Showing 75001 words to 78000 words out of 81312 words
yanajin damuwar ganinta hakan cikin zuciyarsa.
Gefen ammy ta qarasa ta tsaya ahankali ta bude baki tafada musu tafiyar Nuratu din zuwa qasarsu.
Ammy sosai ta yiwa nuratu addua da fatan alkhairi tareda cewa jakadiya nuratun ta sameta kafin washe gari ta wuce.
Bayan fitarta khaleefa yabi bayanta da kallo kafin maheer yayi masa magana da ido suka fita.
Bayan fitarsu ammy ta zaunar da ita tasa aka kawo wani abincin breakfast din.
A palon yarima maheer suka zauna cikin nutsuwa yace,
Khaleefa zaka karbi duk wani bayanin tarihin my queen da mahaifiyar nuratu ta bayar ka kaita har gida kafin ka karbi takardun iyayenta kayi amfani dasu ka nemomin asalinta.
Shiru khaleefa yayi yana sake tauna zancen sbd tafiyar ta jirgin ruwa ce sbd ta ruwa kawai zasubi su bulla garinsu nuratun kai tsaye a yanda akace gashi bai cika son tafiyar ruwa ba saidai kuma dole haka zai daure saidai suyi amfani jirgin dazasu isa cikin kwana biyu.
Acikin daren rumanah tayi kukan tafiyar Nuratu,
Iyayensu sunzo qasar dasu acikinsu gashi su zasu koma batareda ko dayansuba.
Washe gari bayan sallar asuba suka wuce bayan khaleefa yakarbi duk wani tarihi na asalinsu daga hannun anees mai haqqin tattara tarihin sarakunan masarauta Wanda aka ya karbi bayanan daga mamani ya rubuce a littafin tarihi kafin rasuwarta.
Bayan tafiyarsu takira Jakadiya ta miqa mata wani zungureren saqo a rubuce tace takaiwa harooun sarkin fada.
Lokacinda Jakadiya takaiwa harooun saqon yana gama karantawa jikinsa yayi matuqar sanyi da abinda ke rubucen saidai kuma yasan hakan datake shirin yi shine qarshen abinda yake bibiyar mineelik dan haka babu bata lokaci ya fita dakansa yaje gurin Negus sarkin qirar mineelik yayi masa bayani ya karbo littafin zanen karagar mulkin qarnikan baya yadawo yabawa jekadiya takai mata.
Lokacinda Jakadiya takawo mata shirgegen littafin mai nauyi ko budesa batayiba tace,
Kije na zabi lamba ta biyar.
Babu musu Jakadiya takoma ta mayar tana jinjina alamarin rumanah sbd idan Allah ya taimaka abinda take shirin yi shine daidai.
Acikin daren ranar Negus da yaransa suka fara aiwatarda aikin qera sabuwar karagar mulkin mineelik wadda basu ta6a qera abu mai kyau da darajartaba sbd abubuwan dasuka narka ana hadawa dasu gurin qirar.
Lokacinda Jakadiya ta sanarda ammy abinda yake shirin faruwa numfashi ammy tasauke cikin danne fargabarta dan batason tunanin faruwar wani abin saidai zataje tayi magana da sultan sbd shine yasan komai ciki da waje gameda komai na karagar fiyedasu.
Da daddare bayan ko ina yayi tsit sultana ta fito ta nufi sashen sultan kai tsaye aka barta tashiga sanin matsayinta gurin assultana.
Zaune yake hankali kwance yana karatun wani shirgegen littafin tarihi yana shan madara mai zafi da aka kawo masa kullum kafin ya kwanta sbd tana qara lafiyar qwaqwalwa.
Kallo daya yayi mata yasaki murmushi yana cigaba da abinda yakeyi.
Qarasowa tayi kusadashi ta zauna cikin girmamawa ta gaidasa tana kallon littafin dayake karatu tace,
Meyasa haryanxu bazaka sauke dukkanin wani tunani na sharrin shaidanba ka fuskanci gaskia ka bita,
Ka tubarwa ubangijinka ka ajiye duk wata niyya da qudirinda bana alkhairi ba wlh Allah zai karbi tubanka sbd shi mai yafiyane ga bayin dasuka tubarmasa.
Wani irin murmushi yasaki tareda rufe littafin ya ajiye gefe ya kalleta yace,
Baiwarki kuma matar 'danki tayi babban kuskure na aikata abinda ta aikata sbd kaf tarihin mineelik babu wani sultan da aka taba muzantawa saini sultan abdulshams jinin ajani....
Numfashi tasauke cikin takaici da baqin cikin halinda mijinta yasamu kansa idanuwanta na cikowa da hawaye tace,
Son zuciyar kakannin kakanninka shine yasamu ahalinda muka tsintsi kanmu aciki karka bari zuciya takaika aikata irin kuskurensu.....
Katseta yayi da cewa,
Meya kawoki ki fada kai tsaye sbd nasan akwai abinda yakawoki a wannan lokacin.
Kallonsa tayi ganin Sam idanuwansa da zuciyarsa sun rufe..
Cikin sanyin murya tace,
Assultana na shirin canza mineelik gabaki 'daya da wata......
Da sauri ya kalleta yana ajiye cup din hannunsa sbd girgiza da zuciyarsa tayi.
Cikin bayyanarda tsananin tashin hankalinsa yace,
Zata aikata wani babban kuskuren sbd rusa karagar gabaki 'daya na nufin rusa rayuwarta sbd zata rushene tareda jininsu jamal na qarshe daya hau karagar yayi mulki akanta......
Shiru yayi zufa na karyo masa sbd yasan dagashi sai itane suka rage aduniya wainda suka taba zauna karagar har sukai mulki akanta,
A bangaren jini kuwa shikadaine jininsu na qarshe dayayi mulki akan mineelik ita 'din ba jininsu bace akwai yiyuwar abin bazai shafetaba koya shafeta saidai ta nakasta amma shi babu tantama rayuwarsace ke rawa jinin qarshe nasu jamal.
Wannan rumanah gabaki 'daya rayuwarta ta zame masa masifa mai barazana bai taba tunanin ko namiji zai iya fuskantarsaba ya girgizasa bare 'yaya mata daya dauka marasa amfani saigashi ko acikin 'yaya matan ma baiwace take barazaga rayuwarsa,
Bazai Bari su aikata hakanba dole ya juya musu zancen..
Gyara nutsuwarsa yayi cikin vasarwa yace,
Karku bari ta aikata hakan sbd rayuwartace acikin hadari dan kuwa haqqine na qarshe zai fita akanta.....
Murmushin baqin ciki ammy tasaki tareda girgiza kai hawayenta suka sauko tace,
Yanayinka da kulawar daka nuna yasamin kokwanto akan amsarka dan haka mun dangana munbarwa Allah komai zamu barta takawo qarshen mineelik duk abinda Allah ya qaddaro zamu runguma mu dauki dangana.
Miqewa tsaye tayi zata fice ya riqo hannunta akaro na farko dayaji tsoro da fargaba sun ziyarci zuciyarsa ya bude baki daqyar yace,
Karki bari ta aikata sbd rayuwatace a hadari kuma tatama na cikin hadari.
Hawayenta suka qara gudu ta sunkuyar dakai tanajin zuciyarta na karyewa sbd qaunar mijinta uban yayanta saidai kuma kodan sbd 'yayanta da jikokinta zataso akawo qarshen masifar mineelik.
Zame hannunta tayi ahankali tace,
Allah yazaba mana abinda yafi zama alkhairi.
Ficewa tayi jiki asanyaye zuciyarta na sake karyewa saidai bazata bari ta karayaba hakan da rumanah zatayi shine daidai insha Allah.
Zaune yake bakin gadonsa yayi shiru tareda zurfi cikin tunani Sam bayajin nutsuwa a zuciyarsa wani irin rashin sukuni yakeji..
Ahankali tashigo dakin rungume da abeel jikinta amatuqar sanyaye sbd jikinta datake yana tsananta dan ko yanxu kafin tafito saidata yanke jiki ta fadi jini na fita hancinta saidai bata fita hayyacinta ba kuma ta hani Jakadiya fadawa kowa abin yafara tsanani.
Qarasowa tayi ahankali ta kwantarda abeel kan sofa tadawo gefensa ta zauna ahankali tareda dafa hannunsa takalli fuskarsa.
Shima ita ya kalla ta sakar masa murmushi ahankali tareda riqe hannunsa ta lumshe ido sbd abinda taji yana taso mata ta danne yanayin daqyar tasake qaqalo murmushi tana kallon hannunsa dake cikin nata ahankali tabude baki tace,
Karka saki hannuna har lokacinda zan shaqi numfashin qarshena a duniya,
Ka zamo jiqo kuma majingini arayuwata
Ka hanani 'daukar hanyarda zata batardani zuwa duniyar daba tawaba,
Qarfin soyyarka yaci qarfin abinda nakeji ajikina saidai bansaniba ko hakan zai jima shiyasa a yanxu nake roqonka da har abada karka rabu da suhailat sbd itace macen da soyayyarta bazata taba barin cuta ta kutso kai rayuwarkaba..ni tamkar baquwace a rayuwarku ba lallaine na qarasa rayuwa acikinkuba.......
Matse hannunta dake cikin nasa yayi yana rintse idanuwansa dasukai jajir..
Hawayen datake riqewane suka 6alle mata ta kalli fuskarsa datai jajir ya rintse idanuwansa ta shafi fuskarsa hawayenta na tsananta tace,
Maheer abdulshams nagode da soyayyarka gareni..
Bude jajayen idanuwansa yayi yana kallon hawayenta dake gudu sosai yakasa magana sbd radadi da nauyin da zuciyarsa tai masa sai kawai ya rungumota jikinsa.
Ahaka suka kwana cikin wani irin sanyin jiki dana zuciya.
Kwanansu khaleefa biyu a ruwa aranar na uku da yamma sosai suka isa saidai kuma sunsha wahala sosai sbd tuni bakin ruwan yazama border saida sukasha wata irin wuya kafin suka samu wucewa da taimakon wani 'dan asalin qauyensu mamani din.
Bayan wucewarsu duk yanda sukayiwa saurayin bayani bai ganeba sbd basajin hausa ko kadan har gwara nuratu tanaji kadan kadan sbd su mamani da umman rumanah sunayi musu tun suna qanana saidai ya jasu kan mashin dinsa sukayi wani irin mugun overload yajasu dan kaisu cikin qauyen daya samu canji ba laifi.
Tafiya mai tsawo sukayi kafin suka isa qauyen mai tsananin girma da cikar mutane.
Gidan shugaban qauyen yakaisu cikin sa'a lokacinda suka isa yana gida.
Kallonsu aka taru anayi sbd ganin baqaqen labarawa musamman khaleefa dayake cikakken dan Ethiopian asali.
Bayan anbasu guri sun zauna ya fidda tambarin masarautar dasuka fito ya miqawa shugaban ya kalli nuratu yayi mata magana yace,
Kiyi musu bayaninmu yanda zasu gane ko yayane.
Gyara zama tayi muryarta na rawa tace,
Munfito daga qasar Ethiopia ne qarqashin masarautarsu,
Sun siya bayin dasuka fito daga wannan nahiyar tsawon shekara ashirin da biyar yanxu.,
Acikinsu akwai mamani da asma'u dasuka tafi da juna biyu acan suka haifi 'yaya mata dukkaninsu Wanda 'daya daga cikin 'yayan itace ni 'dayar kuma a yanxu itace sarauniyar qasar.
Da wani irin mugun mamaki suke kallonta musamman shugaban garin daya zamto kutti mijin mamani yasake kallon nuratu da gabaki 'daya take kamar yar asalin Ethiopia itama.
Cikin nutsuwa yace,
Ke 'yar wacece acikinsu?
Ni 'yar mamani ce.
Wata irin kabbara tsoffin gurin suka dauka cikeda murna da mamakin wannan alamari kutti yace,
Ina iyayenku?
Dukkaninsu Allah yayi musu rasuwa mamani ko sati batayiba yanxu haka.
Sake daukar kabbara sukayi cikin jimami da tsananin girmama wannan alamari.
Ahankali ta zayyane musu komai gameda rayuwarsu kafin ta gabatarda khaleefa amatsayin Wanda zai karbi takardun dukiyar asma'u da bulama dan neman asalin sarauniya ummu-rumanah.
Bayan dogon koke koken saduwa da baqin cikin rashinsu mamani dasu bulama nan kutti yagabatarwa da su nuratu kansa amatsayin mahaifinta.
Duk wani zuriar gidan antaru an karbi nuratu da hannu Bibbiyu da zuciya daya da wainda suka San faruwar abin da wainda ma ko haihuwarsu baayiba nan dai kowa yataru ana farin ciki.
Ganin yanayin garin yasa khaleefa yanke shawarar wucewa dan sake kutsawa cikin Nigeria dan gabatarda abinda yakawosa.
Kutti ya basa takardun dasuka tsufa sosai ga sanyin ruwa daya soma lalatasu tun wancan lokacin saidai ba laifi yana iya ganin rubutun dake jikinsu atake ya karancesu daganan ya roqi alfarmar tafiya da wani yaron kuttin dayake jin yarensu kadan kadan sbd aiki dayakeyi a border dinsu.
Da mashin din salee suka isa inda zasu samu mota bayan sunyi tafiyar awowi akan mashin din.
Motar dazata kaisu Maiduguri kai tsaye suka hau inda duk hankalin khaleefa yatashi sbd ganin inda yasamu kansa dakuma wata irin azabar wuyar tafiya data fara gigitasa.
Gaf da asuba suka isa Maiduguri kai tsaye wani lafiyayyan babban hotel suka sauka anan yayi baccin wahala ga zazzabin dakeson kamasa na baqar wuyar dabai taba shaba.
#mamuhgee
[8/7, 7:37 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers associationš”_
*45*
Not edited.
Saki jikinsa yayi sbd wutar data daukewa jikinsa da wani irin qarfi ammy ta jijjigasa tareda kiran sunanda da qarfi ya durqusa tareda jawota jikinsa ya dauketa gabaki 'daya yabar gurin da ita.
Anso tsayarda nadin sarautar amma haroun ya fitarda saqonta na gaba dake cewa duk abinda zai faru kar a tsayarda nadin dakuma takardarta tagaba dake cewa a raba mara masarautar biyu a rushe Rabin a gina masallacinda yafi kowane girma a qasar Ethiopia.
Hakan yasa aka cigaba da nadin yayinda sultan dake zaune har aka gama bai motsa daga inda yakeba saida aka watse aka gano ya rasu zaune agurin gakuma jinin da aka ganin ya digo daga hancinsa.
Lokacinda su negasi suka rufu akanta dan ceto rayuwarta alokacin ne aka zo da saqon rasuwar sultan Wanda ya girgizasu ya qarasa wargaza dukkanin sauran nutsuwarsu musamman ammy data kasa riqe kukanta maheer yayi saurin rungumeta yana riqe nasa hawayen sbd Allah yasani yana qaunar mahaifinsa duk mugun halinsa sbd koyaya ya zama mahaifinsane.
Cikin qanqanin lokaci rasuwar sultan da halinda assultana take ciki tareda canza karagar mineelik suka yadu 'yan jaridu da kafafen yanda labarai sukaiwa masarautar wani irin dandazo ana yada abinda ke faruwa.
Dukkanin iyalan marigayi abdulshams sun halarto cikin tsananin baqin cikin wannan rana data riskesu musamman 'yayan marigayiya adama dasuke ganin sun rasa uwa da uba.
Da maraice akai jana'izarsa inda dubban alumma na nesa dana kusa suka hallara inda yawan jama'arsa yasa maheer jin sanyi sanyi aransa tareda yiwa mahaifinsa adduar samun rahamar Ubangiji.
Duk damuwar dayake ciki ta halinda rumanah take ciki bai koma gurinta ba sai dare bayan an watse.
Kai tsaye sashen ammynsa ya nufa inda ya tararda ita tareda sauran 'yan uwansa ya qarasa kusada ammyn ya zauna yana kallonta cikin nutsuwa da tausayawa ya riqo hannunta ahankali ya iya furta,
Allah yaji qansa ammynah.
Kwantarda kanta tayi kafadarsa tareda cewa "amin" da muryarta data shaqe kafin ta 'dora da fadin,
Kaje gurin rumanah dan sanin halinda take ciki duk da meenah da jakadiya na gurinta.
Jinjina kai yayi jikinsa na qara sanyi da tuno wani tashin hankalin dayake ciki.
Lokacinda ya isa sashenta har lokacin bata farfado ba sai jinin daya tsaya Wanda suke sakaran jinintane yayi matuqar qasa sosai.
Zaune ya kwana gabanta yana mata addua cikin wani irin hali dabai ta6a tsintar kansa aciki ba.
Washe gari koda akaga bata farkaba hankula sukai matuqar tashi musamman da jikinta yayi wani irin fari fari Kore Kore ga 'yan jarida dasuka kasa suka tsare a masarautar sunason ganawa da sarauniyar data kafa sabon tarihi a qasar daba tataba.
Duk wani kalar likiti na turai da gargajiya an nuna qwarewa amma abu yaci tura gashi alamunta na sake 6aci ranar da akai uku aranar gabaki dayansu suka tattara suka nufi Georgia..shi,ammy da jakadiya data samu 'yancin rayuwarta itama sai sauran 'ya'yan da kowace takoma inda take aka bar sabon sultan dan gabatarda mulkinsa cikin aminci.
Suna sauka kai tsaye motar asibiti tazo daukarsu aka wuce asibiti dasu cikin tashin hankalinda yafi na farko sbd saki jikinta daya farayi.
Matsayinsa a babbar asibitin garin yasa ana isa da ita dukkanin likitocin dake nan suka taru aka fara qoqarin gano matsalar cikin gaggawa cikin tashin hankali da mamakin yanayin matsalarta sbd basu taba cin karo da irin hakanba.
Ammy daqyar ta iya zama gida saidai gabaki 'daya hankalinta da damuwarta na asibitin gabaki daya cikin kwana ukun ta rame tayi wani irin sanyi ko doguwar magana bata iyawa.
Har gari ya waye likitoci na kanta duk wata dabararsu da qwarewarsu sun nuna dan ganin ta farfado saidai Sam bata farfado ba saidai fatarta data fara komawa daidai sbd jinin da aka saka mata kusan leda biyu hakan yasa suke sakaran idan fatar ta gama komawa daidai ta farka.
Daqyar yake iya hadiye yawun bakinsa sbd tsananin bushewar bakinsa da maqoshinsa,
Duk wata nutsuwarsa da tunaninsa sungama barin jikinsa idanuwansa tuni suka qanqance ko gani bayayi sosai da idonsa dukkanin abokanan aikinsa sun tausayawa halinda yake ciki shiyasa suma gabaki daya hankalinsu tashe yake da ganin ta farfado 'din.
Khaleefa aranarda suka wuce aranar yasauka Ethiopia ya tararda abinda ke faruwa kasa kwana yayi duk da rashin lafiyarsa washe gari yabi jirgin asuba sbd yasan aminin nasa na tsananin buqatarsa.
Har yamma bata farkaba khaleefa ma saukarsa garin alhaji babaye yakirasa sbd news din dasuka gani gameda abinda yake faruwa a qasar nan yaqara yasanardasu abinda yake faruwa nan hankalinsu yayi matuqar tashi suka fara shirye shiryen tahowa cikin gaggawa.
Qarfe goma na dare ta bude idanuwanta dasukai wani irin shigewa sukai nauyi da ja.
Atake dukkanin likitoci suka sake hawa kanta cikin gaggawa da nuna qwarewa tareda fatar samun nasarar sanin matsalarta.
Kasa miqewa yayi sbd saki ga gabobin jikinsa sukayi sbd fargabar abinda za'a fada masa saidai khaleefa ne ya dafasa yana jinjina masa kai alamar qwarin gwiwa ganin halinda yake ciki.
Wasu sabbin dogayen hours suka 'diba suna qoqarin gano matsalar wadda suka gano daga qarshe wadda tayi mummunan 'daga hankalinsu haka suka ringa fitowa jiki amatuqar mace zuciyoyinsu ba dadi sbd dukkanin hotunansu da test test dinsu sun tabbatar musu da abu 'daya.
Dr Edward ne yafito qarshe yana zare glasses dinsa yakalli maheer da khaleefa yace,
Can we talk in my office pls..
Tashi tsaye maheer yayi tareda kallon qofar dakin da take yakalli Dr Edward din yana rintse idanuwansa da abinda za'a fada masa yace,
Just tell me dr Edward I c........
Dafasa Dr Edward yayi cikin tsananin tausayi ganin daqyar yake iya bude bakinsa yayi magana cikin sanyin murya yace,
I'm really sorry Dr m.a shams matarka ta rasa gangar jikinta bazata taba gara aikiba ma'ana tanada rai tana gani tana numfashi tanaji saidai bazata iya motsa jikintaba ko kadan bare magana har abada.
Wani mugun jirine ya dibesa khaleefa da Dr Edward sukai saurin nufarsa zasu taresa ta rigasu taresa cikin kulawa da tausayawa.
Khaleefa ne yakalleta cikin mamaki Dr Edward kuwa jinjina mata kai yayi alamar ta kula da maheer din yana buqatarta fiyeda koyaushe.
Shikuwa idanuwansa na ganinta baisan sanda ya sake fadawa jikinta yana qoqarin tsaida hawayensa saidai Sam basu tsaiduba saida suka zubo ya sake qanqameta yana cewa,
Suhailat please pray for me wlh zuciyata zafi takeyi I just can't live without her sbd wannan ma baida banbanci da mutuwa agareta.
Murmushin tausayinsa tasaki cikin sanyin murya tace,
Insha Allah zata warke
Nayi maka alqawarin zamowa majingini agareka duk lokacinda kake buqatata wannan alqawarin yananan haryanxu kuma nayi alqawarin cika makashi har qarshen rayuwata kuma zan tayaka jinyarta harta ji sauki sbd sonka shine qaddarata maheer abdulshams..
'Dagowa yayi kalleta da idanuwansa itama hawayen takeyi tana murmushi ahankali yaji wata irin soyayyarta mai tsafta tashiga zuciyarsa akaro na farko cikin wata irin rawar murya yace,
I love you suhailat sbd kece hasken rayuwata dakike tallafoni koyaushe.
Wasu hawayene suka gangaro mata ta rintse ido tana kwabar zuciyarta dake neman shegala da kamansa datasan ta samesune sbd nuna qaunarta ga rumanah saidai matuqar qaunarta ga rumanah zata jawo masa soyayyar mijinta to tabbas ta shirya samun soyayyar mijinta ta hakan.
Duk yanda ya 'daga hankalin likitocin asibitin akan abinda sukace dole ya dangana yadauki qaddara sbd result din dayane.
Ko ammy saidata kwana ta yini tana kukan halinda rumanar ke ciki da Wanda yashiga sbd gabaki daya ya birkice musu ko abinci sai ammyn tayi kuka yake iya shan abu mai ruwa ga suhailat data zamo batada wata hidima saita kula da dukkaninsu sbd sundawo gida.
Idan yazo ya zauna kusada ita haka zai riqe hannunta cikin nasa ya qura mata ido
Itadai hawayene kawai ke iya gangarowa ta gefen idonta musamman idan ammy tasata gaba tana kuka kokuma shi idan yazo ya zauna yasaka gaba ya qura mata ido tana iya hango mawuyacin halinda yake ciki.
Ranarda su hajiya yakurah suka iso aranar kuka yadawo sabo ganin halinda 'yarsu dasuke 'dokin gani take ciki...
Ko alhaji babaye dake dattijo saida ya zubarda hawayen baqin ciki da farin ciki.
Akwance take itama amma hawayene keta bin gefen fuskarta suna zuba Wanda hakan yaqara bawa kowa tausayi.
Duk da akwai Carolina sosai suhailat ke wahala sbd lalurar rumanah din.
Kusan satinsu alhaji babaye biyu kafin shi ya koma yabar haj yakurah dataqi dawowa tana jiran isowar mijinta dazasu tafi tareda rumanah sbd gwada nasu na addinin.
Satin alhaji babaye daya da