sbd sbd ayanxu alamu sun fara bayyanar mulkin mace a mineelik Wanda hakan na nufin ba'a zubarda jiniba yanxune za'a zubar dashi.
Girgiza kai ammy tayi da sauri cikin tsananin fargaba da rudu tace,
Rumanah bazata taba zama mai zubarda jinin bayin Allah ba,
Nayi gudun haka kowa yakasa fahimtata,
Na roqi Allah a zuci da fili akan kar rumanah ta haifi namiji idanma ansamesa yazo babu rai amma hakan bata faruba yanxu bansan ta ina kuma wannan masifar ta 6ullo ba.
Duk yanda yaso ganin rumanah tadawo nutsuwarta abin ya gagara saima zuru datayi da ido kukan yadaina fita saidai hawaye kawai ko motsin kirki bata iyayi ta rakube gefe guda ta takure kanta.
Lokacinda aka shigo aka sanarda ita zuwan ammy dubata bata motsaba saima rufe idanuwanta datayi hawayen ciki suka gangaro tunani abubuwa da dama na dawo mata,
"" mafita 'dayace karta haifi namiji idanma ta haifesa mutuwarsa itace mafita""
"" yaya kike tunanin zan fuskanci rumanah ranarda ta San cewar mune sanadin mutuwar iyayenta""
Rintse idanuwanta tayi da qarfi nauyi da zafin zuciyarta na qaruwa saidai batason barin zancen yashigeta a irin yanayin datake ciki yanxu sbd tanason tayiwa ammy fahimta mai kyau bazataso abinda kunnuwanta sukaji mata ba yazama gaskia.
Ammy kasa haquri tayi ta nufi dakin lokacin maheer yaje dubo suhailat.
Har ammy taqaraso gabanta bata motsaba daga inda take takure idanuwanta jajir.
Cikeda tsananin kunya da tausayinta murya na rawa tace,
Rumanah har abada bazan iya cire qaunarki arainaba sbd qaunace Allah yasakamin cikin raina Wanda kisani har abada bazan iya yin abinda nasan zan cutatardake ina fatar zaki riqe hakan aranki...Allah yaji qan abeel Hussain.
Juyawa tayi ta fice jikinta asanyaye sbd tana iya hasaso wasi wasi azuciyar rumanah.
Tana fita rumanar sulale ta kwanta agurin tasaki sabon kuka tana dafe qirjinta dake mata zafi da wata irin tafasa.
Cikin wata irin kaca mai tsananin nauyi da zafi aka na'do mamani da nauyin kacar yasata tafiya ahankali a duqe sbd ko qafarta daqyar take dagawa sbd nauyin kacar datake 'daureda ita.
Aka bude wani tsohon kurkukun dayafi shekara goma ba'a shigesaba aja jefata ciki da qarfi kanta ya bugu da bango take goshinta ya fashe da jini ta fitarda numfashi daqyar sbd azaba gashi batada hannun shafawa taji sbd irin 'daurin da'akayi mata ko numfashi daqyar take fitarwa.
Ta lumshe ido cikin azaba ta bude idon takalli qofar dishi dishi take gani sbd ba qaramar buguwa tayiba gashi anyi mata wani irin duka na rashin imani dan kariya biyu akayi mata a hannu 'daya.
Wani irin kwando aka bude tareda jeho abinda ke ciki aka rufe qofa
Wani irin baqin maciji tagani ya bude kansa yana fitarda huci.
Mummunar faduwa gabanta yayi wasu irin hawayen azaba da tsoro tareda baqin ciki suka gangaro mata jikinta ko qarfin dazaiyi rawa bashidashi sbd ti6is akayi mata.
Tana kallo macijin ya kwantarda kai yayi cikin wani qaton rami dake gurin Wanda shikansa ramin baza'a rasa wani macijin acikiba ko abinda yafisama.
Maganarta da adama ta tuno tana fargabar kar komai yaqi tafiya yanda suka tsara.
""" idan kikai nasarar basu wannan dafin suka sha zasu mutu atake kuma ki tabbatarda ankamaki duk wuya da azaba karki ce nice kice sultana ce Wanda kowa yasan hukuncinta na kisa ne kafin akasheta za'a bani matsayinta na sultana nikuma zanyi amfani da wannan matsayin na hana akasheki kuma daga lokacin namiki alqawarin matsayin Jakadiya kintashi daga baiwa har abada saidai kuma idan kika fadi sunana kisani babu 6ata lokaci dukkaninmu za'a kashemu amma idan kikace itace nizan kubutar dake kinga burinki na shekara da shekaru yacika ga 'yanci da dukiyar kanki dazaki tara""""
Numfashi tasaki a wahalce tana sake qarfafawa zuciyarta dan cika sauran aikin dan kuwa koda ta mutu tasan burinta akan zuriar bulama da asma'u yacika.
Suhailat data farfado ahankali hawaye kebin fuskarta suna sauka kan qirjinta idanuwanta arufe sbd ko hannunta daqyar take iya motsasa.
Qunci ne arayuwarta da zuciyarta,
Rayuwarta ta lalace batada wani sauran farin ciki,
Ta rasa mijinta badan ya rasuba,
Ta rasa rayuwar aure mai farin ciki,
Ta rasa lafiyarta,
Ta rasa mahaifarta gurin haihuwa ga abinda ta haifa ta rasashi mai zaunawama ya rungumeta ya rarrasheta ta rasa
Wace irin rayuwace mai tattareda garari take ciki?
Wani irin kuka mai qaramin sauti tasaki zuciyarta na mata ciwo mai tsanani
Kewar iyayenta da 'yayanta takeji sbd sune kadai sukasan zafinta da damuwarta.
Qarasawa yayi bakin gadon tareda Rungumeta da sauri yana jin tausayinta fiyeda kansa sbd yasan tafi kowa cutatuwa sbd tafi rasawa tunda ba wata haihuwar zata sakeba.
Akaro na farko arayuwarta taji batason kusancinsa agareta sbd nauyi hakan ke qarawa zuciyarta saidai ko motsi sosai bata iyayi bare ta zame jikinta hakan yasa wani sabon kukan qunci zuwar mata ahankali.
Sosai ya lurada batai farin ciki ko jin sanyi da ganinsaba akaro na farko arayuwar aurensu daya hango wani yanayi daban akansa wanda ba sonsa bane atareda ita ya rufe ido cikin wata sabuwar damuwar yanajin tausayin kansama sbd wata jarabawace Allah yake jarabtarsa da ita akan rumanah wadda idan baiyi taka tsantsanba zai tashi da Rabin jiki ranar lahira saidai kuma baisan yaya zaiyiba sbd sonta yazama halitta ajininsa.
Ahankali ya furta,
Allah yaji qan jemaal.
Sakinta yayi ya miqe tareda ficewa batareda ya qara kalma 'daya ba.
A wannan daren mineelik ba kowa yasamu damar kwantawaba bare ya rintsa sbd dukkanin dole da masautar na cikin tasa kalar damuwar.
Rumanah dai duk yanda akayi da ita taci abinci ko motsi taqiyi daga inda take idanuwanta sun bushe sunyi jajir ko gani sosai batayi sbd kumburin idanuwanta.,
Suhailat kuwa har lokacin bata iya kwakwaran motsi sai hawaye da ciwon qirji dayake cinta ita kanta anyi anyi taci abincin amma ko bude ido taqiyi sai hawaye take zubarwa.
A rayuwarsa wannan ne karo na farko dayaji yayiwa sarauta da gidan sarauta wata irin muguwar tsana sbd yasan son mulkine yasa akai hakan,
Ya tabbatarda kisace ta tabbata akan baiwar datayi da wainda suka sakata saidai bayajin zai tsaya ganin hakan gobe zaayi hidimar radin sunansu a goben zasubi jirgin dare su koma dan idan yananan zuciyarsa zata bugane da halinda matansa suke ciki musamman suhailat datake buqatar kulawa sosai.
Ammy da jakadiya kusan a zaune suka kwana ko ruwan arziki babu Wanda ya iya sakawa maqoshinsa sbd tashin hankalin dazai iya faruwa gobe sbd duk Wanda sunansa yashiga koda misali ne cire kansa ya wajabta gashi a sashen ta abin yafaru shine babban tashin hankali da damuwar dasuke ciki musamman dasukasan wacece mamani.
Ayau mineelik acike takeda duk wata masarautar dake zagaye da maqwaftaka da ita tareda wasu sarautun wasu qasashen da dama sbd gabatarda sunan magajinnta dakuma miqawa uwar magajin mineelik kambun saukewa da 'dora sabon sultan.
Wannan matsayin daza'a bata ayau shine abu mafi ha'dari da tashin hankalinda yake ciki ayau
Ammy duk yanda taso daurewa kasawa tayi saida hawayen baqin cikin datake ciki suka gangaro mata tun a daren jiya ta hana su ganta bare ta sanarda ita hadari da kuma illar abinda zata fada.
Saidai alqawarine shi ya daukarwa kansa zai tabbarda ta miqa mulkin nan ga sultan ya dauketa sunkoma adaren yau din.
Lokacinda aka hallara dan qaddamarwa saqo ya isowa sultan uwar magaji batada lafiya bazata iya fitowa.
Kai tsaye aka fara qaddamar da komai aka radawa abeel Hassan sunansa tareda qaddamar da sunan ummu-rumanah acikin littafin tarihin mineelik amatsayin uwar magaji.
Nan take masu rubuta tarihi aka bude paging fara rubuta nata.
Daga ammy har yarima maheer babu Wanda ya halarci taron kuma sarai sultan yagano manufarsu tayin hakan zasu fuskanci hukuncinsa daga baya ayanxu baiwa mamani ce agabansa zai bata wata irin mutuwa mai firgitarwa itada wainda suka sakata ga 'yan baya.
Koina yayi tsit jiran hukuncin sultan akeyi lokacinda mamani ta tabbatarda Jakadiya ce tasakata amatsayin itama sultana ce ta aikota.
Tsita akayi kowa wuta ta dauke masa musamman sultan da mamakin baiwa mamani yakamasa sbd yafi kowa sanin sultanarsa bazata aikata hakanba,
Tabbas wannan baiwa mai taurin raice saidai ji da ganin hukuncin sultan kawai tajeyi batasan waye sultan ba.
Kallo daya yayiwa kaleeb cikin babbar murya yace,
Aje ajefawa zakuna ita su cinyeta da ranta akawo qashinta asa 'dakin kayan tarihin mineelik...
Da ido adama dake dake gefensa tayiwa sultan aqeel magana ya gyara zamansa tareda kallon sauran sarakunan dake Royal hall din yace,
Idan aka kashe wannan baiwa batareda ta fadi wainda suka sakataba baka kai qarshen matsalar a mineelik ba sbd gobe ko jibi magajin ne da kansa za'a kashe kuma hakan zaisakawa mutane wasi wasin hukuncinka tunda ta fadi wainda suka sakata anshare anyi kamar bata fadaba.
Ido cikin ido yakalli sultan aqeel yace,
Babu Wanda ya isa yayi wasi wasin hukuncina a qarqashin mulkina da ikona ko wanene batareda na ciyar da namansa ga dabbobinaba.
Murmushin mulki sultan aqeel yasaki yace,
Hakane kuma idan kanason hakan yacigaba da faruwa saika nunawa mineelik Kaine sultan kuma Kaine kake yanke hukunci kowane irine akan ko wanene.
Nan take sauran sarakunan suka marawa gaskia baya suka qalubalanci sultan akan adalci idan har sultana ce tasakata to