Showing 33001 words to 36000 words out of 83480 words
tayi ne yasa jalal yaji wani iri har cikin zuciyarsa,wato ita baiwar su ce duk inda suka ajiyeta a nan zata zauna..
Juwairiya jin yayi shiru...
sai ta dan sace kallon sa da gefen idonta..
Wai me yasa yarima ya fiya kyau ne haka?taji zuciyarta na tambayar ta..
Jitai yace..
"Ki shiga dakina gobe ki gyara min shi"(hakanan ya tsinci kansa da fadin hakan,dan zuciyarsa na mutukar kwadayin ganinta a kullum)
Kafin ta bashi amsa ya juya ya fara tafiya..
Da sauri tabi shi tasha gabansa tana fadin..
Ranka shi dade ba nan bane wajen aikina..,bazan iya samun shiga na gyara maka dakin ba..kayi hakuri..
Yarima ya daure fuska..
Umarni ne nake baki a matsayina na sarkin ki.. dan haka bana son wani dogon zance..
Juwairiya ta samu kanta da langwabe masa kai gefe,sannan tayi kasa da kanta tace toh ranka shi dade..
Jalal yayi murmushi kafin yace "wuce muje..
Ta kalleshi da mamaki,ina zamuje?
Yace ina zaki je da?
Tace rumfar bayi zan koma ai..
Yace toh muje...
Tace,A tare zamu?ta waro ido..
Ka bari kawai zan tafi da kaina..
Jalal bai tanka ma ta ba ya shige gaba ya fara tafiya..
Juwairiya da sauri tabi bayansa dan kuwa tasan bazata iya komawa ita kadai din ba a wanannan dare ga kuma duhu..
"Yana gaba tana biye da shi a baya..
Gani nayi juwairiya sai faman sakin murmushi takeyi tana kallon yarda yarima ke tafiyarsa cikin kasaita da yanga kamar ba namiji ba..duk takun da zayyi cikin nutsuwa yakeyin sa..
Ta shafa gefen fuskarta cike da nishadi..
ooh Allah me nasa ikon..wai yau kamar ta baiwa diyar bayi. SARKI da kansa yakeyi wa rakiya a cikin dare..
Dadi ne fal a cikin zuciyarta, sai shakar kamshin da yake bazawa a hanyar takeyi.
"Shima din jalal murmushi yakeyi yana mamakin kansa,wani irin nishadi ke dawainiya dashi,ya rasa dalilin da zuciyarsa ke mutukar son kadaicewa wannan yarinyar..
Tafiya yakeyi kamar baya so..
Dan dama ba wani son suyi saurin yakeyi ba.
baya kaunar su iso rumfar bayi da wuri..
Tsayawa yayi ya juyo dan ganin ko yayi mata nisa...(cike da kulawa kamar yarda ko wane gentleman zayyi." kun de gane😉)
"Juwairiya kam tayi nisa sosai a cikin nata duniyar..
dan ko kadan bata ma lura da tsayawar da yayi ba...sai ji tayi taci karo da wani mutum..bum!
A tsorace ta dawo hankalinta..
sannan taja baya da karfinta..zanin jikinta ne ya ta'diye ta..ta tafi zata fadi..
Yarima yayi saurin saka hannayensa ya taro ta..
Sauke lumfashi kawai takeyi dan ya shammace ta...
"Kurawa juna ido sukayi na wani lkcn me tsawo.. kafin ya gyara mata tsayuwarta yace..
Tunanin me kikeyi haka?
Juwairiya ta samu kanta da fadin..
"Tunanin ka"!
Waro ido tayi da sauri jin abunda bakinta ya furta..ta zube kasa a mutukar kunyace..
Jalal kuwa samun kansa yayi da jin dadin furucin ta"tunanin ka"ya lumshe ido...
Juwairiya ta shiga bugun bakinta..
Kafin tace,kayi hkr ranka shi dade subutar baki ne nayi tunanin kaina nakeyi..me yasa ma zanyi tunanin mai martaba ai ban kai wannan matsayin ba..
Yarima ya bude ido yana kunshe dariyar sa..dan ya fahimci kunya taji..
Mike!
Ya fada a daken sa..
Ta mike tsaye ta kasa ko kallonsa..
Muje....
Ya fada yana ci gaba da tafiya..
Har suka kawo kusa da rumfar bayi juwairiya bata daina jin haushin kanta ba..
Ya tsaya yana juyowa gabanta..
Ki shiga..
Ta gyada kai..
Har ta fara tafiya ta sake dawowa da saurinta..
Nagode kwarai da gaske ranka shi dade..
Ya jinjina kai kawai bai ce komai ba.
sannan ya juya ya fice...
Juwairiya ta dafe kirjinta sannan ta juya dan shigewa cikin rumfar bayi sai murmushi takeyi..
caraf sai hango umayma tayi a tsaye bakin kofar tana kare mata kallo..
Gabanta ne ya fadi..
Kada dai umayma taga mai martaba yanzun nan?
Umayma ta kura mata ido cike da tuhuma.
fitowar ta kenan jin su hansai na jajen rashin dawowar juwairiya da wuri..
Waye wancan daya rako ta?umaymata tambayi kanta dan bayansa kawai ta iya hangowa sbd duhun wajen...,lallai kuwa akwai abunda wannan yarinyar ke boyewa..dole sai ta shiga jikinta sosai dan ta gano miye sirrinta..
Da sauri ta kamo hannun juwairiya,kin dawo?dama neman ki zan fita yanzu wlh.. naji ne su laure nata cigiyarki ganin abokan aikin ki sun dade da dawowa babu ke..
Juwairiya tayi murmushin yake,ai a baya suka baro ni ne..
Umayma tace Allah sarki muje ciki toh..
Juwairiya ta gyada kai suka shige ciki a tare..
************
Washe gari...
Gimbiya kilishi ce tayi kiran surukan nata..
Ta kallesu duka daya bayan daya kafin tace..
Ina fatan ku duka kun samu labarin yarda al'adar masarautar mu take...
Idan har aka na'da sabon sarki toh dole ne idan ya cika sati na biyu a mulkinsa matansa ne da kansu zasu shiga madafa suyi masa girki...
Khadija tadan murmusa dan dama ita jiran wannan ranar kawai takeyi,dan ta burge jalal ta samu yabawar sa..
surayya kuwa uwar son jiki cewa tai...
Umma amma dai na yau din kadai ne ko?
Kilishi ta gyada kai,yau da gobe ne tunda matansa biyu..
dan haka dolene ku raba rana kun yarda yayi muku.
wacece zatayi yau sannan wacece zatayi gobe..?
Khadija tayi saurin fadin,ai umma tunda surayya ce babba ita ya kamata tayi yau din ni sai nayi gobe ko?
Kilishi tace hakan ma yayi,ta maida kallonta kan surayya, kije ki shirya zan hadaki da du'bu dake Rumfar bayi..
Surayya tayi saurin yatsine fuska,umma a cikin RUMFAR BAYI zamuje yin girkin?
Kilishi girgirza kai tace,ai jinin sarauta baya shiga rumfar bayi..kanskanci a garemu hada jiki da bayin mu..
akwai madafa a can sabon bangare.. dan haka a can ne zakuyi girkin naku,sai ki zaba bayin da zasu taimaka miki..
Surayya ta gyada kai sannan ta mike cike da haushin wannan banzar al'adar ta fita..
***************
"Da safe"
"Koda juwairiya ta shigo sashen sarki,sai ta samu kanta da rasa taya zata shiga dakin na jalal.
taji dai ance tun asubahi surayya tabar sashen..
Jakadiya ce tayi kiranta,da sauri ta karasa wajenta..
Kallonta tayi tana wani nazari kafin tace,ki shiga dakin mai martaba ki gyara masa..
Juwairiya tace ni?
Jakadiya tace kwarai ke juwairiya .
Ta gyada kai kafin tace,toh inna..
"Sannan ta nufi hanyar dakin..
jakadiya kuwa tabi ta da kallo tana mamakin yarda jalal yasan har sunan juwairiya kuma ya bukaci data tura masa ita gyaran dakinsa,Allah dai yasa ba abunda take zargi bane..
*************
Tana shiga dakin ta ware ido ganin irin girmansa ga furnitures masu shegen kyau da tsada,dakin ya tsaru iya tsaruwa..
Motsin dataji ne a cikin toilet ya tabbatar mata da cewa yarima yana ciki..
gyara daurin zanin ta tayi sannan ta sa'bi tsintsiyar dake hannunta ta shiga gyaran dakin cikin kwarewa..
Ba karamin mamakin dadewar yarima acikin toilet tayi ba,sai kace wani mace?
Tana goge goge ne taji fitowar shi daga cikin ban dakin..
Kamshin sabulun wankansa ne ya daki hancinta..
Ta juyo dan gaisar dashi..
Sai ganin sa tayi daga shi se wani dan towel ya daura a kugunsa..
Tayi kasa da kai da saurinta..
Tace barka da safiya mai martaba..
Ya kura mata ido..
Sannan ya shiga tafiya wajen da kayansa suke yana fadin..
"Na lura baki dauki mgn ta da mahimmanci ba ko?
juwairiya tace,kayi hkr ranka shi dade..
Yayi shiru ya shiga shirinsa..
juwairiya ta juya dan ficewa ta basa waje..
Jitai yace...
"Ki zauna ki jirani"
Batayi gardama ba Ta samu waje ta zauna kasa..
Da gefen ido take kallon yarda yake shiryawar sa cikin nutsuwa da kasaita,ya shafa turare sun kai shidda (tadan matse baki,shiyasa yake kamshi abunsa)..
Sai daya gama shirinsa tsaf sannan ya dawo ya zauna a gefen gado yace..
Ina son anjima da daddare ki same ni a can wajen da muka hadu jiya..
Juwairiya ta gyada kai..
Jakadiya ce ta rangwada sallama..
Juwairiya jiki na rawa ta mike ta koma bakin kofa ta tsaya.
Jakadiya ta shigo tadan kalleta tace, idan kin gama kije umayma na neman ki a waje..
Juwairiya ta gyada kai ta fita..
Jakadiya ta karasa wajen jalal tana fadin..
AMALE bango madafar bayi,dama yanzu ne gimbiya kilishi ta aiko da sako a fada maka..
Jalal ya jinjina kai irin inajin ki..
Jakadiya tace,idan ranka shi dade bai manta ba a al'adar masarautar nan duk cikon sati biyu na sabon sarki matansa ne da kansu zasu fito suyi masa girki..
Dan haka ne yau sarauniya surayya zata shiga madafa da kanta ta girka maka abinci na gani na fada.
gimbiya kilishi tace a sanar dakai kada kaci komai har lkcn da za'a gabatar maka da abincin..
Jalal ya gyada kai yace,naji jakadiya, magajin ya iso ne?
Jakadiya tace,ya iso ranka shi dade yana can a falo yana jiran fitowarka..
************
"Juwairiya na fitowa daga cikin dakin yarima ta tarar da magaji zaune a falon..
Ta duka har kasa ta gaishe dashi..
Magaji a sake ya amsa mata,harta mike zata fita yace..
Bakiji ba..
Ta dawo tace na'am..
Ya kurawa fuskarta ido..
Kafin yace,Ina tunanin kamar na san fuskar nan taki shekaru da suka wuce..
Juwairiya se a lkcn itama ta dago tana kallonsa sosai..
Kallon juna sukayi kafin a tare suka nuna junansu suna fadin..
MANGORO ko??????...
Murmushi sukayi wa juna..
Magaji yace,haba ko da ince ni na san nasan wannan fuskar ashe ke din ce..
Juwairiya tace,ai kuwa dai ni ce kaga ko ranar ban samu damar yi maka godiya ba..
Magaji yayi dariya ah ah ai ya wuce shekaru dayawa,kinsan kuwa tunda ga ranar ban sake ganinki acikin masarautar nan ba ,har nemanki nayi.
Juwairiya tace,Allah sarki ai lkcn ne na fara aiki a sashen zainaba shi ya sa.
Yana shirin mgn sai ga jakadiya tare da yarima sun fito..
Jalal idonsa akan juwairiya,ganin murmushi akan fuskar ta yasa shi kallon magaji...
Shima din yaga murmushi akan leben sa...
Daure fuska yayi yace..
Magaji muje ko?
Magaji yace mai martaba sai yanzu aka samu fitowar?
Yarima yayi banza da shi..dan yasan halin magaji da zolaya..
Jakadiya ta kalli juwairiya, ke baki je neman da ake mikin bane?
Juwairiya tayi saurin guduwa tabar wajen..
Jalal yayi gaba shima..
Magaji yayi saurin binsa a baya yana fadin..
Takawarka lafiya darzaza amalen sarakuna....
************
"Har suka shiga fada jalal bai kalli inda magaji yake ba..
Magaji kuwa zancen nata cinsa a rai..
Kasa hakuri yayi Yace,wai ka san kuwa mai martaba yarinyar nan itace dai wacce na taba gani shekarun baya..
Se lkcn jalal ya kallo shi..
Wace yarinyar?
Magaji ya washe baki..
Wannan me konannar fuskar mana da mukaje da ita chadi..
Nayi mamaki sosai ma da ta gane ni itama wlh..
Yarima ya tabe baki..yaci gaba da aikin gabansa.
***************
"Zainaba ta kalli zabba'u,tashi muje sashen khadija..
Zabba'u tace toh ranki ya dade..
"Sun shiga sashen suka tarar da goggon khadija tazo..
Zainaba ta gaishe ta sannan ta dawo falo ta zauna tana jiran khadija ta sallame goggon nata..
"Goggo ta kalli khadija,ina fata kin gane bayanin da nayi miki ko?
Khadija ta murmusa na fahimci duk bayanin ki goggo,kada ki damu zan samu wacce na yarda da ita ta shiga cikin bayin da zasu tayata girkin sai tayi yarda kika fada din..
Goggo tace yauwa nizan koma..
"Sun fito falo zainaba ta kalli khadija dake ta washe baki..
Yadai ko goggo tazo miki da wani albishir din ne?
muje zuwa👇
TEAM RUMFAR BAYI
[9/18, 3:22 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction )
Na Afrah bhai
Page 23
Wattpad @afreey101
_"@ Ayshat maghili,Admin TEAM RUMFAR BAYI group thanks for the effort love😚"_
*****************
"Khadija ta saki murmushi, ai abunda ma yafi albishir tazo min dashi..
Zainaba ta gyara zamanta,Allah ko?sannu yar lelen goggonta..
Khadija ta kwashe da dariya..
Kafin tace,wai ina Mustapha ne?kinsan dai da an gama mgnr bikin su ya turaki da hamza kanki za'a dawo ko?
Zainaba ta lumfasa,nima damuwata kenan wlh,kuma gashi kinsan halin abba da shegen son auren hadin nan daya burgeni ko kadan..
Khadija ta dan zungureta,ni ai auren hadin ba karamin taimaka min yayi ba,ke kinsan in ba dan shi ba ai bazan taba samun ya jalal dina ba..
Zainaba tace ke kenan,ni kin ganni nan ma kadaici duk ya ishe ni a cikin yan kwanankin nan, tun dauke min juwairiya da mijin ki yayi..
Khadija ta tabe baki..
Kema dai zainaba da rigima kike, kawai ki bari sai lkcn auren ki yayi sai ki zabe ta a matsayin kyautar ki daga wajen mai martaba..
Zainaba ta sa dariya,wlh kin kawo shawara kawata..
Suka saka dariya a tare..
***************
"Umayma da kanta takai juwairiya har wajen surayya. .
Surayya ta kalle ta cike da kyamata tace..
Ki shirya zamu shiga madafa dake yanzu..
Juwairiya tadanyi mamaki amma ta share tace toh ranki ya dade ..
"Tunda suka shiga madafar suka soma aiki ba kama hannu yaro..
Surayya kam na hakimce akan kujera tana basu orders cike da isa..
Har sun kusa kammala aikin juwairiya dake gefe ta jinjina kai ganin irin delicacies din da aka shiryawa yarima..
tana mamakin yarda mutum daya zai iya cinye duk wadannan abincin..
Abinci har kusan kala goma sha biyar?ina zai kaisu?
Aiko duk tsokali daya yayi a duka se cikinsa ya koshi..
Tadan tabe baki,ko dayake duk bajinta ce ake son a yi masa..
Juyowar da zatayi kawai ta hango wata baiwa na barbada wani gari acikin tukunyar miya..
Da sauri ta karasa wajenta..
Baiwar tayi saurin kakkabe hannunta tana kallon juwairiya da kananun idanunta tace,lafiya?
Juwairiya tace,me kika zuba acikin tukunyar nan yanzun nan?
Baiwar ta watsa mata harara tace,zargi kikeyi?toh babu abunda na zuba sai gishiri..tana gama fadin haka tayi gaba da sauri..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Meye ta zuba a abincin yarima?ta tambayi kanta..
Hankalinta ne yadan tashi dan ita kam bazata so a cuci yarima ba...
Umayma ce tazo tayi kiranta akan surayya tace su fara kai abincin can babban falon jalal..
****************
Rabi ce ta shigo sashen khadija da gudun ta..
A daki ta tarar da khadija a zaune gefen gado..
Ta samu waje a kasa ta zauna tana lankwashe kafafunta tace..
Albishirinki ranki ya dade?
Khadija ta saki murmushi bani in sha..
Rabi tace yanzun nan muka gama da mgn da wannan baiwar da muka saka aiki acikin bayin gimbiya surayya..
Kuma Ta tabbatar da min cewa tayi yarda muka bukaci tayi...
Khadija ta kwashe da dariya cike da murna sosai..
Tace naji dadin albishir din nan sosai..
Dan Babu wacce zata samu yabawar jalal sai ni ni kadai kuma...
Su uwar gida manya,dole ne asha kunya da wulakanci ayau..
Ta kalli rabi,Allah yasa dai ta zuba dan'tsamin nan dayawa acikin abincin dan bana so ko kadan girkin wannan matar yakai cikin cikin ya jalal dina..
Rabi tace kada ki damu ranki ya dade na tabbata tayi komai kamar yarda muka tsara..
***************
"Su juwairiya sun gama jidar abincin zuwa sashen jalal..
An gana gyara falon tsab kamar za'ayi wata uwar liyafa..
Kuyangi biyu akabari sai surayya data sha wata uwar kwalliya tana zaune gefe tana jiran fitowar yarima..
Kallon su juwairiya tayi,tace duk zaku iya tafiya..
A sanyaye juwairiya ta fito tunani duk ya cika zuciyarta..
Ta kasa yarda gishiri ne wannan baiwar ta saka a cikin abincin yarima,kodai wanine ke son halakar da shi?toh amma waye zai so cutar da sarki?
Da wadan nan tunane tunane ta isa rumfar bayi..
********
Sai da jalal ya gama shirin sa tsab acikin kayansa masu tsada sannan ya fito falon..
Surayya ta mike cike da kissa tace..
Sannu da fitowa sarkina..
Yarima ya jinjina kai yana shirin zama ..
Surayya tace,na tabbata zaka yabawa kokarina..
Yarima ya kalli jerin abincinan dake gabansa..
Lallai kinsa aiki,duk wannan abincin ina zan kai su?
Surayya tace,haka zakace ma kenan ki?
Jalal ya murmusa bai ce komai ba..
Surayya ta banka wa kuyangin harara,ku zuba masa mana kuka tsaya kallon mu..
jiki na rawa sukayi serving din yarima first dish,wanda ya kun'shi (farar shinkafa me kayan lambu da miyar tsokar shanu,sai dafaffen kwai a gefe),
Jalal ya dauki tsokali cike da yanga ya tsakuri abincin yakai bakinsa..
yamutse fuska yayi yana Matse baki jin wani irin mugun tsami ya gauraye masa baki..
Da sauri Ya kalli surayya a fusace..
Miye wannan?harshena kike shirin cirewa..!ko kashe ni kike son yi?
Surayya taji gabanta ya fadi tace a rikice me kike nufi jalal?
Yasa hannu ya ture plate din daga gabansa... ya tura mata shi yace..
Dandana kiji ma kanki mana!wannan ai muguntar banza ce..
Surayya hannu na rawa ta dauki tsokali ta soma dandana abincin..
Da sauri ta zubar dana bakinta..tace..na shiga uku!
Meye haka?wallahi ba haka abincina yake ba..ta fadi kamar zata rusa kuka..
Jalal yaja tsaki hade da mikewa cike da haushi ya fice daga sashen abunsa..
************
"Juwairiya gaba daya ta kasa tsaye ta kasa tzaune,tunanin halin da yarima yake ciki kawai takeyi,ta kagu duhu ya fara taje ta same sa a inda yace su hadu..
laure ce ta kawo mata kwanon abincinta da bataci ba.
kewai ban gane miki ba?tunda kika dawo kike a nan zaune kin buga uban tagumi sai kace wacce ta ka'yar da uwar miji..lafiya ?
Juwairiya ta girgirza kai tace,babu komai goggo laure amma ni na koshi da wannan abincin ki koma dashi..
Laure ta ajiye kwanon hannunta,nasan dai bakici komai ba dan haka ki ajiye zuwa anjima idan kin gama muraja'ar,tana gama fadar haka ta fice..
Juwairiya ta mike itama tana kallon jikinta,a haka zataje wajen yariman?taji zuciyarta ta fada ..
Wasu kayanta masu dan haske ta canza sannan ta lallaba tayi waje da gudu..
**************
"Tunda ta fito Gaba daya tunani takeyi,Allah dai yasa babu wani abunda ya faru da shi..
Tana isa wajen ta samu wani dutse ta zaune akai tana buga uban tagumi..
Daga kai tayi ta kalli sama,garin yayi duhu amma hasken taurari ya kayatar da daren..
Ta dade a wajen zaune,zuciyarta na gargadinta ko dai yarima bazai samu zuwa bane?wata kilan ma ya manta da haduwar tasu a nan..
Ta mike a sanyaye, dama mai take tunani wacece ita da yarima zai zo ya same ta,wata zuciyar tace mata,toh ai shine ya bukaci ku hadun?
Mtsww....(whatever )
***************
"Koda ya fito daga sashen sa da hamza sukaci karo a hanya..
Hamza ya bishi da kallon tuhuma yace..
Yaya sai ina ne haka da daren nan?gashi babu wani bafade a tare dakai..
Jalal yadan dafa kafadarsa,hamza kenan kasan fa ko sarki yana son sirri..shiyasa ban gayyaci kowa a fitar tawa ba..
hamza ya mishi kallon rashin fahimta..
Jalal ya murmusa..
Hamza..ya kwashe da dariya yana cewa ooooh sai yanzu na gane ai yaya,amma kasan dai duk inda zaka wuce a masarautar nan indai a haka kake... (ya nuna shigar alfarmar dake jikin yarima) to dole ne mutane su shaida ka.. kaga ba wani batun sirri kenan...
Jalal ya jinjina kai ganin lkcn da dan sauran haske ko ina zai wuce sai an lura dashi..
Hamza yace,kana son taimako na?
Jalal yace,wane irin taimako zakayi min kanina?
Hamza yace duk da bansan ina ne wajen sirrin naka ba amma ina tunanin da ka batar da kama zai fi..
Jalal yadan kwabe fuska,ni da masarauta ta ina matsayin sarki sai na batar kamanni na dan na samu sirri..
Hamza