Showing 57001 words to 60000 words out of 83480 words
ba dan kuwa munyi wa zarah'u alkawarin zamu bata damar zabar mijin da zata aura..
Kuma a wannan lkcn ma a yarda na lura da ita ba auren bane a gabanta karatun da takeyi shi ta saka a gaba..
Ana cikin haka ne kuma sai muka riski ziyara daga sarkin kanon dabo a lkcn daurin auren garba..
Mai martaba ne yayi kiran dukka iyalensa dan gabatar dasu ga sarki ABU-TURAB...
Duk muka hallara a cikin babban falon mai martaba dan gaisawa da babban bakonsa..
Amma banda zabba'u wacce take can bangaren kakarta suna shan firarsu..
Marka ce na aika dan ta sanar da ita neman gaggawar da mahaifinsu keyi mata...
Zabba'u da gudunta ta shigo falon da sallama..
Kallone ya koma kanta..
A lkc guda kuma ta shiga zuciyar sarki ABU-TURAB farat daya....
Bayan mun gama gaisawa ne da sarki duk muka tashi muka fice dan basu waje..
Sarki ya kalli mai martaba yace..
Takawa Duk wadan nan yan matan yaranka ne?
Mai martaba ya gyada kai yace,duka yarana na ne ni na haife su..
amma zarah'u ce karama ce a cikinsu duk da tafi su jikin girma...
Sarki abu-turab ya jinjinar da kai kafin yayi sallama da mai martaba suka kama hanya..
Sati daya da zuwa ziyarar shi sai ga waziri da wambai sun sake sauka a kasar zazzau...
Munyi mutukar mamakin ganinsu dan basu aiko mana da wasikar zuwan nasu ba..
Mai martaba ya saka akayi musu tarba mai kyau suka ci suka sha kafin aka sake zama dan a gaisa..
Waziri bayyi kasa a gwiwa ba ya sanar da mai martaba sakon sarki abu-turah...
akan sunga IRI a cikin gidan sa kuma suna so..
Murna sosai mai martaba yayi dan kuwa yayi wa AMINA sha'awar abu-turab din..
Yayi murmushin su na manya yace..
Toh madallah ai babu wata matsala tunda akwai dangantaka mai karfi ta zumunci a tsakanin mu..
Waziri da wambai sukayi farin ciki sosai sannan cike da murna suka koma kasar kano...
Bayan sun sanarwa sarki abu-turab amincewar mai martaba ba karamin dadi yaji ba..
A take kuma yaje ya sanar ma mahaifiyar sa HAJJO..
Itama din taji dadi sosai dan kuwa tana mutukar son dan nata ya karo aure sbd irin rikicin da suke samu a wajen matar sa ta faro HINDU...
"Bayan wata daya ta shude sai ga sarki ABU-TURAB ya sake kawo mana wata ziyarar amma a wannan karon Zance ne ya kawo sa na Aure..
Mai martaba ya tare shi cikin murnar sa ya kuma saka YAYA BABBA (kishiyar ammi)ta shirya AMINA dan su dan gana da abu-turab din..
A can falon baki inda ya sauka aka shirya musu wajen da zasu kebe dan fahimtar junan su..
"Lkcn da amina ta shiga falon abu-turab ya kyalla ido ya ganta sai ya mike da sauri yana kiran waziri dake waje...
Ya nuna amina yace,ba wannan bace nake so..
Waziri mamaki ne ya kamasa..
cikin Fa'da suka koma a nan abu-turab yake sanarma mai martaba shi ba amina ce yake nufi ba wata ce daban..
Mai martaba yayi mamaki dan kuwa a lkcn yan matan gidan duka basu fi guda uku ba..
HAJIYA (kishiyar ammi ce itama )ya sake sanar ma wa akan a shirya BILKISU ta zo fada yana nemanta..
Bilkisu na zuwa abu-turab ya sake cewa ba ita bace..
Sai lokacin ne hankalin mai martaba ya tashi,dan kuwa yasan ba kowa bace abu-turab yake mgn face ZARAH'U ...
Jiki a sanyaye ya saka aka zo aka sanar min dana shirya zarah'u taje fada..
Nayi mutukar mamaki sosai sannan kuma hankalina ya tashi..
A haka na matsa mata ta shirya ta tafi..
Tana shiga Abu-turab yace ai itace yake mgn,shi itaa yake so a basa..
Mai martaba ya rasa yarda zayyi gashi kuma yayi musu alkawari tun da farko akan cewa ya basu..
damuwa sosai ne ya shiga dan ba'asan sarki da mgn biyu ba..
Bayan su abu-turab sun koma kasar su akan zasu dawo dan a saka ranar biki..
mai martaba ya same ni dan neman shawarata..
Rasa abunda zan fada nayi dan kuwa ina son farin cikin ya'ta amma kuma rashin amincewa sarki ABU-TURAB kamar zubar da ki'ma da mutumcin masarautar mu ne..
Cikin rasa wata mafita muka yanke shawarar aurawa abu-turab ZARAH'U...
Lkcn dana same ta da mgnr ba karamin tashin hankali ta shiga ba..
Kai tsaye ta fada min ita bata son Shi..
Cikin lalama da dadin baki na samu zarah'u ta amince akan zatayi mana biyayya amma fa ita ba dan tana jin zata iya son abu-turab a zuciyarta ba..
Ba bata lkc Aka saka ranar biki..
Gaba daya jama'ar gidan suka hau jin haushi da kishin mu,har fadi sukeyi asiri naje nayi dan diyata ta auri sarkin kano...
Duk habaicin su bai wani dame ni dan kuwa yarda zarah'u duk ta rame sbd damuwar data saka a ranta nima sai hankalina ya kasa kwanciya da auren dolen da muke shirin yiwa diyar mu..
Ranar asabar da rana aka daura auren zarah'u da abu-turab a ranar kuwa da wani mugun zazzabi zarah'u ta tashi..
Jikinta babu wani sauki a haka muka lallaba aka kaita dakin ta a can babbar masarautar ta kanon dabo...
AMMI taja lumfashi tana share kwallar dake fitowa a cikin idanunta..
Tunda zarah'u ta shiga gidan take samun matsala sosai a wajen uwar gidan abu-turab Hindu..
Sai dai saukin abun shine,mahaifiyarsa da shi kansa suna mutukar kula da ita..
Hakuri kawai takeyi a gidan dan kuwa a kowace rana sai ta hadu da tsangwama a wajen HINDU da ma yan uwanta..
Shekarar ta daya a gidan Allah ya bata ciki....
Wayyo zo kiga kishi karara a wajen hindu da tawagar ta...
Lkcn ba karamin kula take samu a wajen abu-turab ba,kyaututtuka sosai yake bata yana nuna mata soyayya..
Hindu ta kasa hakuri da irin bakin ciki da kyashin da takeyiwa zarah'u, dan haka suka hada baki da wani bawa me kula da sashen abu-turab suka kulla wa zabba'u sharri..
Akan tana gayyatar wannan bawan cikin dakinta suna ZINA..
Sarki abu-turab ba karamin girgiza yayi ba da jin wannan zancen ba..
Duk da haka bai yarda ba..
Ya saka aka kirawo masa duka bayin dake aiki a sashen zarah'u dan su bada sheda akan zargin da akeyi mata..
Ga babban mamakin zarah'u gaba daya sukace ai anyi haka,tabbas suna ganin wannan bawan yana shige da fice a dakin zarah'u kullum dare..
Zarah'u ta fashe da kuka mai tsuma rai tana rokon abu-turab daya yarda da ita amma inaaa...yayi fir yaki yace ta kwashe inata inata tabar masa gidan sa...
Cike da tsananin damuwa zarah'u ta dawo masarautar zazzau da karamin cikin ta wata shidda...
Lkcn data same mu da wannan zancen ba karamin fusata mukayi da ita ba dan kuwa mun san zarah'u tasha fadin rashin son da takeyiwa abu-turab..
Daki nakai ta na shiga tuntubar ta ta fada min gsky ko da gaske ne ta aikata abunda ake zargin ta tayi.
Tana kuka ta shiga fada min ita shirri ne akeyi mata wannan cikin ma na jikinta na abu-turab din ne...
Mai martaba ba karamin fusata yayi ba,dan lbr ne ya shiga yawo a kasar zazzau akan sarki ya bar diyarsa tayo yaji kuma ya kasa daukar wani hukunci akanta..
Watan zarah'u biyu mai martaba ya hadata da wasu yayyinta suka koma can kasar kano dan yin bi'konta..
Da kyal abu-turab ya amince dasu bar ta su wuce komai ya wuce..
Rayuwa tayi wa zarah'u zafi..dan kuwa abu-turab banzatar da ita yayi acikin masarautar dan babu me kula ta,ko bayin dake tare da ita ma gulmar ta sukeyi..
Cikin ta na wata tara a wani dare hindu ta saka ayi mata (kidnapping)din zarah'u a cire dan dake cikinta a kashe shi ko kuma gaba daya a kashe zarah'un dan bazata taba bari ta haihu acikin masarautar ba.
dan dama tayi tayi ta zubar da cikin Allah bai bata iko ba..
Lkcn da aka fita da zarah'u wani bafade ne ya gansu,dan haka yabi bayan kattin har suka kaita wani daki suka ajiye..
Bayan sun ajiyeta ne sai yaji suna mgn akan abunda hindu ta saka su suyi..
Hankalinsa ne ya tashi sosai..
Jiki na rawa yaje ya taimakawa zarah'u suka gudu...
Suna cikin gudun sukaji muryoyin kattin mazan a bayansu..
Bafaden ya kalli zarah'u gaba dayan su sun gama jigatuwa..
Yace,ranki ya dade ki wuce abunki,ki gudu ki ceci rayuwar dan dake cikin cikin ki..
Zarah'u na kuka sosai ta girgiza masa kai..
Bazan iya tafiya na bar ka a wajen wadan nan mugayen mutanen ba..
Bafaden ya runtse ido sannan da kyal ya samu zarah'u tabar shi a wajen taci gaba da gudu dan ceto rayuwar ta dama na dan dake cikinta
Ba karamin wahala da jigata tayi ba,gudu kawai takeyi bata san inda zataje ba...
Sai gashi ta shigo kasar daura,ta haife mana JUWAIRIYA sannan tace ga garin ku nan......
Not edited pls am tire😌
Team RUMFAR
*RUMFAR BAYI*
(A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 34
Wattpad @afreey101
******************
"Ammi ce da kanta ta saka juwairiya a gaba suka ringa shiga bangare bangare na cikin masarautar dan gaisawa da matan mai martaba da kuma ya'yansa..
Daga karshe Ammi ta kaita wani tsohon sashe na mahaifiyar ta zarah'u ..
Hawaye ne suka shiga zuba daga idanuwanta..ba karamin tausayawa irin rayuwar da sukayi ita da mahaifiyar ta ba takeyi ba...
Kallon dakin takeyi cike da tausayin irin rayuwar da mahaifiyar tayi a baya..
Ammi ta dafa kafadarta,ki ci gaba da yi mata addu'a kinji?
Juwairiya ta gyada kai sannan tayi wa ammi tambayar dake ta cin ta a rai tun jiya..ta saukar da kai kasa tace..
"Ammi yanzu shi sarki Abu-turab din har yanzu bai gano sharri akayiwa ummar ba?
Sannan har yanzu suna tare da matarsa hindu ne?
Ammi ta kamo hannunta suka zauna a gefen gadon dake gefen su..
Ta kalli juwairiya tace, kin san indai mutum baya da hakkin wani...
Toh Allah sai ya san yarda yayi gaskiya ta fito koma daren dadewa..
Wannan bafaden dai daya taimakawa zarah'u ta tsira daga hannun wadan nan mutane shine ya bayyanar da komai..
Duk da dai ba karamin wahala da azabtuwa yayi ba a wajen wadannan mutanen..
Sai da zarah'u tayi kusan sati daya da bacewa sannan Allah ya kubotar da wannan bawan..
Kai tsaye yan farautan da suka taimake shi sukayi fadar sarki abu-turab dashi..
Shi kuwa ya fayyace wa sarki duk abunda ya faru da zarah'u sannan ya sanar masa da sa hannun HINDU aciki..
Abu-turab a take a rikice susuce..
Ya saka aje a kawo masa hindu da duk mutanen da suke da sa hannun aduk abubuwan da akayi wa zarah'u..
Hindu na jin asirinta ya tuno ba karamin rikice wa tayi ba..
sbd tashin hankali da kuma mugun hali irin nata sai sakawa tayi yayanta ya taimaka mata ta gudu daga masarautar gaba ki daya....
Toh a cikin ikon Allah kwana biyu da guduwar ta ta sai gashi an kawo gawarta har cikin masarautar kano..
wai yan fashi ne suka tare su a hanyar su ta shiga kasar nijar suka kwashe musu duk kudin dake garesu sannan suka kashe su..
Abu-turab bai amsa gawar hindu ba,yace aje can akai wa yan uwanta shi babu ruwan shi da ita tunda ya dade da sakinta..
Abu-turab ya saka mutane dayawa dan neman zarah'u hakama mu ma a nan amma shiru babu wani labari akanta....
Mahaifiyar sa ce ta matsa masa akan sai ya sake wani auren..
Toh a lkcn mijin AMINA ya rasu sai mai martaba ya bashi ita,abu-turab bai wani musa ba aka daura musu aure bayan shekara daya kenan da batan zarah'u...
a halin yanzu kuwa har sun hayayyafa sannan kuma ya kara aure bayan ita,ya auri diyar sarkin AZARE JAMILA ....
Juwairiya taja lumfashi lallai ta tausayawa iyayen nata..
Ammi tace,kada ki damu idan kika kara kwana biyu zamuje ki gansa kinji?
Juwairiya ta gyada kai..
Mikewa sukayi suka bar sashen..
********
*Masarautar daura...*
"Bakin ciki ne da takaici suka taro sukayi wa surayya yawa..
Ace wai a halin yanzu ko kallo bata ishi jalal ba?
Sai dai ta ringa samun labarai daga wajen umaymah wai a kullum sai ya gayyaci khadija zuwa sashensa sannan yaje ya dauke ta su riga fita yawon shan iska da yamma...
Surayya ta dunkule hannu ta naushi gadon da take a kai..
"Dole ne na san abunyi dolene na tashi tsaye ta nemo wa kanta mafita.....
"Jalal ne zaune a kan gadonsa yana tunanin ko a wane hali juwairiya take ciki yanzu?ba karamin kewar ta yayi ba,kodai ya shirya ne yaje zazzau din..?
Sallama akayi ne ya katse masa tunanin sa...
Khadija ce ta shigo dakin..
Jalal ya kura mata ido yana wani nazari..
Khadija ta sakar masa murmushi, ya jalal ka tashi muje toh...ina can ina ta jiran ka ashe ko ma niyyar zuwa bakayi ba..
Jalal ya lumshe ido ya bude su ahankali...
yau gaba daya baya jin fitar nan gashi kuma ya sabar mata yadan ja tsaki..
Khadija ta karasa wajen sa tashiga jan hannunsa..
Jalal yaki mikewa ko motsi bayyi ba ma..
tana ta faman jansa a dolensa ya mike yana fadin..
Kin cika rigima khadija..
Tayi masa gwalo tace..
naji din nidai muje yaya..
Jalal ya daura alkyabbar sa suka fito..
Suna tafiya a cikin masarautar bayi nata faman gaida su suna yaba dacewar jalal da khadija..
Samira da turaki ne suka hango su fitowar su kenan daga sashen fulani diyya..
Karasawa sukayi wajensu..
Khadija da samira suka gaisa hakama jalal da turaki..
Jalal ya samu kansa da tambayar samira ko ta samu wasika daga can masarautar su?
Samira ta girgiza masa kai tace,ah ah ina dai saka rai a cikin satin nan.
Jalal ya jinjina kai kawai kafin yayi gaba khadija tayi saurin binsa..
********
"Rayuwa tayi wa juwairiya dadi..
ba karamin canzawa tayi ba a cikin yan kwanankin nan..
gashi kuma har tana neman kusan wata daya kenan mai martaba bai bada izinin tafiyar ta kasar kanon dabo ba..
Yau dai da kyal ta samu Ammi ta hada ta da wata baiwa suka fito zuwa sashen khaleed..
Suna shiga suka tarar dashi shima ya fito cikinsa..
juwairiya ta gaishe shi tana murmushi,KAWU irin wannan gayun haka?
Khaleed yayi dariya,diyata zance zani ..ko zakije ne ki gaisa da matar Kawu..
Juwairiya tayi dariya, khaleed ya kamo hannunta muje zakiji dadin haduwa da ita..
Wani bangare taga sun shiga duk a cikin masarautar..
Ta kalle shi da mamaki..
Kawu matarka acikin masarautar nan take itama?
Khaleed yace,kwarai kuwa diyar kanin me martaba ce fa..
juwairiya ta jinjinar dakai,ashe kuma a nan kuna auren hadi..
Khaleed yace,tsoro kikeji?
Juwairiya tayi dariya tsoron me?
Khaleed yace,a hadaki da wani mana..
Juwairiya taji gabanta ya fadi, a hada ta da wani?AMALEN ta fa?ta cije harshenta,zuciyarta JALAL take so bazata taba iya rayuwa da wani ba,ba zata maimaita irin rayuwar da mahaifiyar tayi ba.....
Budurwar khaleed,me suna sumayya tana da kirki sosai,a take shakuwa ta shiga tsakanin su da juwairiya...
Washe gari....
da yammacin ranar talata suka fito ita dasu hassana da hussaina..
Juwairiya ta kallesu,wai na tambaye ku mana?
Hassana tace muna jin ki..
Juwairiya tace,idan kamar mutum yana son ya aikawa wani wasika da baya cikin kasar nan taya mutum zayyi hakan?
Hussaina ta rike baki..badai diyar tamu har ta samo mana suriki ba?
Juwairiya ta ware ido tana nuna kanta..
Ni ah ah wlh uwar dakina..ah ah zainaba kawata ce nayi wa alkawarin aikawa wasika shine nake son na cika mata alkawarin..
Hassana tace,nidai ban taba aika wasika ba amma muje bangaren hajiya na tabbata ya mas'ud zai sani..
Juwairiya tace toh muje dan Allah..ai kuwa duka dunguma suka tafi..
Suna shiga bangaren hajiya sukaci karo da yasira...
Yan biyu suka gaida ita juwairiya ma tayi yarda sukayi..
Yasira ta kurawa juwairiya ido tana tuna kanwarta zarah'u da sukafi shakuwa sosai a baya...
Hawaye ne suka ciko mata a ido,ta dauke kai tayi gaba ko mgn kasa yi musu tayi..
Juwairiya taji jikinta yayi sanyi..
Hassana ta dafa ta..
Kada ki damu kanki,bawai dan sun tsane ki bane kawai dai kina tuna musu da yaya zarah'u ne..
Juwairiya ta jinjinar dakai kafin suka shige ciki...
Hajiya uwar gidan mai martaba ce itama ta manyanta sosai..
A cikin falonta suka tarar da ita bayi na ta mata hidima..
Duk suka gaishe ta cikin girmamawa ..
Ta amsa a sake tana fadin..
Sai yau kuma yan matan suka tuna dani?
Hussaina tace,ah ah wlh hajiya kina ran mu..
Hassana tace,hajiya wai ya mas'ud fa ya na nan kuwa?
Hajiya tace,kun bani ajiyarsa ne?yaron da sai nayi sati ban saka shi a idona ba..
Hassana tayi dariya ai dadin autancin kenan..
Hajiya tace,ku duba sa dai can bangaren maza kila ku same shi..
Juwairiya tace,mun gode hajiya..
Hajiya tace,ai duk kin fi iyayen naki hankali..
Suna dariya suka mike suka fice..
Sbd rashin sa'a suna fitowa sashen hajiya wata baiwa ta tare su da sakon Ammi akan suje tana neman su..
"Lkcn da suka shiga bangaren ammin,khaleed suka tarar a falon tare da haruna suna cin abincin rana..
Juwairiya ta gaishe su duk suka amsa a sake...
Ammi ce ta fito daga cikin dakin ta tace,wai ku yanzu ace kun fita tun safe baku san ku dawo kuci abinci ba ko?
juwairiya tace,kiyi hkr ammi..
Ammi ta kamo hannunta ai baki da wani laifi ke kam yaran can dai dama haka suka gada...
Muje ciki na nadanar miki abincin ki..
Yan biyu suka saki baki suna kallon ammin farat daya ta daina kuya dasu sai juwairiya..
Khaleed da haruna ne suka hau musu dariya..
"Washe gari mai martaba yace juwairiya ta shirya zasuje can kasar kano dan ta gana da mahaifinta..
ai kuwa ammi da kanta ta shirya juwairiya tsab,khaleed da haruna ne zasuyi musu rakiya zuwa can din..
*Masarautar kanon dabo...*
"Da yamma suka shigo masarautar..
sarki abu-turab na can fada waziri yaje ya sanar masa da zuwan su..
Yayi mamaki mutuka dan a ganin sa mai martaba yayi tsofan da zai ringa damun kansa da zuwa kawo musu ziyara..ko lafiya?
"Sashen Gimbiya amina suka yarda zango...
Amina tunda taga juwairiya taji gabanta ya fadi..
Ta kalli ammi cike da tsananin mamaki ta nuna juwairiya..
Ammi tayi dariya tace,kwarai diyarki ce amina..
Amina kuka ne ya zo mata,taje ta rungume juwairiya cike da kaunar diyar yar uwarta ta..
Juwairiya tayi kasake tana jin wani iri wai itace yau matar sarki kamar amina take runguma haka,kuma wai yayar mahaifiyar tace...
Khaleed ne ya leko dakin yace,ku fito zuwa falo ga sarki abu-turab ya shigo..
Juwairiya taji gabanta ya fadi..
Hannun amina taji acikin nata..
Tayi saurin kallonta..amina ta sakar mata da murmushi kafin tace muje kiga babanki..
"Juwairiya na saka kafa acikin falon ta hango shi a zaune