Showing 21001 words to 24000 words out of 83480 words

Chapter 8 - Rumfar Bayi Hausa Novel Complete

07 Jan 2025

974

zata tashi sama..
"Ina zataje?"
Ya fada acikin zuciyasa...

Magaji ne ya dafa sa ganin hankalin sa baya tare dashi..
Muje mana kasan fa yau inna ta hada abinci damu kuma tace dole na taho dakai,rannan haka kayi min wayo naje nasha fada na..
Yarima yayi murmushi dan kuwa yana jin dadin abincin innar sosai,kai fa ka cika korafi dayawa,ko ranar ma ai umma ce ta tsare ni a sashen ta,magaji yace,naji din muje dai kada muyi rana....
  
"Juwairiya har tayi musu nisa sai ji tayi kawai ta taka wani abu a kafarta..
da sauri ta dage kafar tana sakin ihun azabar da taji..
Waje ta samu ta zauna tana dago da kafar ta duba me ya tsake ta haka..
    Wata kwalba ce kuma ba kadan ba ta fasa mata kafar se jini ke fita..
Kuka sosai juwairiya keyi tana rike da kafarta ta...

*************
Yarima da magaji na tafe suna yar firar su sai jin shashshekar kuka zasuyi acan gefen hanyar..

Magaji ya girgiza kai,yanzu haka yaran nan ne masu guje guje a hanya..
Yarima yakai dubansa inda sautin kukan ke fitowa..
    Caraf ya hango ta a zaune rike da kafarta se jini ke fita...

   Gabansa ne ya fadi..
Me ya same ta?
Da gudunsa ya karasa wajenta magaji na kiran shi amma inaa...bai ma san yana yi ba..

Juwairiya kuwa ji kawai tayi ya fisgo kafarta..
A tsorace ta dago tana kallonsa cike da  mamaki..

'Yarima?'...ta fada a ranta...
Ai da sauri ta kwace kafar ta zube kasa a mutukar tsorace...
Kayi hakuri ranka shi dade,amma kama kafar baiwa iri na kaskanci ne a wajen ka...

Yarima ya tsaya yana kallonta,tun daga kan kafafunta da babu ko takalmi,zuwa kayan jikinta kodaddo
har kan fuskar ta...

Lallai ko mahaukaci ya kalleshi ya kuma kalli juwairiya sai ya fahimci level dinsu ba daya bane ko kusa,yarima yafi karfin yarinya irin juwairiya, ko ma a matsayin SA'DAKARsa bata kai ba..
Amma meyasa ya damu da ita ne haka?

Ya mike tsaye yana daure fuska,sannan yana jin haushin abunda ya aikata yanzu..

Juwairiya taji yayi shiru hakan yasa ta dago tana kallonshi..
Ita yake kallon shima,da sauri ta maida kanta kasa tana jin azabar zafi a kafarta...

Magaji ne ya karaso wajen shima..
Lafiya yarima wai baka ji ne ina ta kiran ka?
Turus yayi ganin yarima tare da wannan half burned face din...

    Juwairiya ta sake fadin,ka gafarceni ranka ya dade nayi sanadiyyar tsayar daku daga uzurinku,tana gama fadin haka ta shiga kokarin mikewa tana matse baki...

     Ji tayi kawai an kamo hannunta...
Ba ita ba har magaji se daya kalli yarima da mamaki..
  Yarima ya maida ita inda take a zaune...

Wani kyalle ya fito daga cikin alhujin wandon sa ya mika mata..
Juwairiya duk a tsorace take,wai meke damun yarima ne?me yasa yake yi mata haka?bai san cewa yafi karfin ya kyautata mata bane?

Me yasa yanzu yake nuna kulawa a gareta?ita dai tsoro takeji idan aka gansu a nan fa?wayyo Allah idan gimbiya kilishi taji wannan lbrn kashin ta ya bushe...

    Yarima kallonta kawai yakeyi jikinta har rawa yake sbd tsoro,idanunta cike da kwalla.
Ya ajiye mata kyallen a jikinta sannan ya mike tsaye baice komai ba yayi gaba...
Magaji ma yabi bayansa...

Kallon kyallen tayi se fitar da kamshi yakeyi,me yasa ya ajiye mata shi?
Ta shaki kamshin dake jiki...
Yarimaaaa me ke damunka kwanan nan ne?
Har ta mike taji kafarta na mata zugi,ta kalli kyallen yarima se lkcn ta fahimci me yasa ya bata kyallen,dan ta daure kafar ta ne..

Ina zata iya saka wannan kyallen me kyau da tsafta ta daure kafarta me datti..
Wani ganye ta dauka ta yagi rigarta kadan ta daure kafar dashi...sannan ta fara tafiya da kyal da kyal tana rike da farin kyallen a hannunta...

**************
Inna na zaune a tsakar gida tana dibar ruwa a cikin kofi su magaji sukayi sallama suka shigo..
Da fara'ar ta sosai ta amsa musu tana zolayar yarima..
Ango shikenan sai aka yarda mu ko?
Yarima na murmushi ya zauna akan taburmar dake shinfide a tsakar gidan..

   Magaji ne ya amsa innar da cewa..
Inna baki ga har wani haske ya kara bane?
Inna tayi dariya,sannan ta kwalawa khadija kira..
    Khadija kuwa dama tana jin muryarsu ta jawo kayan kwalliyarta ta shiga shafe shafenta..

Inna na kiranta ta gyara kayan jikinta ta fito...
Idanunta kyam akan yarima...tace..
Ya jalal ina wuni?

Ya dago a hankali yace lafiya kawai yana tunanin ko wannan sukuwar yarinyar ta gane manufarsa na bata kyallen oho..

  Inna tace maza khadija shiga madafa ki dauko musu abincin su..
Khadija ta juya cike da yanga zata shige madafar kenan taji muryar juwairiya tana rangwada sallama...

Da sauri ta juyo tana kallonta..
  Yarima da magaji ma sunyi mamakin ganinta a gidan...
Idanun yarima a kafarta suka sauka..
Ganin babu kyallen se wani ganye a kafarta yasa yaji wani iri a zuciyarsa,yasan tsoro ne ze hanaka daure kafar dashi...

Amma hakanan se yaji babu dadi..
Har zai dauke kansa ya hango kyallen a hannunta ta rike shi gam cike da daraja..
Murmushi kawai ya saki ba tare da ya sani ba..

   Juwairiya ta karasa ciki tana gaisar da inna..
Inna ta amsa mata a sake tana tambayar ta me yasame ta a kafar..

Kwalba ce na taka..
Ta fadawa inna a sanyeye..
Yarima kuwa gaba daya hankalinsa na kansu..
   Khadija ta shige kicin ta dauko musu abincin ta ajiye a gabansu,sannan ta karasa wajen juwairiya tana fadin,ayyah JUWAIRIYA sannu...

Yarima yaji gabansa ya buga JUWAIRIYA ya maimaita sunan,dama sunan ta kenan?ashe tana suna?wani irin dadi sunan yayi masa....JUWAIRIYA maimaita sunan babu adadi a cikin zuciyarsa......

"Khadija kuwa sbd ta burge yarima yaga ita me tausayin bayi ce,sai ta ce,zo ki zauna na saka miki magani..

Ta jawo hannun juwairiya..
Juwairiya ta shiga girgiza kai ah ah ki barshi kawai babu komai,sakon zainaba ne nazo na amsa nasan tana jirana sauri nakeyi...

  Khadija zatayi mgn se ji sukayi ance...
"Me yasa kika fiye gardama?!
Da mamaki duk suke kallonsa..
Ya dauke kai yana bude kwanon dake gabansa...kamar bashi ne yayi mgnr ba.

Khadija mamakine ya kashe ta,wai yau yarima jalal ne da kansa ke tsoma baki acikin mgnr da bata shafe shi ba,mai?"me yasa kika fiye gardama" yau she yasan juwairiya da har yasan ta fiye gardama din?oh!tafiyar su ko?toh amma a yan kwanakin ne har yasan ta haka?kishi ne ya cika zuciyarta..

  tunani kala kala khadija keyi har bata lura da inna harta bawa juwairiya wasikar ba ta mike zata fice..
Da sauri ta sha gabanta,haba juwairiya baki ga yarda kafarki ta fara kunbura bane?ta fadi da yanayin tausayi tana kallon yarima da gefen idonta..

Juwairiya ta dan kallo inda su yarima suke zaune har sun fara cin abincinsu..

Hada ido sukayi dashi,tana kokarin dauke idonta taga ya mata wani irin kallo,hakanan taji gangar jikinta ta fahimtar da ita me kallon nasa ke nufi.. (na amince da taimakon khadija)
Khadija tace muje mana...
Nagode juwairiya ta fada ta dawo ta zauna..
  
Khadija ta juya gunsu yarima tana matse muryarta tace..
Ya magaji ina wannan maganin naka?
Magaji yace ki duba cikin dakina..
Khadija ta mike ta nufi dakin..
Magaji kuwa mikewa yayi shima dan karo musu miyar fankasun da suke ci..
   Aka bar yarima da juwairiya a wajen su kadai........



_"Team RUMFAR BAYI ina gaisuwa,nagode da addu'o'in da kuke yimin,sannan ina ganin comments dinku i rlly appreciate alot,thanks alot,Allah yabar zumunci.._

*Team juwairiya*90%
*Team yarima*70%


Keep
Sharing
Voting
And
Commenting
[9/18, 3:14 PM] Aysha Galadima:           *RUMFAR BAYI*
      (A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 16
Wattpad  @afreey101


*****************
"Me yasa bakiyi amfani da kyallen dana baki ba?"

   Juwairiya taji muryar sa me dadin saurare a bayanta yana mgnr kamar bayaso dan itama zuciyarta na wajensa da bazataji me yace ba..

  Juyowa tayi kanta a kasa kafin tace a sanyeye..
Kayi hakuri ranka shi dade amma bazan iya daure kafata da abunda ya fito daga hannunka ba,dan ko kadan ban kai wannan matsayin ba..

  Yarima ya jinjina kai..sannan yace da ita,
Daga yau duk umurnin dana baki ina so ki bi shi inda har kin dauke ni a matsayin da nake din..
juwairiya ta gyada kai da sauri..

Kinci abinci?
Tambayar tazo mata a ba zata..

Juwairiya taji kamar ta nutse,miye na sa wai idan taci abinci ko bata ci ba..
  Girgiza kai tayi..

Yadan ja lumfashi idan kin koma cikin masarauta ki same ni a sashena...
Zatayi mgn taji karasowar khadija...
Khadija ta mika mata maganin tace ta shafa,ta amsa da hannu biyu ta shafa ,sannan khadija da kanta ta daure mata kafar..
Godiya sosai juwairiya tayi mata sannan ta fice....

***********
"Har ta kai wa zainaba wasikar amma ta rasa taya zata je sashen yarima,me yasa yace mata taje?tunani ne ya cika ta sosai har bataji firar da zainaba ke mata ba..

  Zainaba na lura da ita tace,lafiya juwairiya ko kafar ce?..
Kije kawai ki huta zuwa anjima.
zansa fulani ta aiko min da wata baiwar..
Juwairiya ta samu kanta da jin dadin hakan..
Ta mike tayi mata godiya kafin nan ta fice..

***************
"Tana fitowa daga sashen sukaci karo da turaki zai wuce ..
  Tayi saurin gaishe sa..

Ya amsa yana kallon kafarta..
Ciwo kikaji ne haka?ya fada cike da kulawa..
Juwairiya tace eh dazune wlh..
Turaki yace ayyah,muje na baki magani kiyi amfani dashi..
Juwairiya zata fara mu'sa masa sai kawai yayi gaba,dole tasa ne tabi bayanshi..

'Tafiya kawai takeyi,amma hankalinta na kan umurnin da yarima ya bata na zuwa sashen sa...
      Suna shiga sashen a bakin kofa taja ta tsaya,turaki ya shiga ya fito mata da maganin,amsa tayi tana masa godiya...

Turaki ya saki murmushi yace, ki rin ga kula da lafiyar ki..
Juwairiya ma murmushin tayi tace nagode sosai yaya turaki..
Juyowar da zatayi ta hango yarima da hamza a tsaye zasu wuce..

  Idanuwansa a kanta..
Gaba daya taji wani irin faduwar gaba..
Yarima ya dauke kai kamar bai gansu ba yayi gaba abunsa...

********
"RUMFAR BAYI ta nufa kai tsaye babu wadu bayi dayawa a ciki,dakin du'bu ta shiga,ta tarar itama bata nan..
Komawa tayi dakinsu ta canza kayan jikinta sannan ta zube akan taburma.

    Da sauri ta mike ta dauko kyallen da yarima ya bata dazu tana kare masa kallo,wata zuciyar na tunashe ta  umurnin sa na zuwanta sashen sa..
Ta mike da sauri ta fito kai tsaye tayi sashen nasa..

   Ta dade a waje tana tunanin ko kada ta shiga..
    Can dai ta tayi shahada ta shiga tana addu'a Allah yasa ba wani laifin tayi masa ba.
bawan dake waje ne ya sanar da shigowar ta...
    A sanyaye cike da tsoro ta shiga falon da sallama..

   Zaune yake ya lumshe idonsa..
Ta samu waje ta takure sannan tace..
Ranka shi dade gani nazo..
Har cikin ransa yaji sautin muryar ta..
A hankali ya bude ido ya sauke su akanta..

  Juwairiya tayi saurin dukar da kai..
Yarima yace,zauna yana nuna mata waje a nan kusa dashi kadan..
Juwairiya ta kalleshi taga yarda ya tsare gida dole yasa taje ta zauna wajen a takure..

Yarima bai bata lkc ba ya kwalawa bawansa kira..
Se gashi ya shigo cikin saurinsa..
Yarima ya fada masa dayaje ya sanar da du'bu a can rumfar bayi a kawo masa abincinsa yanzu..
Bawan ya amsa da toh kafin nan ya fice..

Juwairiya dai ta rasa me zatace masa,yace  mata tazo sashen sa amma ya ajiye ta a nan yayi shiru,ga ciwon dake kafar ta yana dan damunta kadan kadan...

A wajen Yarimakuwa  ya rasa meke damunsa,me yasa yake son ganin wannan yarinyar a kullum ne kusa dashi?me yasa ta dame sa har haka?

    Yadan kallo ta, tsoronsa ma takeyi daga gani,yaja lumfashi me dumi,kafi karfin baiwa kamarta yarima...ya fadawa kansa..

      Haka yayi ta tunani a zuciyarsa har bayi suka shigo da abincin jere a cikin tiren silver.
sai faman kallon juwairiya sukeyi cike da mamakin ganinta a sashen.
balle kuma a inda take zaune dan kuwa basu da hurumin zamaa  wajen,balle kuma wai tare da yarima cab...!

    Suna gama shirya abincin suka fice bakin su kunshe da gulma iri iri..

    Juwairiya ta lura da hakan dan kuwa tasan a Rumfar bayi gulma kala kala ake kawo musu..
Ta tabbata sai lbrn zuwanta sashen yarima  ya kai wa ummanta..

   Ta kalli yarima shi kam ko a jikinsa ma..
Mikewa tayi da sauri tace,uhm ranka shi dade bari na zuba maka abincin..
Jiki na rawa ta kai hannun ta dan daukar plate dake ajiye gabansa..
   Sai jin saukar lausassan hannun yarima tayi akan nata..
  Tsikar jikinta ce ta tashi..
Gabanta na faduwa ta kalleshi ido a bude...

Yarima ya motsa bakinsa,duk da shima baisan dalilinsa na taba jikinta ba kawai dai bayajin yin mgn ne kuma yana so ya tsayar da ita daga daukar plate din.
Ki barshi...ya fada yana dauke hannunsa daga nata..
Juwairiya tace toh!
Zan iya tafiya?
Yarima ya girgiza kai ,zauna kici...ya nuna abincin dake gabansu.
juwairiya ta waro ido ta dafa kirji Ni?
Yarima yace me kika dauke ni?Giwa?baki ga naci abinci bane dazun?

Juwairiya tayi wiki wiki da ido,nima zanci anjima...ta fadi kamar zatayi kuka..
Yarima ya daure fuska,umurni ne nake baki ba zabi ba...

A sanyaye ta zauna..
Yarima ya basar abunsa...
Juwairiya ta kalli delicacies din dake gabanta, miyau ta hadiye dan rabonta da abinci tunda safe da suka karya..
  Ta kalli gefen yarima taga ya dauke kai gefe..

Abincin ta diba ta hau ci da saurinta dan ta samu ta tafi da wuri..
   Yarima yayi murmushin gefen baki.
Tana kammalawa ta mike,nagode zanka shi dade Allah ya baka kujerar mulkin daura..

  Ya saki murmushin da bai san lkcn daya subuce masa ba..
Juwairiya mutuwar tsaye tayi...dan bata tunanin ta taba ganinsa yana murmushi haka,kyau da kwarjini yayi mata har bata san ta kafe shi da ido ba..

Yarima ya kalli kafarta...
Na lura kin samu masu baki magani dayawa ko? ba sai na baki wani ba...
  Juwairiya ta dauke idonta tana kallon kafar,murmushi ta saki tunawa da kyallen daya bata dazu..sai ta kwanto shi daga zaninta ta mika masa..

Ga wannan Allah ya baka yawan rai,nagode kwarai da gaske...
  Yarima yabi kyallen da kallo..
Sannan ya mike yazo kusa da ita ya tsaya..
     Bana amsar abunda na bada a matsayin kyauta..
Juwairiya ta dago da sauri,kyauta ya bata?ita juwairiya har ta kai yarima ya bata kyauta?
      Yarima ya lura da mamakin furucin sa takeyi,yace zaki iya tafiya..
Juwairiya ta juya da sauri tayi waje...

*************
"Tana shiga tafe tana tunane tunane,har ta kawo wajen ajiyar dawakai,hango mahaifinta tayi yana bawa dabbobin abinci...
Ai da sauri da gudunta ta karasa wajensa...

Lah baba! Ta fadi da karfi..
Ya juyo cike da farin cikin ganin ta,juwairiya kece haka?
juwairiya ta saki dariya baba yaushe ka dawo?shine umma bata sanar min da dawowarka yau ba?ta karashe mgnr cike da shagwaba..

  Baba ya kamo hannunta,jiya da daddare na samu dawowa,juwairiya tace nayi kewarka baba sosai,ka tafi ka barmu...
Baba yayi murmushi kiyi hakuri juwairiya kinsan fa cewa sarki da kansa ya bani umurnin tsayawa a can kasar kanon ta dabon,sannan shima mai martaba na can yaki barina na dawo kasata akan lkc, yanzu ma haka sati daya kacal zanyi na koma..

Juwairiya ta jinjina kai,su kenan basu da yan'ci sai yarda akayi dasu,gsky BAUTA batayi ba...
Zama tayi a wajen babanta suka sha fira har yamman dare sannan ta koma rumfar bayi...

"Tana shiga laure tazo ta fisgo ta cikin karfi,da mamaki take ta kallon yarda take ta janta  har suka shige daki... hansai na a zaune ta buga uban tagumi...

   Miye haka goggo laure?juwairiya ta tambayeta...
Laure ta kai mata dankwashi akai,ubanki ne !wato ke juwairiya duk yarda muke jan kunnenki ba zaki san matsayin ki ba ko?
  Juwairiya tace,na sani mana...me akace nayi kuma?tayi mgnr a sanyaye..dan tasan ruwa baya tsami banza..

Hansai tace,me ya kaiki sashen yarima?
Baki san waye shi bane? Acikin wannan watan fa zai zama sarkin daura !!!yafi karfin yarinya irin ki!bakya tausayin rayuwar ki ko!???

Juwairiya ta kalli hansai da mamaki,tace sarki?
Laure tace,kwarai kuwa,mai martaba zayyi murabus ya basa mulki kwanan nan!...

Hansai ta kamo hannunta, juwairiya a kullum ina fada miki,ke Baiwa ce!ki kare mutumcin kanki...

Juwairiya tayi murmushin yake,na fada miki umma ki yarda dani,kawai fa sako naje amsa a wajensa,kuma shi ya umurceni dana je wlh..
Laure tace,ki kula dai kinsan haukan kishin matarsa atooh..
Juwairiya ta gyada kai zan kula goggo...

**************
"Gimbiya kilishi ta kalli fulani diyya suna zaune a fadar mai martaba.
ina ganin tunda lkc ya matso kusa ya kamata mu fara shirye shirye a kan lkc..

Fulani tayi murmushi, hakane zan saka turaki ya hadu da hamza se suyi duk abunda ya dace..
Mai martaba ya murmusa, sai dai nima akwai alkawarin da nake so na cikashi a wannan babbar ranar..
Kilishi tace,muna jinka..
Mai martaba yace,akan auren yarima ne da diyar waziri nasan kun san da wannan mgnr amma ina ganin kamar lkc yayi dana cika alkawarin dana dauka shekaru dayawa da suka wuce,tunda dai anyi auren sa na farko ..
Kilishi tadan tabe baki,hakane tunda ya zama dole mu cika wannan alkawarin..
Fulani tayi murna sosai tace,lallai yarima ya cika dan gata,mai martaba yace,ai da mun gama dashi zamu zo kan sauran suma,sbd dai akwai diyar galadima da nake so a hada da shi hamza,shi kuma turaki nayi masa mgnr jikar sarkin zazzau...

Kilishi murmushin yake tayi dan ita kam tana wa hamza tanadin diyar sarkin katsina,mai zanyi da wata diyar galadima lallai kam....

"har an gama mgnr su kenan suma?fulani ta tambaya cikin tsantsar farin ciki ..
Mai martaba yace kwarai kuwa lkc kawai nake jira..
Fulani tace toh Allah ya kaimu lfy..

**************
Surayya ce ta karaso cikin lambun cike da fara'ar ta,yanzun nan ta samu labarin na'din yarima da za'ayi a karshen satin nan...

   Hango sa tayi a tsaye yana karewa wasu tsuntsaye kallo...
  Ta karasa da saurinta ta rungume sa ta baya tana murna sosai..

  Yarima yana jin kamshin ta ya gane itace..
Surayya tace,ina taya ka murna sosai sarkina...
Yarima yadan murmusa,kodai kina taya kanki murnar zama gimbiyar daura?...

Surayya ta dawo gabansa,duka biyun daidai ne...
yarima ya gyada kai..
Surayya ta kamo hannunsa,sai yaushe zaka bani damar shiga zuciyarka?
Yarima ya kura mata ido,surayya ta karkace kai,naji lbrn aurenka da diyar waziri,hawaye suka taro a cikin idanuwanta....

Yarima yace, na zata duk wannan bazai dame ki ba...
Surayya tace,inji wa?ai duk mulkin mace bazaso ayi mata kishiya ba..
Yarima ya jinjina kai....

************
Juwairiya tare da zainaba suna tafe sai lbrn wasikar da Mustapha ya aiko mata take bata...
Suna kawowa kofar lambu zainaba tace,mu dan shiga naji kukan tsuntsayena,ta janyo hannun juwairiya suka shige ciki....

  "Turus sukayi ganin yarima da surayya rungume da juna...
"Juwairiya taji gabanta yayi wani irin muguwar faduwa har se da ta saka hannu ta dafe shi..
  Zainaba kuwa sakin baki tayi..ganin basu ma ji shigowar su ba yasa tace, sannunku masoya...!

  Da sauri duk suka juyo suna kallonsu..
Yarima idanuwansa akan juwairiya dake tsaye ta dauke kanta gefe,haka nan takeji zuciyarta wani iri,meye nata aciki dan kawai miji da mata na more rayuwar su..tasan dai ita harta mutu bazata samu wannan ba..

   Zainaba tace,lallai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login