Showing 75001 words to 78000 words out of 96510 words

Chapter 26 - Jin Dadi Sabo Book 1 Hausa Novel Complete

19 Jan 2025

248

happy, Honey Sometimes I wonder if love is worth fighting for. Then I look at you. I'm ready for war.
tana karantawa itama ta tura Masa again:
Wow When you need someone to be there for you, I'll be right there by your side always! I love u My Hero, haka suka dinga chat iri iri ko wannensu na jin nishadi har sukayi sallama ta koma class.,Ahleef Yana ganin yafi ko wanne Namiji sa'ar samun mace itama Haka take gani tafi ko wacce mace dacen miji.

Shukura yau har tayi kawa Fatima me hankali da Nutsuwa,ga ilmi gata Yar gayu wayayya kyakyawa light chocolate tana da kyau ba laifi, itama sabuwar kawowa ce, tayi mamaki da taji Yar Shukura tana da aure kuma mijinta Bata taba ganin Dan gayu me kyau kamarsa ba Tunda take a duniya sai yau data ga ya kawo Shukura har class.
Shukura Bata kula kowa sai yanzu data yarda da nutsuwar Fatima, yau Latifa takaici bai Bari ko break ta fito ba Dan kar ma taga yanda Shukura tayi kyau.

Mutanen Unguwa da Wanda suka San Ahleef suka samu labarin abinda Momee tayi sun jajanta lamarin sai zagi Momee take Sha wasu Kuma Yan bakin ciki Allah ya Kara sukewa Ahleef, wasu Matasa masu Zama a Majalisa suna Hira sai gulma sukeyi ta gida gida har suka Fado kan Ahleef ai gwara ma da aka kwace,uban iyayi yanzu zamuga Dame zaiyi gadara,shi a Dole me kudi, wani cikinsu yace baku da labari ai kunya ta koreshi daga unguwa ko motar Hawa ta gagareshi duk an kwace,Wani makaryaci ya Kara da ai har kayan sawarsa Suka karbe ko gajeren wando basu bar Masa ba,mace ta raine ka tun kana yaro Amma ka zageta har kana ikararin Marinta,wani yace haba abin har ya Kai Haka? Tab ai labari sai Wanda kaji, wani Kuma yace gaskiya Ni yanda naji labarin Momee ce da laifi ta takurawa rayuwarsa, ku daina daukan jita jita da zance ya shiga gari sai kaji ya koma iri iri,gaskiya nima yanda naji Wacce ta raineshi ce me laifi Amma shi ai mutumin kirki ne Amma gaskiya zatayi halinta ai.

Momee zaune Cikin katafaren Palon ta cikin shiga ta alfarma,Hannunta rike da waya tana latsawa kana ta Kara a kunnenta alamar Kira tayi,Ana dagawa tace Excellency Naga kiranka, jam'iya ta Baki Babban mukami ki Duba News yau da dare Zaki ji,sannan kwanan Nan Zan Baki Babban mukami a state Dina,Murna Momee ta shiga yi,Yanzu zata yi suna a duniya itama ta Kara shiga sahun manyan kasar nan, sai bukawa frnds nata waya take tana sanar musu a tayata murna ta Zama Woman Leader ta jam'iya ta kasa Baki daya,Niima da Latifa sai Murna,Sultan su basu yi murna ba Sam da suka ji labari sai haushi ma da suka ji.

Niima da Mubaraq sai abinda ya Kara gaba tayi tayi ya aure ta sai yace ta jira tukun sai ta Gama koyar style iri iri na sex sai asha biki ita kuma Bata ganewa kullum suna Manne suna aikata Zina ba ruwansu daular kudi na eban su an mutu an bar musu dukiya sai hauka,da yawa Mutane suna Haka idan sun samu kudin gado sai a lalace Kuma Hajiya ta Zama tantiriya Yara Kuma suna Abubuwa Marasa kyau,Allah yasa mu Dace kudi su daina rudarmu suna halakar damu.

Tunda Mubaraq ya karbi dukiyar Ahleef da Momee ta damka Masa shike Nan su Hafcy gaba daya suka dauke kafarsu da zuwa gidan wata Momee,Mubaraq ma yanzu ya Dan fara rage haduwa da Niima sai tayi ta nemansa da kyar yake samu yace tazo su hadu a gidansa inda a Nan zai Kara lallaba ta ya kwashi gara,maganin Hana daukan ciki kuwa dankararsu kawai takeyi sabo da Mubaraq yace sam baya Jin dadin xxx idan yasa Condom.

2pm aka tashi su Shukura daga schl, sun fito suna Hira Fatima kawar Shukura ta kalleta sosai tace sai Naga kamar kina tafiya wani iri kamar Yar koyo ko rauni kika ji a kafar, Murmushin karfin Hali Shukura tayi sannan tace bugewa nayi a gwiwa ta sosai,Latifa sai Harara take zubawa Shukura ganin tana ci gaba.
Fitowarsu kenan sai ga Ahleef yasha Boyal dark Brown yasha kyau har ya gaji Shukura tana ganin motar Ahleef tace Fatima Mijina yazo dauka ta sai gobe na tafi,Fatima itama driver dinsu ne yazo ta shiga motarsu suka tafi tana dagawa Shukura Hannu.

Ahleef Yana daga cikin mota mazaunin Driver Shukura ta bude Bayan mota ta jefa Jakarta ta dawo gaba ta bude tare da shiga cikin motar bakinta dauke da sallama,amsa Mata yayi kawai ba fara'a a fuskarsa,Shukura ta kalleshi taga kamar Yana cikin damuwa,ko me ya faru dashi oho, tunda ta shiga mota taga Yana tunani ko motar ya kasa matsawa bare su tafi gida, a hankali ta kamo hannunsa tare da furta lfy Sweet heart? a hankali ya kalleta ya Dan saki Murmushi sannan yaja Motar suka tafi,suna kan hanyarsu taji muryarsa yace ya jikin? Kallonsa kawai tayi tace da sauki amma Me yake damunka? Kamar kana cikin damuwa, yace hmm Honey Dad din Farhan ne ya Bata Mana Rai Ni da Farhan,anjima zamuyi maganar. Sai hakuri cewar Shukura.

Bayan sun koma gida Umma tuni ta Gama komai da komai gidan a gyare tsab Yana kamshi abinci ma du tayi ta Gama, Umma tace Sannu da zuwa suka Amsa suna gaida Umma suka wuce Bedroom, tare sukayi wanka tare da shiryawa sannan suka fito Dining, Shukura tace Umma Ina Baba? ya fita wurin abokansa tsofaffi irinsu can unguwar su Hafcy inda mukayi aiki da,Baba Yana son zuwa wurin mutanan Nan,Ai an Saba ne da juna can cewar Umma, Ahleef yace Haka ne,Shukura ce ta zuba Musu abinda suke so a plate daya suke ci tare,lemo ma a cup daya suka zuba suna Sha cike da shauki,Umma tana kitchen tana aiki.

10pm Sunyi Shirin bacci suna saman Bed Ahleef Yana rungume da Shukuransa Yana shafa gashinta,Shukura cike da Shagwaba da shauki tace My Hero baka bani labari ba me Dad din Farhan yayi muku? Hmm Honey Wai Munje yace zai bani jari Amma karki ga fadan daya shiga yi min wai na tabbatar na biyashi kudinsa Nan da 1yr dama mu Yara mun Saba barnatar da kudi maganganu iri iri banji dadin kalamansa ba,yanzu har Ni zai fadawa tattali,ko iya Business sabo da zai bani rancen kudi kafin na biyashi sabo da yanzu yaga bani da shi.
Kirjinsa Shukura take shafawa a hankali tace Kayi hakuri Haka rayuwa take,ka daina damuwa kaji mijina ai Dad dinku ne,idan Kuma kaga da matsala ka bar Masa kudinsa kawai Allah ya baka naka, Honey harfa da cewa Wai idan kudinsa ya salwanta sai ya daure Ni har Farhan zai daure yace, Shukura tace to bar Masa kudinsa kawai Amma muyi Shawara da Baba ko Umma muji me zasuce, Allah ya kaimu gobe sai na sanar musu muji cewar Ahleef, Zancen su ne ya canja salo zuwa na soyayya Nan suka shiga farantawa juna Rai ba tare da yayi Xxx ba sabo da Shukuransa Bata warke ba.














AsmaBaffa



Ayi min afwa fans bana baku kullum Busy nake tnx all😍😍😍.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO






66-70







Official







By
AsmaBaffa









Washe gari da safe sabo da makaranta da wuri Shukura ta fada kitchen zata fara girki kenan Umma ta isketa suka gaisa,Umma tace kiyi iya cikinki da safe Kinga mu bama karyawa da Sassafe ke Kuma ga makaranta,Murmushi Shukura tayi tare da cewa to Umma ba matsala,Nan Shukura ta hada chips and Egg sai tea,tana Gama ci ta Shiga wanka,Bayan ta fito ta tashi Ahleef ya kaita schl, da sauri ya shirya suka yiwa Baba da Umma sallama suka wuce.

Bayan Ahleef ya dawo ya samu Umma da Baba ya sanar musu yanda sukayi da Dad din Farhan,Umma tace Shawara daya karka karba kawai bar Masa kudinsa,Baba ma yace hakane kawai kace ya barshi ka samu wasu sun Isheka,Farhan yace to sannan ya mike ya koma Bedroom dinsu kawai yaji gidan ya Masa zafi ba Shukura tunaninta ya addabe shi,ita kawai yake son gani suyi Hira, wanka yayi ya shirya tare da Fita ko karyawa bai yi ba,Umma tace yaci yace a koshe yake,Take away ya tsaya yayi na lafiyayyen Fried rice and chicken tare da Drinks ya wuce Schl din su Shukura yaga an kusa yi musu Break ma.

Yana zuwa lokacin sun fito Break tare da Fatima Kawarta suna Hira Shukura ta hango kamar Motar Ahleef, laa Fatima Kinga Mijina yazo nasan ma shine Maybe abinci ya kawo min,Murmushi Fatima tayi tare da cewa Lallai Yana ji dake,Fari Shukura tayi da Ido kana tace sosai yake Sona nima Ina mugun kaunar abina,Kirji ta dafe tana Allah sarki Dan Mijina muje na ganshi naji sanyi sanyi a Raina,Dariya Fatima tayi tace sai dai kije ke kadai Ni bazan je ba kunyarsa nake ji,Naga baya dariya ga kowa sai ke kadai yake yima,inje ya min kallon Tara saura quarter, ke kika sani cewar Shukura ta bar Fatima tsaye ta wuce wurin Mijinta.

A hankali take takunta cikin nutsuwa har takarasa tare da bude gaban motar ta Shiga tana dauke da sallama a bakinta, amsa Mata yayi sannan yace ya karatu?Yana Mai sakar Mata Murmushinsa Wanda ke Kara Masa kyau, Alhmdllh ta furta tare da cewa My Hero abinci ka kawo min? Dariya yayi sarkin Kwadayi ba abinda na kawo,Cike da Shagwaba ta kwabe fuska kamar zatayi kuka to kaje Ka siyo min Mana yanzu idan kana da kudi,Wai naga kamar bakayi Breakfast ba Baby? Ledar take away ya Mika Mata, ta karba cike da murna tana godiya,daya ledar ya dago Mata Kinga nawa,Murmushi ta saki tam Sweetheart ka cika cikinka dam idan na dawo Naga kaci kadan dure zan maka, dariya yayi kadan kana ya rungumeta tare da kissing din lips nata ya Mata sallama ta koma ajinsu shi kuma ya tafi,tare da Fatima suka ci abincin tas suka Sha ruwansu da lemo sannan suka koma aji, Ana tashinsu lokacin Ahleef suna tare da Farhan neman Mafita, ya Duba agogon hannunsa zumbur ya mike yace an tashi Su Honey zan dakko ta a schl,Farhan ya bude Baki sannan yace ka bari nasa Driver na ya dakko maka ita sai mu Gama maganar mu,A',a ni ban yarda ba da kaina zan dakko ta,Driver yayi min gudun ganganci da matata ba zai yuwu ba da kaina zan dakko ta,Dariya Farhan yayi yace Allah kiyaye hanya da yamma nazo gidan,Ahleef yace Allah ya kaimu yayi gaba.
Yana zuwa Already Shukura tana bakin gate tana jiransa, aiko ya dauko abarsa.

Yamma Liss Farhan yazo suna tare da Ahleef suna tattauna ya za ayi Ahleef ya samu Jari masu yawa,Farhan Yace Man kyale kudin Dad kar ya hanamu sakewa sabo da Dad shima akwai son Kudi, Gidana Na Lagos Dana Gina kasan yanzu zai kar Million dari kawai a siyar dashi kaci gaba da harkokinka,Ahleef yace no idan anyi Haka ai baka da kadarar da ta Kai wannan kudi ai kuma na takuraka,Masifa Farhan ya Shiga yi kamar zai tashi sama,To kudin Dana yi waye yamin silar samunsu idan ba Kai ba,Ni jarin nawa ka bani har na Zama abinda na Zama,Ko Dad bai min abinda kayi min ba a duniya duk abinda na Samu ta silarka ne Sannan yanzu Dan na baka Abu shine zaka min iyayi,Ni duk abinda na mallaka wlh zan iya mallaka maka shi Amma kana Fuck up,Ahleef zaiyi magana Farhan ya mike a fusace zai fita dai dai lokacin Shukura ta shigo dauke da tire na kayan Sha Dana ci, tace ah Ina zaka je Haka Kuma? Murmushi Farhan yayi mijinki ya Bata min Rai.

Murmushi Shukura tayi tace Dan kace Zaka bashi jari ko? Ya fada min jiya nace ya karba Amma karka saurareshi ka kawo kudin Ni zan karba Kuma Dole ya karba,ko ka tura min a accnt Dina zanyi maganinsa Ni da kaina,Dariya sukayi gaba daya Har Ahleef yanda Shukura tayi maganar kamar Babarsa, Farhan ya koma ya zauna tare da cewa to kaji abinda tace Mijin tace, Ahleef Yana dariya yace Totally Surrender abinda yace an Gama Yana dagawa Shukura gira daya,ta ajiye abincin ta zuba ta mikawa Ahleef nasa tace Gwauro Kuma ya zubawa kansa,Farhan yace na kusa daina zuwa gidan Nan tunda Ware Ni akeyi Ana min Gori.
Shukura tana Murmushi ta bar dakin suna ta hirarsu akan Business din da Ahleef zaiyi da kudin Farhan daya bashi.

Bayan wata daya kudin su Momi Sunyi kasa sosai ga Business baya tafiya kudi sai Bata sukeyi basa gaba,Mubaraq ya Gama tatike su kullum baya kasar Momee so take ma ta ganshi ta tambayeshi ya kudi suke Bata da Masifar yawa Haka,Amma Mubaraq Sam yaki yarda ma su San inda yake,Idan Niima ta tambayi Hafcy ko Mamansu basa fada sai suce su Basu San ma Mubaraq Yana juya musu kudi ba,Basu San inda yake ba,kudi Kuma da kadarori sai Bata suke wasu kadarorin ma suna tambaya za ace ai tuni an siyar da su.

Niima kuma sai cuta takeyi Ga Amai da tofar da yawu,Momee ta kaita asibiti aka ce ciki gareta har na 3mnths,Momee kuka sosai takeyi,Ga Latifa kullum sai Shan kwayoyi da giya tana club kullum, Women Leader ma da aka bawa Momee tuni an Kai sukar cewar ba Yar siyasa bace sabo da Haka Dole sai labari taji an tsigeta an Sa Yar siyasa.

Momee duniya ta fara Mata zafi musamman idan ta kalli Niima da Latifa sai ta zubar da Hawaye,A waya ta Kira Sultan da Suhail ta sanar musu halin da suke ciki,Sultan yace Momee lokacin da muka fada muku maganar gaskiya laifinmu ma kika gani,gashi yanzu kin Kai yaran wasu an lalata su,Kinga Dole ayiwa naki yaran,Haka Matar ya Ahleef kika Mata kazafi yanzu Kuma gashi Dole kina daukan karatun Duniya,dama idan baka ji nasihar mutane ba to duniya da kanta zata yi maka Kuma Dole ka ji nata, Momee tana Hawaye tace Ni dai kuzo a San yanda za ayi da Niima,Sultan yace wlh ba ruwanmu Kuna zubar da ciki kunyi kisan Kai again,Kuma kika Bata da danginki kaf Momee Akan abin duniya dare daya kika canja hali.

Visa Momee tayi ta nufi USA da niyyar ta karbe kudi da kadarar da Abba ya barwa Ahleef kyauta.
Tana zuwa mutumin yace bazai bayar ba sabo da Amana Abba ya bashi yace Kar ya bawa kowa kudin sai Ahleef yazo da kansa,Kuma da court din us akayi komai,tana takura Masa zaisa a daure ta,ba shiri Momee ta dawo gida ta dauki Niima zuwa asibiti Wai a cire ciki, Bayan aune aune aka gano Niima ta Gama kashe mahaifarta da Shan kwayoyin Hana daukan ciki,sabo da Haka ciki bazai zubu ba,idan aka cire to zata rasa ranta dolensu suka dawo gida suka ci gaba da rayuwa Kullum Kuma kadara da kudi suna karewa,Momee da kyar ta lallaba ta kwashe wasu kudaden masu yawa ta canja account sannan kadarar da ba a siyar ba ta siyar ta hada kan kudin kaf ta ajiye a accnt.

Ahleef Bayan kwana Hudu ya Gama dagawa Shukura kafa,kamar kullum yau da dare ya dawo gida,Shukura tana kwance a jikinsa suna kallo.
Wani mayen kallo yake binta da shi,Shukura ta tsorata gaba daya,a wayance tace Bari naje wajen Umma na karbo sako, Ahleef ya kalleta tare da cewa da Daren Nan? Wanne dare Kuma just 9:30 kace dare yayi,yanzu zan dawo pls ba musu yace alright da kansa ya mikar da ita tsaye tasa hijab tayi waje tana fita ta tsaya a Palo tana sauke numfashin tsoro tare da dafe kirji Wanda ke bugawa sabo da tsoro Tasha wahala first night yanzu Kuma taga take taken Ahleef.

Ta Dade a tsaye taki komawa sai ga Umma ta fito da niyyar zuwa kitchen zata hadawa Baba tea, Shukura tana ganinta ta buya Amma Umma ta rigada ta ganta,Muryar Umma kawai taji tace lfy ke Kuma? Dole ta fito fili tana Ina..Ina...dama..uhmm...kitchen zanje zan dafa Indomie ....au tea zan hada, Murmushi kawai Umma tayi tace to dama Nima Babanku zan hadawa zo sai na dafa daku,Shukura ba shiri tabi Bayan Umma har kitchen.
Fridge Umma ta bude ta dauko wani tsumi na mata tace ungo shanye yanzu,Shukura ta kalli abin tace Umma du kalli fa da yawa,ban son surutu na gyaran jiki ne ki shanye ki bani rubber ta,Shukura ta daga Kai ta kwankwade shi ta mikawa Umma robar, kafin Umma ta Gama dafa tea tuni magani ya fara aiki,Shukura duk taji ta Zama wet ga wata Yar Shaawa na kamata kadan taji ba Wanda take bukata sai Ahleef, ta rasa dalili,so take ma tayi sauri ta koma room dinsu,Umma na Gama dafa tea Shukura ta karba tace sai da safe Umma, to kin manta sugar din cewar Umma,da sauri ta dauki Sugar tayi gaba,Umma tace Spoon fa Baki dauka ba Wai meke damunki ne,da sauri ta Kara dawowa bula bula da Hijab dinta ta dauki spoon,Umma tace cups fa? Nan ma ba magana ta sura tayi gaba abinta.

Ahleef kuwa ya gaji da jira har ya mike zai je ya daukota sai yaga ta banko kofa bata kulashi ba tace ga tea Nan Bari nayi wanka,ta fada toilet tayi wanka da brush,tana fitowa ta shirya tana zuba kamshi cikin kayan bacci masu daukan hankali,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login