Showing 51001 words to 54000 words out of 83480 words
uban tagumi suna tauyawa kawar tasu..
juwairiya har cikin zuciyarta batayi nadamar rashin fadin sunan jalal da batayi ba..
Oh ! ko yana ina yanzu?a wane hali yake ciki?ta tabbata hankalinsa a tashe yake...
Jakadiya ce ta shigo da wata me magani a bayanta da yarima ya sakata taje ta dauko ta..
Me maganin ta hau duba juwairiya..cike tausayawa.
**********
"Samira ta kurawa turaki ido ganin yarda yake ta faman sauke ajiyar zuciya..
ba karamin fada yasha a wajen fulani ba wai yana son ya zubar mata da mutumci ya juyawa yan uwansa baya akan mace.
ita ba wai yantar da juwairiyar da yayi bane damuwarta,ah ah furta Auren ta da yayi shine bacin ranta,duka duka jiya aka daura masa aure ko yan uwan matarsa basu gama watsewa ba yake so ya ballo musu ruwa...
Samira ta tausaya mishi sosai dama haka So yake?
Ta dawo gabansa ta tsugunna tace..
Turaki inaso na baka wata shawara idan bazaka damu ba..
Turaki ya dago yana binta da kallo..
Tace na tambaye ka?
Yayi shiru..
Samira taci gaba..
Ita baiwar da kake so din ka tabbata tana sonka ne?
Ko kuwa dai nuna mata iko da mulki zakayi ka aureta a cikin rashin damuwa da(feelings)dinta..
Turaki ya kura mata ido yana wani nazari,tabbas yasan juwairiya bata son sa,dan da tana son sa da zai gane tuni..,yasan dai ta dauke sa a matsayin yayanta ne amma baya tsanmanin tana SON SA...
Samira ta jinjina kai,yanayin ka ya tabbatar min da cewa ba sonka takeyi ba...
Ta riko hannunsa..
Idan zan fada maka cewa kaima ba sonta kakeyi ba zaka yarda da ni?
Turaki ya girgiza kai..yace..
Sonta nakeyi samira ba zaki taba ganewa ba..
yarinyar nan tun tana yar karamar ta take aikin bauta a rayuwarta,bata san wani jin dadin yarinta ba da kowane yaro yake samu..
bata da wani yanci ko zabi a rayuwarta,haka ta taso a cikin RUMFAR BAYI babu wani digon farin ciki a rayuwarta..
Dan haka idan auren tane kawai zai sa na fitar da ita daga wannan rayuwar da take ciki toh zan iya sabawa da duk yan uwana dan nayi hakan..
Samira tayi murmushi lallai Allah yayiwa turaki zuciya me kyau..
Tace,TAUSAYINTA kawai kakeyi turaki..
Dan haka a shawara ta indai har kana son kagan ta acikin farin ciki toh lallai ne ka YAN'TAR da ita kawai daga bauta amma kada kayi kuskuren danne mata hakki kace zaka aure ta...
Tana gama fadar haka ta mike ta fice...
Turaki ya shiga nazarin mgnr samira..
*********
Jalal na kwance a kan gadonsa zazzabi ne sosai ya lullube sa...
Khadija ce ta shigo dakin..
Ganin halin da yake ciki ba karamin tsorata tayi ba..
Da sauri ta fita tayi sashen gimbiya kilishi dan ta sanar da ita..
Hankali a tashe gimbiya kilishi ta shigo sashen nasa..
Tausayi sosai ya bata,dan tasan ko da yana karamin sa baya son ko kadan mahaifinsa yayi masa fada akan gaskiyarsa...lallai dole ta koyawa surayya hankali,dan duk sbd ita ne haka ya faru..
Me magani aka kira ya shiga duba sa..
Khadija na gefe tana masa sannu..
*******
Mutanen ku kuwa su umayma...
Wani kauye sukaje can kusa da SANDAMU a nan suka samu wani malamin tsabbu..
Surayya ta fayyace masa komai..
Dariya yayi ya buga kasa yace..
Ni ban ga wani aure a tsakanin wannan baiwar da kanin mijin naki ba...
Sai dai kuwa naga wani haske a tattare da yarinyar..
Surayya taja tsaki..ya wuce na yan'cin da take shirin samu gobe..
Malamin yace yanzu me kike so ayi miki?
Surayya tace,so nakeyi kawai gobe idan an gama yan'tar da ita tayi gaba... tabar masarautar mu,dan bana son ta kara waiwayar kasar daura .....
Umayma ta jinjina kai lallai surayya ta cika shu'umar mace..
Malam ya buga kasa ya kallesu..
Kamar anyi an gama ne ranki ya dade..
Surayya tayi murmushin murna sannan ta basa kyauta me tarin yawa suka fice...
**************
Washe gari...
Sosai ne juwairiya taji sauki se de kafafunta da kyal take iya tafiya..
Fadawa ne suka shigo har cikin rumfar bayi sukace ana neman ta a can fa'da..
Hansai da laure ne suka shiryata tsab dan lbr har ya gama bazuwa,kan ZA'A YAN'TAR DA JUWAIRIYA...
Murna sosai bayi suka shiga yi,lallai Allah yana son juwairiya da alkairi daga ruwa rumfar hukunta bayi sai barin BAUTA daga daya...
A fada kam,jalal ne a kan (throne ) dinsa ga sauran royal family duk an hallara kowa ya samu waje ya zauna..
Surayya ma kanta dadi takeji dan tasan abunda ta kulla har wani kagara take ayi ayi a yantar da juwairiyar ta bace daga rayuwar su..
"Juwairiya kuwa na saka kafa acikin Fa'dar idanuwanta suka kai kan jalal dake hakimce fuskarsa babu yabo babu fallasa..dan sosai yake jin dadin yantar da ita da za'ayi..
Ahankali ya dago da kwayar idonsa ya sauke su akan ta yana aika mata da wasu sakwannin masu wuyar fassarawa.
Gaba dayansu zuciyoyin su sun dan karaya balle ma shi jalal din da yake ganin kamar(plan)dinsa bazai yi masa wani amfani ba.......
Toh readers menene PLAN din JALAL?
Not edited
Team RUMFAR BAYI
*RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 31
Wattpad @afreey101
*****************
"A gaban dun'bin jama'a waziri ya Yan'tar da baiwa juwairiya kamar yarda al'adar masarautar tasu take..
"Wani irin lumfashi me nauyi ta sauke....
farin ciki sosai ya ziyarci zuciyarta bata taba jin irin wannan yanayin ba a duk rayuwarta..
Jalal kansa sai da yaji wani irin sanyi acikin zuciyarsa,yau kam zai zama tahiri babba a wajensu,daga inda yake yana kallon yarda juwairiya ke ta sakin murmushi hakan ba karamin dadi yayi masa ba..
Hansai da sauran bayi ne suka shiga congratulating din juwairiya cike da murna su,suna ji dama ace sune aka yantar,dan a wajensu idan aka yantar da baiwa kamar an sake haihuwar ta zata fara sabowar rayuwa me cike da yanci da farin ciki.
Addu'a akayi taro ya watse...
"Jalal na fitowa daga fa'da ya koma sashen sa ya saka jakadiya ta turo masa juwairiya can bayan sashensa su hadu yana da mgn mahimmiya da yake yayi mata..
Jakadiya ta jinjinar dakai tana tuna lkcn da suka sanar mata taimakon da turaki yayi mata da kuma furucin da yayi na sonta,ko yanayin fuskarta se da jakadiya ta fahimci juwairiya bata son turaki,jalal ne a zuciyarta..
"Zainaba ba karamin murna tayi ba ta makakkale juwairiya a jikinta,tana jin dadin yarda zata iya hada jikinta da ita a yanzu..
samira ce ta karaso wajensu tare da khaleed dan uwanta, dukkanin su mamakin kamanni ta sukeyi da Ammi har lkcn.
samira tace,na taya ki murna sosai..
Juwairiya ta murmusa cike da farin ciki tace nagode kwarai..
Khaleed ya kura mata ido yana tunanin zancen su da sarki jalal yau da asuba Allah yasa yarinyar ta amince..
Wani bawa ne yazo wajen yayi kiran samira,tayi musu sallama ta kama gabanta..
"A daki samira ta tarar da turaki a zaune..
Ta karasa wajensa tace..
Gani ance min kana kirana..
Ya dago ya kalleta..kafin yace..
Nayi tunani akan maganar ki ta jiya..
Surayya tace, kuma me ka yanke hukunci akai..zaka tilasta mata auranka ne,ko kuwa ?
Turaki yace bazan taba yiwa juwairiya dole ba..dan haka bashi ne niyya ta ba..
Samira ta saki murmushi tace,naji dadin yarda ka zauna kayi tunani me kyau haka ,
yantar da ita da kayi ma ya isa ka taimaka mata sosai..
sai dai fa ni wlh wannan juwairiyar tana min kama da AMMI sosai..
Turaki ya gyara zama..
Me kike nufi?wacece kuma Ammi?
Samira tadan muskuta..
Ammi amaryar mai martaba ce wato kakana..
Turaki ya girgiza kai,babu alakar da zata hada Juwairiya da ita gsky dan kuwa iyayen juwairiya a cikin masarautar nan suka haife ta kuma naji lbrn yan asalin kasar daura ne..
Samira ta jinjina kai hakane nima nayi wannan tunanin...
*******
"Jakadiya ce ta samu juwairiya ta sanar mata da sakon jalal..
Kallon jakadiya tayi a dan tsorace..dan bata zaci tasan me ke tsakanin ta da yarima ba..
Jakadiya tajawo ta zuwa gefe tace..
Kada ki damu juwairiya ina bayanku keda AMALE..yanzu kije yana kiran ki..
Juwairiya na daga kafarta taji wani irin faduwar gaba,muryoyi ta shiga ji a kunnen ta kamar ana kwala mata kira..
Waige waige ta shiga yi..
Fuskokin su laure,hansai,rabi,zabba'u, zainaba kawai take kallo dake wajen tana jin wani irin abu yana tokare mata wuya..
Gaba daya jikinta ya hau rawa..
Jakadiya tace,kije mana kinsan ba'a barin Amale jira..
juwairiya ta gyada kai,tana tafiya ne kawai amma gaba daya zuciyarta a dakule take..ji takeyi gaba daya gangar jikinta bata kaunar zama acikin masarautar..
"Jalal kuwa na zaune akan wani dan dakali yana ta faman zuba ido..
Duk ya rame sbd tunanin da saka a gaba yanayi duk lkcn da yake shi daya..
Yanzu dai addu'ar shi daya ce Allah yasa ta amince da (plan)dinsa...
Hango ta yayi ta taho amma hankalinta kamar baya jikinta...
Da sauri ya mike ya karasa wajenta..
Tana ganinsa ta lumshe ido tana dafe kirjinta,wani dan sanyi sanyi a cikin ranta ganin fuskarsa...
Jalal ya kamo hannunta..
Ya jikin ki?ina fatan kin samu lafiya..
Juwairiya ta kura masa ido kawai ta kasa furta komai..
Jalal yace,ki yafe min ....
nasan duk nine silar shigan ki cikin wannan halin..
Juwairiya gaba daya ji takeyi lumfashin da take sha'ga yana dauke wa..
Jalal gani yayi ta fada jikinsa babu shiri..
A rikice yace..
Me ya faru?
Baki ji dadin yantar dake da a akayi bane?na dauka ai yau ranar farin cikin ki ne..
Juwairiya ta girgiza masa kai..
Idanuwanta na fitar da kwalla ta dago daga jikinsa tana kallon kwayar idonsa tace..
'Ka taimaka min ranka shi dade..
Jalal cikin murya me sanyi yace..
Bakya son auren turaki ne?
juwairiya ta kallesa da mamaki kafin ta girgiza kai..
Jalal ya ce toh taimakon me kike so nayi miki?
(A zuciyarsa kuwa yana addu'a yake Allah yasa idan ya bukaci ta gudu daga masarautarsu tabi khaleed kasar zazzau ta yarda...yarda zai samu ya yi shirinsa sosai,dan bazai taba bari ta zauna a nan ba turaki ya aure masa ita,dolene ya samar ma kansa mafita)
Ji yai tace..
Ka taimakeni yarima,ina ji a cikin zuciyarta ko sakwon daya nayi a cikin wannan masarautar toh zan iya rasa rayuwata...
Waro ido jalal yayi cikin al'azabi..me hakan yake nufi?me ya same ta dare daya?daga samun yancin ta?
Yanayin ta kawai yake kallo,shes not normal..akwai wani abu a kasa dan har kwayar idonta juyawa takeyi tana birkicewa..
Ya sa hannu ya share mata hawayen dake fuskarta..dan tausaya mata sosai,dole akwai abunda akayi mata,dolensa ya kare ta daga sharrikan GIDAN SARAUTA..
kwantar da murya yayi yace..
Naji ki kwantar da hankalinki nima nayi wannan tunanin..(yayi using opportunity din)
Zan hadaki da khaleed dan uwan matar turakine ku tafi can kasar zazzau sai ki zauna a wajen kafin na gama shirin da nake na waiwaye ki..
Juwairiya ta damke hannunsa cikin nata..
Kayi min al'kawarin zaka neme ni koman dadewa..ni kuma nayi maka alkawarin jiranka har lkcn da zaka zo min da amsa ta..
Jalal ya janyo ta jikinsa yana cikin wani irin tausayinta a cikin zuciyarsa..
Na miki alkawari JUWAIRIYAR..na miki alkawarin nemo ki a duk inda kike,zan zo miki da sakon zuciyarta..
Taja lumfashi kafin tace nagode sosai AMALE...duk suka sauke ajiyar zuciya..
*******
"Kamar yarda suka tsara da shi da khaleed..
zai saka shamaki ya fitar da ita ta kofar baya sai su hade a can da tawagar du khaleed su wuce zazzau da ita...
"Juwairiya ta shiga rumfar bayi da gudu ta shige dakinsu tana rusar kuka..
Hansai na ciki tare da laure suna ta faman murna basu san meke faruwa ba..
Kallonsu tayi..
Kafin ta fada jikinsu ta saka wani kukan...
Hankali a tashe suka shiga tambayar ta ko lfy?
Juwairiya ta dafe kirjinta..tace
Umma bazan iya ba..bazan iya ba umma,zuciyarta jinta nake kamar zata tsage ya zanyi umma?
A rikice laure tace..
Meke damunki haka juwairiya?
Juwairiya ta fashe da kuka..
Umma zan bar RUMFAR BAYI zan bar masarautar daura, idan ba haka ba ji nake umma kamar zuciyata zata iya fashewa.. ji nake na tsani duk wani lumfashi da zan shaka a wajen nan..
Hankalin su ba karamin tashi yayi ba..
Kuka suka sosai sukeyi dan a take suka fahimci sihiri ne a jikin juwairiya(kunsan mutanen da' da saurin canfin su)
GIDAN SARAUTA kenan! sunsha ganin ire iren wadannan matsalolin..
Jakadiya ce ta shigo cikin saurinta..
Itama kukan ta saka ganin su a haka ba karamin karaya zuciyarta tayi ba.
"ta shiga kwaso kayan juwairiya dan jalal yayi mata bayanin komai,ita kam a ganinta kila wani haske ne yazo musu dan bayyana wa juwairiya ASALINTA ... (dan har kamarsu da Ammi sun fada mata shi da khaleed kuma bata koye wa jalal komai ba ta fada mishi yarda suka sami juwairiya ,jalal ya girgirza sosai amma yasha alwashin indai yana raye sai ya nemo wa juwairiya ASALINTA)
Hansai ta kamo hannun jakadiya suka dan fita waje..
Jakadiya tace,kiyi hakuri hansa'u ni a ganina duk abun nan da ke faruwa alkhairi ne inshaAllahu a wajen juwairiya,kika sani ko wannan tafiyar tayi sanadiyyar saduwarta da yan uwanta na usuli?
Hansai na kuka shabe shabe tace,hakane jakadiya, amma ina zata nufa yanzu?wa take dashi?
Jakadiya tadan waiga ganin babu kowa a wajen sai ta fayyacewa hansai duk abunda ta sani a tsakanin jalal da juwairiya...
Hansai ta ware ido ta saki baki,ta kasa gasgata mgnr jakadiya, amma ko ba komai taji dadin taimakon da jalal zayyi wa juwairiya,gashi kuma Allah ya kawo wa juwairiya ranar da zatayi bankwana da BAUTA..
"Jakadiya,laure da hansai ne suka fito a asirce dan su fitar da juwairiya..
A kofar Rumfar bayi sukaci karo da shamaki yana jiransu..
Juwairiya ta juya tayiwa RUMFAR BAYI kallon bankwana,sannan ta kalli hansai tace..
Umma dan Allah ki bawa zainaba hakuri,kice mata nayi alkawarin aiko mata da wasika idan har na samu masauki me kyau..
Hansai tace,kada ki damu juwairiya zan isar mata da sakonki...
'Ta kofar baya suka fita,a inda suka tarar da motar khaleed tare da wasu maza kuda biyu..
Juwairiya na kuka shabe shabe tayi bankwana da iyayenta sannan tayi bankwana da MASARAUTAR DAURA....
********
"Gu'da kawai kake ji na tashi daga sashen gimbiya surayya,umayma ta kalleta cike da farin ciki..
Yanzun nan wani bawa yake sanar dani,yaga fitarsu juwairiya ta kofar baya kuma da alama ita akeyiwa rakiya...
Lallai aikin malamin nan kamar yankar wuka yake..
Surayya ta gyara zamanta..tana murmushin samun nasara...tace
Yanzu dai na kawar da wannan shegiwar yarinyar saura na mallake SARKI JALAL na haifa masa YARIMA me jiran kujerar mulki...
Duk suka kwashe da dariya..
************
"Tunda suka hau kan hanya juwairiya ke ta rusa kuka,sai dai ba karamin wasai takeji a cikin zuciyarta ba,ji take kamar an sauke mata wani katoton dutse daga kanta..
Khaleed ne ya lumfasa ya kalleta..
Ki daina kukan nan haka mana..
Juwairiya ta gyada masa kai ta shiga goge kwallarta..tana jin kewar yan uwanta da kuma AMALEN ta..
Khaleed ya kalli me tuka su yace,idan mun kai malumfashi sai mu tsaya a ci abinci..
Juwairiya ta buga tagumi tana tunanin irin rayuwar da take ciki...
Ooh!
Yanzu kuma komai rayuwa ta ajiye mata?
...daga aikin BAUTA zuwa samun YANCINTA yanzu kuma tana hanyar yin HAJIRA......
**********
"Ba su iso kasar zazzau ba sai cikin dare sosai...
Khaleed na ganin haka ya wuce da ita can bangarensa ya bata wani daki yace ta kwana a ciki zuwa gobe da safe...
"Juwairiya tayi masa godiya sannan ta shige cikin dakin da kullin kayanta..
Dakine karami amma ya tsaru sosai dan tunda take ma a rayuwarta bata taba kwana a cikin irin sa ba..
"Ta ajiye kayanta a gefe sannan ta mike ta shige kofar da take tunanin ta ban daki ce..
Alwala ta farayi tana kaiwa wajen wanke fuska ta shafo tabon dake fuskarta, tsaki taja tace,Allah ya kawo min lkcn da zan wanke wannan tabon karyar daga fuskata har abada..
Ta saka ruwa sosai ta wanke shi tas,se taji wani irin wasai a fuskar ta ta,alwalar ta dauro ta fito..
Tana shirin ta'yar da sallah taji an kwankwasa kofar dakin..
Tsoro ne ya dirar mata..
Muryar khaleed taji yana cewa ta bude shine..
Ta karasa ta bude masa kofar...
Wani irin faduwar gaba ne ya ziyarci khaleed..
Cikin mamaki ya nuna fuskarta..
Me ya samu fuskarki ina tabon yake?
Tayi murmushi tace..lbr ne me tsawo..
Khaleed ya jinjina kai,lallai akwai wani boyayyen al'amari a tattare da yarinyar nan,yaji dadin da jalal yayi wannan tunanin,tabbas akwai (link)a tsananin su da Ammi..
"Takardar dake hannunsa ya mika mata,ga wannan babu yawa dan nasan dare yayi da kyal mu samu abinci daga cikin gidan..
Juwairiya ta bude takardar,balangu me zafi ga kuma yaji a gefe da albasa sai baza kamshi yake..
Miyau ta hadiye tace nagode sosai..
Khaleed yace,babu damuwa se da safe..
juwairiya tace Allah ya kaimu lfy...
"Tana shiga dakin,tayi sallolinta sannan ta jawo takardar balangun ta,ta lashi lebenta na kasa,lallai kuwa Allah me iko wai yau itace da cin balangu irin wannan..
"Sai da Taci ta koshi tasha ruwa ta kwanta...
******
Washe gari da safe..
Bayan tayi sallar asuba ta sake komawa barci dan gaba daya jikinta a gajiye take..
Kwankwasa kofar khaleed ne ya farkar da ita daga mafarkin jalal da takeyi..
Ta mike da sauri tana mamakin kanta..
Lallai su juwairiya har an samu wuri,ta fadi tana ma kanta dariya..
Bude masa kofar tayi..
Khaleed yace,ki shirya zan shiga dake can cikin gidan..
juwairiya ta gyada kai sannan ta koma ciki tayi wankan ta ta sake kaya..
Lkcn da khaleed zai dawo har ta kammala komai..
Dan haka tafiya kawai sukayi....
Team RUMFAR BAYI
*RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 32
Wattpad @afreey101
_"Lovely fans of RUMFAR BAYI i appreciate your love for this story,your comments means alot to me,INA YINKU IRIN SOSAI DIN NAN"_
_#teamyarima #teamjuwairiya #teamJJ #teamJULAL #teamRumfarbayi_
*******************
"Tunda suka fito daga cikin bangaren na khaleed juwairiya ke ta kallon irin tsari da girman masarautar zazzau, tabbas tafi masarautar su nesa ba kusa ba..
"Tafiya sukeyi juwairiya na faman kallon yarda bayi take zurga'zurgar su ,a zuciyarta tace,oh duk dai in da bawa yake dan wahala ne shi..
Gani tayi duk inda suka wuce sai an tsugunna an gaishe da khaleed cike da girmamawa,shi kuma a amsa musu a sake,ta lura ko kadan baya da wani girman kai..
Wani bangare taga sun nufa,me girma da kyaun tsari,yasha sabon fanti..
Suna shiga cikin wani makeken falon ta ware ido tana kallon irin kwalliyar da falon yasha,gasu fan'teka da kwalla duk an yi jere dasu gwanin ban sha'awa..
Khaleed ya kalleta yace,ki zauna mana ya nuna mata waje a kasan darduma..
Wata baiwa ce ta fito daga wata kofa ta zube a gaban khaleed tana kwasar gaisuwa cike da girmamawa..
Ya jinjinar dakai kafin nan yace,marka ina uwar dakin naki take ne?ita na shigo na gani..
Marka dake ta kallon juwairiya tace,ai tana ciki ranka shi dade bari na sanar da ita ka shigo..ta juya ta koma kofar da ta