Showing 18001 words to 21000 words out of 83480 words
ya na saka shi farin ciki.
***************
"Da sassafe kuwa itace ta fara tashi taje tayi wanka sannan a cikin toilet din ta zauna ta maida tabon fuskarta.
Suna zaune rabi nata lin ke musu kayan shinfidar su akazo yin kiran su,duk suka mike suka fito waje..
Sashen yarima suka shiga hade da sallamarsu..
Yana zaune tare da magaji suka shigo..
Idanuwansa gaba daya akan juwairiya suka sauka.
A take yaji kwanciyar hankali na ratsa sa duk da kuwa tabon dake fuskarta a yanzu bayajin kyamarsa ko kadan...
Shi dai kawai ya kasa gane dalilin ta na boye fuskarta da takeyi da wannan tabon na karya.
"Magaji ne ya kallesu..sannan ya amsa musu gaisuwar su..
Ga wannan ya mika musu wasu kaya dake ajiye a gefen sa..
Zaku saka su ne yanzu dan zamu fita daku..
Rabi ce taje ta dauki kayan sannan tayi godiya suka juya dan ficewa..se jin muryar yarima sukayi yace..
Ke!!!!
Su duka duk suka juyo a tare dan basu gane wacce 'ke' din bace yake nufi..
'Shiga ki hada min ruwan wankana...'
Tsuru'tsuru sukayi dan basu gane wacece acikinsu yake bawa umurnin ba..
Magaji ne yadan fahimci rashin ganewarsu akan furucin da yarima yayi, dan haka sai ya nuna rabi dake tsakiyarsu,ke shiga ki had...
Bai kai ga gama maganar ba kawai sai ganin yarima yayi ya nuna juwairiya, waccan nake nufi...
"Juwairiya gabanta ya fadi,ta gyada kai a sanyaye sannan tayi hanyar ban dakin..
Magaji ne ya kalle shi,a zuciyarsa kuwa mamaki yakeyi,meye ke damun yarima da waccan yarinyarne,da zasu taho duk yawan bayin da aka kawo musu ita kawai ya zaba,Allah yasa ba abunda yake tunani bane,dan kuwa indai hakan ya faru,ya tabbata abokin nasa zai sha wahala ba karama ba...
Ya dai da kallon?
Yarima ya fadi yana kallon magaji daya tsura masa ido..
Magaji ya mike..ah ah babu komai idan tayi tsami ai zan ji ..yana gama fadar haka ya fice..
Yarima yayi murmushi, tsami? Ya maimaita yana girgiza kansa..kafin ya mike ya shige daki..
Juwairiya na gama hada masa ruwan wankan ta fito.
Bata iske shi falon ba dan haka dakinsa tayi sallama ta shiga..
Yana zaune wasu takardu ne a gabansa yana gyara wa,juwairiya tayi kasa da kai..
Na gama ranka shi dade..
Ya dago yana kallonta..
Kije ki shirya ki dawo...
Da mamaki tace,na dawo?
Yarima ya danyi tsaki bai amsa mata ba..
Juwairiya a sanyeye ta fita tana mamakin halayen yarima sam ta kasa gane me yasa ya canza mata haka..
"Bayan sun shirya cikin wasu riga da zani na hadin atamfa da shadda, rabi ta kalli juwairiya cike da sha'awa tace,lallai juwairiya kin ganki kuwa?
Juwairiya ta dan kalli jikinta me nayi?ko ba haka ake saka kayan ba ne?
Su rabi suka kwashe da dariya, ah ah kyau kikayi acikinsu wlh ,ko dan bamu saka kaya irin wannan ne?
Juwairiya tayi murmushi, gaskiya ne amma ni kam kayan nan sun takura ni dayawa,rabi tayi dariya dan bakya yawan daura zani ne shiyasa amma ni kam sun min wlh Allah yasa su bar mana kyauta ma..
Juwairiya na dariya ta fito dan komawa wajen yarima..
Da sallama ta shiga falon,yana zaune ga kalaci nan an kawo masa amma bai taba ba..
Barka da hutawa ranka shi dade..
Yarima ya dago yana bin ta da kallo daga kasa har sama..
Ba karamin canzawa tayi ba da kayan,a zuciyarsa yace,sai ma idan babu wancan tabon a fuskarta...
Zo ki bani abinci...
Toh...
Tana a tsugunne ta hada masa abincin,ta dawo gefen daman'sa ta zauna a nutse sannan ta fara basa abincin yana ci kamar baya so..
Ya isa haka...ya daga mata hannu..
Gyada kai tayi ta mike tace,ranka ranka shi dade zan iya tafiya?
Ya girgiza kai..
Zauna ki ci'
Ta dan kalli fuskarsa babu alamun zata iya yi masa gardama..
Ta koma ta zauna amma ta kasa cin abincin..
Kina bata min lkc'
Ya fada a da'ke yana kallonta..
Afuwa nake ranka shi dade amma akwai abincin mu a can dakinmu..
Yarima ya tabe baki...
Na lura har yau dai baki gama sanin dokokin dake cikin bauta wa uban gidan ki ba, ba'a yiwa yarima gardama kin gane?
Ta gyada kai sannan ta jawo apple ta dauka ta kai baki hannunta na jawa..
Gani tayi yarima ya dauki plate ya shiga zuba abincin a ciki sannan ga mamakin ta a gabanta ya ajiye plate din..
Gabanta na faduwa ta kalleshi..
Ya harare ta,ki cinye shi tas!
Ta zaro ido'
Yace ni kike zarowa ido?
Tayi saurin sa'dda kanta kasa,afuwan ranka shi dade..
Yadan murmusa kafin yace,toh fara ci..
Ta saka hannu ta fara ci a kunyace,wai meke damun yarima ne?kodai duk so yakeyi ya siye ta da dan abincin da yake bata dan kawai ya kwanta da ita?
A tsorace ta dago tana kallonsa..
Taga hankalinsa na wajen takardun da yake dubawa..
Anya?
Ai bata tabajin ance yayiwa bayi fyade ba,ta girgiza kai kila dan sunzo wani gari ne bayaso ace basa kula da bayin su,amma me yasa ita kawai yake kyautatawa haka?koma dai miye ita ba zata taba bari a lalata rayuwar ta ba ehe...
Tunanin me kike?hala bakiji me nace bane ko?
Juwairiya ta dauke hannunta daga cikin plate din tace,na koshi ne ranka ya dade..
Yarima ya daga kafada, toh tashi mu je.. .
Juwairiya ta mike tayi gaba harda su tuntube..
yarima yabi bayanta da murmushi s "matsoraciya "
Yau kunji ni shiru,tun safe na fita schl ne daz y..
Pls
Vote
[9/18, 3:14 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 14
Wattpad
***************
"Gidan wani babban dan kasuwa sukaje wanda yana cikin manyan yan kasuwa na duniya gaba daya..
gidane na zamani mai kyan gaske gashi makeke sosai har yaso ya tsorata su juwairiya...
' Zo kuga kallo kuwa wajen su, rabi har dasu sakin baki,tana zungoro juwairiya da zabba'u..
A waje suka zauna kan wasu fararen kujeru masu kyau su kuwa su yarima suka shige ciki dan an aiko wani ya shigar dasu...
"Sun dade a zaune wajen, juwairiya gaba daya zaman ya gundure ta,dan tun suna firar kyaun gidan har kowa ya gaji yayi shiru..
mikewa tayi tana dan shawagi a wajen..can ta hango wasu fure masu kyan gaske dan bata taba ma ganin irin su ba a can kasar tasu (rose flower)
Da sauri tayi wajen tasa hannu ta tsi'go daya tana murmushin ta mai kayatarwa..
***************
Yarima tare da magaji na tare da wannan babban dan kasuwan dan isar da sakon mai martaba na son fara fafada kasuwancin sa a nan kasar ta chadi.
Yarima ya gama bayani ya dauki cup din tea da a gabatar musu yayi dan sipping kadan...
Ya gyara zamansa...
Open glass din dake gefen su ya kalla...
Can ta hango ta rike da furen a hannu ta na dama tana murmushinta...
Hakanan yaji ta burge sa sosai ga view din wajen se ya kara mata kyau a idon yarima,ya murmusa kawai yana kokarin dauke kansa ne kawai yaga wani saurayi na karasawa wajen ta...
********
"Yan mata ya kike?
Taji an fadi da hausar da bata goge sosai ba..
Ta dago ta kalleshi da rashin sani...
Lafiya ta fada tana rusunawa kasa..
Yace No ah ah basai kin rusuna min ba,kema din da mutanen nigeriyar kika zo?
Juwairiya tace eh tana dukar dakai..
Ya saki wani irin shu'umin murmushi yana karewa jikinta kallo...dan ya fahimce baiwa ce ita...
Furen hannun ta ne ya fadi kasa sbd tsabar a tsorace take sosai,jikinta har rawa yakeyi ganin irin kallon da mutumin yakeyi mata har da yashi leben sa..
Da sauri ta du'ka dan daukar furenta tayi gaba..
Kawai sai jin hannunsa tayi a kugunta yana shafata...
A firgice ta dago tana kallonsa cike da tsoro..
Miye....ha...ka?muryarta na rawa ta fada..
Yayi mata murmushin yaudara..
Yan mata ina son irin ki sosai,zaki zauna dani?zan siye ki da kudi masu yawa na baki ga'ta da yan'ci....
Mamakin kalamansa tayi sosai...kuka ne yazo mata ba shiri dama abunda ake fada kenan?yau ta shiga ukun ta..
Shi kuwa ganin haka sai yasa hannu ya jawo ta jikinsa wai ze lallashe ta..
**************
"Yarima gaba daya wutar sa daukewa tayi,fushi da takaici ya mamaye zuciyarsa ,cup din dake hannunsa ne yayi wurgi dashi da karfi...
Duk su magaji suka kalleshi da sauri cike da mamaki.
Ya mike kawai cikin bacin ran da baisan me yasa yake jinsa ba yayi waje...
""""Juwairiya nata kokarin ture mutumin daga jikinta cike da tsoro,kuka takeyi sosai ganin wani irin sabon al'amarin da bata taba fuskantar irin shi ba,duk da tabon dake fuskarta amma wannan mayen mutumin sai da ya tunkare ta haka,ko su nan basa kyamatar masu tabon ne...
Bata ankara ba sai ji tayi an fisgo mutumin cikin karfin gaske..
Tayi sauri ja da baya tana kallon yadda yarima ke saukar wa mutumin nan tagwayen marika..
Mamaki sosai ne ya rufe ta,meyasa yarima ke taimake ta,wacece ita?ita ba kowan kowa ba banza baiwa marar galihu...
Da kyal magaji ya amshi mutumin daga hannun yarima yana mamakin karfin halin sa..gashi kuma wannan deal din da sukazo dashi da kyal ne ya zama successful tunda yarima ya gama kufsa musu...
Dan kasuwan kuwa ba karamin fushi yayi ba dan kuwa kanin sane yarima ya gama jubga,su tafi kawai yace musu zasu ji daga gare sa idan yayi shawara....
Yarima ko a jininsa suka tattara sukayi gaba.
Juwairiya kuwa hawaye basu dauke mata ba su rabi ne ke ta lallashinta...
******************
Koda su ka dawo masaukin su yarima kwanciya kawai yayi akan gado yana jin wani abu a cikin zuciyarsa.. tambayar kansa yayi miye dalilinsa na ka're mutumcin wannan yarinyar?
Duk yarda yaso ya gano dalilinsa kasa wa yayi...
Magaji ne ya shigo yana kallonsa kawai ya girgiza kai..
Zama yayi kusa da shi yace..
Gobe da sassafe zamu koma tunda dai mun zo munyi abunda ya kawo mu sai dai a tunani na kai ma kasan abunda ka aikata ba zai....
Yarima ya tsayar dashi..
Na sani magaji,ba zai amince da deal dinmu ba...amma inaso dan Allah kada wannan lbrn yakai wa su mai martaba ko umma...
Magaji ya gyada kai kada ka damu zan gargadi dukka bayin da mukaje dasu..
Yarima yace yauwa sannan ya koma ya sake kwanciyarsa..
Magaji ya mike ya fita kice da tambayoyi a cikin zuciyarsa...
"Har dare ya tsala sosai juwairiya na takure a gefe tana fitar da kwalla, se yanzu ne ta fuskanci duk abubuwan da su ummanta ke fada mata..
Ita dai Tsoro takeji sosai,addu'ar ta daya Allah yasa gobene komawarsu, ta koma rumfar bayin ta wajen su ummanta masu sonta,Allah kadai yasan halin da zasu shiga idan sukaji abunda ya faru da ita yau....
Yarima ma dai bai samu barcin ba ko kadan,duk yarda yaso ya samu runtsawa kasawa yayi,yana nan kwance shiru..
Can ya mike yana fadin,ko ta bar kukan yanzu?
Ya ja lumfashi hade da mikewa ya saka riga ya fito waje..
A gaban kofar su ya tsaya yana rike da kugunsa,kodai har tayi barcin ta ?
Yana kokarin juyawa yaji shashshekar kukanta daga cikin dakin...
Tsayawa yayi kawai ya rasa me ya kawo sa wajen ma?zuwa zayyi ya lallashe ta ko me?shi yarima jalal ya lallashi mace!!!!
inaa... ai hakan ze zubar masa ki'ma da girman sa ne...yadanyi tsaki yana jin kukanta na ratsa shi a sanyeye ya juya ya koma dakinsa..
***************
"Da safe idanun juwairiya duk sun kunbura dan bata samu runtsawa ba a wannan daren..
Har suka gama shirin su Rabi se faman sake lallashinta takeyi..
Suna gama shirin ne magaji yazo ya sanar Musu da su fito za'a tafi yanzu,juwairiya tayi mamaki da yarima bai kirasu hada masa ruwan wanka ba da safen..
" A tsaye gaban mota suka tarar da shi ya jingina, fuskarsa kawai zaka kalla ka fahimci baya jin dadi sosai..
Juwairiya ta kura masa ido,ya taimaka mata jiya taimakon da ba zata taba san yarda zata gode masa ba...
Ji tayi magaji na fadin,yarima ya jikin naka?kodai mu kara kwana ne sai ka kara jin sauki tukun?
Gabanta taji ya fadi,bashi da lafiya me ya same shi?kodai ta jawo masa wani babban matsalar ne jiya?
Rabi taji tadan taba ta,suka shiga cikin motar su hankalinta na kan yarima...
**************
"Tafiya kawai sukeyi amma juwairiya tunanin yarima takeyi,ta rasa me yasa takejin tausayinsa dan bashi da lfy,tasan ita ba kowa bace a wajen sa,kodan ya taimaka mata ne jiya oho..
Lokacin da suka iso kasar daura dare ya tsala sosai..
Suna fitowa daga cikin mota juwairiya ta hango yarima yayi sashen sa yana tafiya kamar bayaso...
Lumfashi ta sauke,ko ya jikin nasa yanzu?
Wai meke damunta ne,yarima ne fa,yarima jalal,me jiran kujerar mulkin kasar daura,yana da wadan da zasu damu dashi da suka fi ta mahimmanci da daraja a rayuwarsa..
Gyada kai tayi,dan kawai ya taimake ni shiyasa na damu da lafiyarsa,ta saki lumfashi tana murmushin jin dadin dowawar ta,kullin kayanta ta dauka tayi rumfar bayi da gudun ta..
Tana shiga duk suka zo suna rungume ta cike da murnar dawowar ta,hansai ba karamin dadi taji ba ganin diyar ta dawo lafiya...
******************
Washe gari..
Yarima ne zaune a gaban mai martaba..
Sannunku da dawowa jalal ina fatan kun dawo mana da labari mai dadi..
Yarima ya gyada kai,amma munyi dashi akan zai neme mu idan ya yanke shawara..
Mai martaba yace,babu damuwa sai mu jira shi muji ai...
Yarima ya mike daidai lkcn da aka sanar da shigowar su Turaki tare da zainaba..
Zainaba ce ta fara gaida shi,a sanyaye ya amsa mata,suka gaisa da turaki kafin ya fito daga bangaren...
"Hango ta yayi a tsaye tana wasa da yatsun hannunta da gani jiran zainaba takeyi a wajen.
Haka nan yaji wani sanyi ya ratsa sa hatta ciwon kan da ya tashi dashi se yaji ya tafi bat!..
Ita kam juwairiya tana tsaye ne amma sai taji kamar ana kallonta..
Ta dago a hankali....
Sai Hango shi tayi cikin kayan alfarma kamar kullum,amma mai?sai kawai taji zuciyarta na ayyana mata cewa "yayi kyau"
Ta girgiza kanta da sauri ta sake yin kasa da kanta tunda tasan ya tsani ganin fuskarta...
Shi kuwa yarima tana yin da kasa da kai sai yaji wani iri,ya tuna yarda yake kyamatar ta a baya..
Juyawa yayi a sanyaye ya fice...
********************
"Surayya na gani a tsaye a gaban sashen yarima,gaba daya hankalinta a tashe yake tunda taji ance ya dawo da zazzabi jiya bata runtsa ba..
Tana hango shi ya tunkaro sashen tayi saurin zuwa wajen sa..
Yarima ya jikin ka?
Ya kalleta kawai yayi gaba ya shige ciki..
Surayya ta kalli baiwar dake bayanta,ki jira ni a nan,itama ta shige ciki da saurinta...
Yarima ta iske a kwance yana kallon sama...
Ta shigo ta zauna a kusa dashi tana kai hannunta saman goshin sa,zafi taji rau,da sauri ta dauke hannun tana kallonshi cike da tausayawa, a shagwabe tace,zazzabi ne fa a jikin ka..
Yarima ya lumshe ido,shi kansa ya rasa dalilinsa na kin shan magani tun jiya,duk runtse idon da zayyi se ya hango abunda ya faru tsakanin wannan yarinyar da mutumin nan,me ke damun sa ne haka?
Surayya tadan turo baki,ka tashi muje sashen umma kasha magani,kasan dai idan taji baka da lfy kuma baka sha magani ba hankalin ta ne zai tashi...
Yarima ya bude ido ya sauke su akan surayya,me yasa bazai so ta bane?
Hannu yasa a sanyaye ya shafa gefen fuskarta..
Surayya taji wani irin yaar a gaba daya jikinta..se kallonsa kawai takeyi..ko me ya same shi haka kuma oho?
Ka tashi...ta sake fada a sanyaye. .
Yarima ya mike zaune yana fadin..
Kije ki turo min da me maganin kawai..
Surayya cike da murna tace,da gaske?
Yarima yayi banza da ita yana juya mata lulu eyes dinsa..
Ta mike da sauri tayi waje..
Shi kuwa yabi bayan ta da kallo....
" _Kuyi hakuri baku ji ni ba jiya,data na ne ya kare,idan nayi subscription zaku ringa jina akan lkc"_
Please
Vote
[9/18, 3:14 PM] Aysha Galadima: *RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 15
Wattpad @afreey101
************
".....Bayan sati biyu...."
"Juwairiya na zaune a cikin RUMFAR BAYI, lkcn karfe goma na dare ne amma a cikin rumfar se ka rantse da Allah ko shidda ta yamma batayi ba.
dan kuwa sai a lkcn ne suke samun yin duk wata hidimar kan su,irin su wanki,kitso da sauran su...
" Rabi ce ta kalleta tana jefa gyadar dake hannunta cikin bakinta..
Ya dai juwairiya kinyi shiru sai mgn nakeyi kin wani share ni...
Juwairiya tayi dan firgigit ta dawo daga duniyar tunanin data tafi..
Kai Ina fa kinji rabi,kikace mai ma?
Rabi takai mata dukan wasa,ai dama nasan uwar shegu kikayi dani..
Laure ce ta karaso wajensu da yan kayanta a hannu..
Juwairiya ta kalla tana narke murya,diyata ga ka'ron wankina..
Juwairiya ta zunboro baki,goggo laure duka duka fa sati biyu kenan danayi miki wanki..
Laure tace,ke yar gari yo ni wanki har nawa nayi miki da kina yar jaririyarki uhm!
Juwairiya ta juyar da kai,laure takai mata duka tace,ni kike juyawa ke'ya?yar fama kawai..
Hansai ce ta karaso wajen nasu, ta kamo hannun juwairiya, sannan ta kalli laure,babu ruwanki da diyarta ,wanki kuma bazatai ba,ai ba ajiyeta kikayi ba,muje ya'ta,laure ta rike baki,ni hansai?ni hansai?lallai ina nan zamana zaku dawo ai,kici gaba da shagwaba ta kema sai tace baki isa ba... ta ja tsaki ta juya tayi gaba..
Juwairiya da hansai suka shige daki suna mata dariya..
**************
"Da sassafe ranar alhamis juwairiya tayi shirin ta tsab sannan ta wuce wajen uwar dakin ta..
Tana shiga sashen zainaba ta same ta a zaune..
Ta gaishe ta tana kokarin shigewa ban dakine zainaba tayi saurin kiranta..
Juwairiya zo kiji..
Tazo ta duka har kasa tace gani..
Zainaba tace so nake kije min gidan waziri ki amso min wasikar da Mustapha ya aiko min da ita jiya,juwairiya tayi murmushi wato baki manta da ranar ta yau ba kenan?
Zainaba ta murmusa tana gyara zaman ta,ni kaina mamaki nakeyi wlh,kullum cikin addu'ar Allah ya kawo min wannan ranar nake,tunda yace min ze aiko min da lambar wayar su ta landline gaba daya na zaku dana kira naji muryar sa..
Juwairiya ta saki baki cike da mamakin kalaman zainaba..
Zainaba ta taso ta rufe mata bakin tana dariya..
Juwairiya tayi murmushi sannan ta mike tace toh bara naje na dawo, da sauri ta juya ta fice.....
**************
"A nutse take tafiyar ta har ta fito babbar kofar masarautar,can ta hango su a tsaye tare da wani bawa (wato yarima da magaji kenan)
Da sauri ta dauke kanta sannan ta karawa tafiyar tata sauri...
Magaji ne ya fara hango ta,ya kalli yarima yana sosa kashin kansa yace,ni fa wancan yarinyar se na riga gani kamar na santa a wani waje..
Yarima ya kalli gefen da magaji ke nuna masa...
Can ya hango ta sai buga sauri takeyi kamar