Showing 6001 words to 9000 words out of 96510 words

Chapter 3 - Jin Dadi Sabo Book 1 Hausa Novel Complete

19 Jan 2025

225

Madina Baffa ta furta tare da fadawa gado tana shan AC.
Shukura ta fara shagwaba wanka Inna Baffa wanka zanyi,Haka suka rude suna lallashinta kowa ya shiga yayi wanka tare da Sallah.

Baffa yace to Alhmdllh amma baza muci abincin nan ba yayi tsada, Karaf Shukura tace ni kosai zanci da doya da kwai, Inna tace a siyomin Biredi da fanke me sugar.
Baffa ya fita ya siyo musu shi Kuma ya siyo gurasa da kuli, Bayan sunci sun koshi sai suka bazama kallon gari,wannan haske kamar a Makkah Cewar Inna,sai cikin dare suka koma masaukinsu,Inna da Baffa a kasa sukayi shimfida,Shukura kuma ita kadai a saman Bed sabo da gata.

washe gari Baffa yaje inda zai ga mutanen da zai gani dama shine dalilin zuwansa kano,Bayan ya dawo suka kuma bazama cikin gari yawo sune har countryMall,Shukura taga kofa wacce ake turawa ta Glass sai ta fara knocking Kwan... Kwan... Salamuakaikum a bude,ku bude min,a bude.sai da Ma'aikatan suka zo suka bude Mata,bayan sun gama yawonsu kaf tare da siyayya sai kawai Baffa ya Manta sunan Hotel da Address,suna ta shan wahala a cikin napep sai Baffa yace Shukura Dan ubanki baki rike Sunan ba?ke da kike yar Boko, Inna tace wlh kuwa kai mun gaji,baki Shukura ta turo yo Kai Baffa ni ina zan sani,kaine fa ka kawo mu,me Napep yace ya gaji shi tafiya zaiyi,nan ya saukesu ya kara gaba,Su Baffa dai bakinsu Kamar zai cire sabo da tambayar Hotel, Shukura ta zabura ta tare wani me Taxi yana tsayawa tace Dan Allah tambaya nake,yace ina ji,dan Allah malam kasan wani Otel me kyau jikinsa duk fulawoyi? Da bene sannan ga kamshi,yana ta kyalli...shuru tsagal Inna tace yaro da Kwan lantarki a ciki,harda Tv,Me taxi ya fara dariya ya gansu daga daji suke yayi mamaki ma da suke zancen Hotel shi bai gane ba yayi tafiyarsa.

Su Baffa sai a gindin wata bishiya suka kwana, Gari na wayewa sai Baffa ya tuna Sunan Hotel din,nan suka shiga Napep suka Koma suna zuwa sukayi wanka suka shirya suka fito da kayansu sai Tasha, Suka shiga mota sai kauyensu suna ta murna sunzo birni sunga Gari cikin mota sai ciye ciye suke.Shukura ta damu mutane da surutu har suka isa kauyensu lfy.

Kwance yake saman cinyar Momee shima Ahleef kusan irin Shukura ne yana son sa wani aiki yana kwance yana hutawa amma shi sai dai kannensa ba Manya ko iyayensa ba, in banda tunanin masoyiyarsa Niima ba abinda yakeyi son da yakewa Niima ko rabinsa Niima bata son Ahleef haka,sabo da shakuwa da kyau ga kudi shine yasa take son Ahleef sosai ba wai tayi zurfi bane, Shi kuwa Bashi da wacce ta fita a duniya.
Niima ce ta shigo daga aiki ta Dawo ido suka hada da Ahleef masoyinta ya kashe mata ido daya tare da furta sannu kamar bazaiyi magana ba,hannu ta daga masa tana zuba masa murmushinta me tafiya da zuciyarsa,sai kallonsa takeyi a ranta Tana jinjina kyau,kyan diri da kyan sura irin na Ahleef,a ranta ta ayyana dadin da zaiyi on bed take duk da cewa bata taba bin maza ba amma Tana kwadayin Ahleef wanda shi kuwa Son Niima yake tsakani da Allah ba Dan komai nata ba.
Muryarsa taji a nutse yace 5pm ki shirya zaki rakani gidan su Farhan,ok tace Tana fari da ido.
Misalin 5 na yamma taci uban wanka kamar a saceta cikin wani lace maroon color,
Hannunsa ta rike yasha azabar kyau kamar wankin engine haka yake tafiyarsa kamar wani Gomna,hannunsu rike cike da so kamar a sace su,Bayan sunje gidansu Farhan yawo suka wuce na shakatawa,Suna zaune suna shan Ice-cream sai ga wani frnd dinsa yazo zai wuce nan Ahleef ya Mike ya tafi wajensa suna tafawa suna Hira,Niima tana latsa waya sai ga motocin Gomna zuga guda sun shigo da Alama Meeting suka zo yi Abuja,Niima ta gigice kamar bakuwar kudi bayan gidansu ma sunfi Gomna kudi, sai gyara Riga takeyi tana karairaya,Ido hudu sukayi da Gomna tare da Manyan masu kudi da suke kusa da Gomna,tasan Gomna ne amma bata San Gomnan wanne state bane,Gomna shima yaga me Kyau yawunsa ya tsinke,ba bata lokaci yayiwa yaronsa magana,sai gashi Cikin Guard wani ya kawo mata card na Gomna yace gashi Inji me Girma Gomnan Taraba State Exelency Muhammad Aliyos,fit Niima ta cafke Card tare da jefawa a jaka tare da furta tnx, guard da sauri ya koma cikin tawagar Gomna,Niima kuwa wani Farin ciki da girman kai ne ya mamayeta lallai ta cika me kyau da farin jini har Gomna guda binta sukeyi, tace ahaf har wani kudi ne damu,ai kudin yan siyasa sune kudi kullum shigowa suke ta ko ina kamar banza,duk da Babana shima yana siyasa ai ba kamar Gomna ba kai zan yashi dollars fa zanyi abinda naga dama,tana wannan maganganun zucin kawai Ahleef ya dawo cikin takunsa ko ina ka duba kallonsa akeyi maza da mata,ita Kanta Niima a ranta tace Allah ya zuba baiwa a nan.
Ahleef kashe mata ido daya yayi yana murmushi sai wani lallaba ta yake yana mata shagwaba sai ta fara biye masa sai ta tuno samarinta yan siyasa masu kudi ciki harda Gomna Aliyos.













AsmaBaffa
[7/22, 1:09 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO







3








Official










By
AsmaBaffa









Naku ne Fans na ko ina.











Hannun Niima ya kamo yana kare mata kallo,wani yarr taji a jikinta shima haka a hankali yace I love u Niima dan Allah ki rikeni amana karki barni duk da nasan bani da wani Asali iyayenku sune gata na dan Allah karki kyaleni ki taimaka min ta wannan hanyar kadai zan iya sakawa da Momee da alkhairi tare da Abba shine na aureki ina matukar Sonki Niima,hankalin Niima ne ya Tashi gaskiya ita yanzu bata son auren nan idan tayi aure shike nan Namiji daya tal zata dinga kulawa mijinta,ba samari duk masu kudin nan baza ta kula kowa ba, a hankali tace ina sonka nima ai baka da matsala Dani,Murna ta kamashi yace yanzu dai na fadawa Abba a sa mana Rana ko? Uhm Kawai tace tana wasi wasi a ranta,sai kallonsa takeyi kamar mayya ,Kalli mijinki da kyau Babyna,kunya ce ta kamata ta mike tsaye tare da cewa tashi mu tafi Hearty.
Soyayya sosai take nunawa Ahleef bata nuna masa akwai matsala,shi kuma ya gama sakin jiki da ita sai kashe mata kudi yakeyi sosai,so iya so tare da kulawa yake nuna mata,ita kuwa bata wani caring dinsa amma tana nuna tana sonsa,sai wahala yake a kanta,Har Abba ya dawo sukayi shawara da Momee suka yanke hukunci,nan Abba ya nemo danginsa Maza da mata,tare dana Momee suka yanke ranar aure nan da 4mnths,Wasu a dangi suna ta gulma za a aurawa Niima Marar asali Dan gidan raino dan tsuntuwa,Niima munafuka a gaban dangi sai ta zauna tare dasu a dasa gulmar Ahleef da ita, tace sam ita bata sonsa Abba da Momee ne suke so nanfa Zance ya zaga dangi ai auren dole za ayi mata Ahleef kadai ke sonta sabo da yaci dukiyarsu sabo da yasan bashi da gado,Haka Niima tabi itama kawayenta tana fada musu sai tsinewa Ahleef akeyi shi kuma bawan Allah bai san komai ba murna kawai yakeyi kamar me, Momee da Abba ma murna Sukeyi Sosai.

Shukura zaune take gefen Inna dake dama fura,Shukura tace Inna Sosa min bayana,Inna ta jawota tare da kwantar da ita a cinyarta kamar jaririya ta fara sosa mata baya,ita kuma tana Inna nan nan,Tana kwance tace Inna miko min Plate din can na cinye awarata,Inna ta dauko mata,sai da ta cinye sannan tace Bari nayi wanki Inna, Inna tace wanki? A'a kwanta ki huta zan wanke miki su,Shukura tace Allah bar min ke Inna, Tana kwance Inna taje ta wanke mata kaya tas, da yamma Inna na aikin tuwo Shukura tace kawo nayi miki tankade Inna, a'a Shukura zaki bata kayanki zauna ki Huta abinki,Shukura kuwa ta fice yawonta cikin kauyen.
Tun safe Shukura yau da period ta tashi tana shan wahalar ciwon Mara Dama idan tanayi Sai kuka takeyi harda shagwaba ma abin nata,Inna kuwa harda kuka tana tausayin yarta,Baffa kam yau ko kiwon shanu bai fita ba sha lele ba lfy,sun rufu a kanta sai addua suke mata har ta samu bacci ya kwasheta,da yamma kuwa ta tashi sosai taji sauki har ta fito Tana wanke kayan da Jinin ya bata tare da panties dinta,bayan ta wanke tace Inna...zo ki karba ki shanya minsu,da sauri ta karba ta shanya mata Kuwa,Baffa ne ya shigo da sauri ya manta ma da wata Sallama so yake yaji jikin Shukuransa.

Shukura tana so ta fadawa Baffa Pad dinta ta kare dama ita take zuwa cikin gari can jikin wani asibiti ta siyo abarta Sabo da kauye ma basu wani santa sosai ba Da tsumma suke kunzugu,sai tace Baffa kaje bakin asibiti kace a baka Biredin mata,Baffa ya washe baki ahh lallai sauki ya samu Shukurere ta har Biredi zaki ci,wanne kala?,murmushi Shukura tayi tace Baffa a bakin asibitin Ishu kawai ake samo shi,kace biredin mata zasu baka haka ake fada a kauyen,Baffa harda tuntube wajen sauri yana zuwa kuwa yace a bashi biredin Mata aka bashi ya biya kudin duk tunanin Baffa wani Bread ne Me dadi a ciki,ya kawo mata gashi Shukurere ta aci da yawa kinji tace to Baffa,yace wannan katon Bread ai sai da lemo Shukura, Inna tace kayi sauri ka siyo mata Maltina tunda tafi Sonta,nan ma jikin Baffa na rawa ya siyo mata Maltina me sanyi yace tasha da biredinta.
Sosai suke ji da Shukura gata sai wanda ta gani,kullum haka take a rayuwarta cikin gata da jin dadi sabo da haka kuma mutanen kauyen sai suka tsaneta sosai kowa burinsa ya zaiga Shukura ta tozarta ta wulakanta amma ba dama Allah ya riga ya bata masu hassada sai kallo.

Ahleef tare da Farhan suna garden sai shirye shiryen biki sukeyi sosai ganin saura 2mnths bikin sai matsowa yakeyi, Ahleef ya Kalli Farhan cike da iyayinsa da ya saba yace Man ina ganin Matsala a wajen Niima abin yana damuna,na tambayeta ko da matsala tace a'a,murmushi Farhan yayi shima da Iyayi yace kai dai tsoro Kake ji so yayi maka yawa,hmm baza ka gane ba sam ba caring yanzu wani shareni takeyi na rasa me nayi Mata gaisuwa ma yanzu sai taga dama,bata ma so mu hadu,kasan fa mata haka sukewa ango idan za ayi musu aure haushin angon suke ji,pls ka daina damuwa tunda har itace ta Amince idan bata sonka baza ta yarda ba, Kai wace ta isa taganka tace bata so ko baturiya yace ai tayi karya,Ahleef yayi murmushi yace haka Momee ma tace dana fada mata amma wlh kaji na rantse da matsala a wajen yarinyar nan sai dai kawai Addua.

suna zaune saiko ga Niima tazo tana tafka uban Selfie ita da kawayenta su biyu ta Kalli su Farhan shekeke tare da galla musu harara,sai suka matsa gefe kawayenta suna yaushe zamuje Government House dinne? Tace munyi waya execelency na yace Next wk yana nemana,sannan jibi Senator dina zaizo gida wajena ban San ya zanyi da wannan angon nawa ba, dariya yan matan sukayi tare da cewa ai ba a daura ba bare ya Hanaki kula wasu shegen angon naki sai shegen iyayi ga rainin hankali dan kawai yana da kyau da kudi, daya a ciki tace Niima Allah yayi Miki baiwa da miji kamar Ahleef amma kina so ki cuci bawan Allah,Niima ta turo baki tare da cewa ke kin san dai nima kyakyawa ce ga farin jini idan ma yatafi dubu zasu zo min mutimin da ba'a san asalinsa ba har wani kyansa za a gani,idan kuma kudi ne ga Manyan kusoshin Gomnati nan duk ina dasu kuma nima ina da kudin haka ubana Ma.
Su kansu kawayenta sunga haukar Niima tare da butulci.
Niima haka kullum burinta ta dinga gulmar Ahleef Tana aibatashi tana zaginsa cikin mutane har zancen ya Fara dawowa kunnen Momee amma tayi shuru taga gudun ruwan Niima yarta.
Shiko Ango kullum yabon Amaryarsa yakeyi sonta na karuwa a ransa kullum yana manne wajen Abba da Momee suna shawarar biki.
Kwanaki na ja biki saura 1wks ango ba zama Amarya kullum cikin bakin ciki take bata shirya aure ba za a tauye mata rayuwa,yanzu idan ta yarda da auren shike nan Alhazawanta sai mijinta kawai.

Shukura kwance take cikin dare Tana ta kwasar baccinta taji kamar hayaniya a hankali ta bude idonta ta kunna torchlight kenan taji ashar da zage zage,ai sai ta kashe torch ta leka ta window nan take ta hangame baki tare da fara Hawaye taga Baffanta da Innarta an dauresu ga wasu jibga jibgan arna sunkai su 15 dauke da bindigu,Baffa taga sun kafe da mari,da sauri ta bude kofa ta fito da gudu Tana kuka tana rokonsu su bar mata Baffanta itama mari suka zuba mata nan take ta sume sharaf a kasa Inna ta fasa Ihu sabo da rashin Imani wani yasa wuka yayi mata yankan rago,Baffa ya rafka salati tare da dafe zuciyarsa nan ya fadi matacce zuciyarsa ta buga.

Arnan dariya suka dinga Yi ta mugaye sannan suka kada shanu da dabbobin Baffa kaf suka tafi dasu,a garin basu kadai ba har sauran fulani da dama wasu an kashe su an tafi da dabbobinsu, Tunda Shukura ta suma bata farfado ba sai da gari yayi haske lokacin Mutane sun cika gidan taf,da kuka hade da salati ta farka Tana Ihun Baffa...Inna.... Wayyo...nan tayi arba da gawarwakin Inna da Baffa sai ta haukace gaba daya tana birgima da ihu tana na Shiga uku ina zan sa kaina na huta,gatana ya kare Inna... Baffa sambatu takeyi Kala kala sai da kowa ya tausaya mata harda masu kuka gaba daya ta haukace bata san inda kanta yake ba, har akayiwa Inna da Baffa sutura tare da kaisu makwancinsu ana ta zaman makoki,Shukura kuwa suman ta yafi sau goma tana farfadowa kamar zata sheka lahira,sai maza ne suka riketa aka shiga yi mata addua tare da Kiran Nasuru me Chemist yayi mata allurar bacci ya sa mata Drip nan bacci ya kwasheta,bata farka ba sai dare Ta dora daga inda ta tsaya ana mata nasiha amma abanza cewa take ni bazan Hakura ba, in Allah ya yarda kuma sai iyayenku sun mutu Allah yasa babanku da babarku su mutu suma,bazan ba kowa hakuri ba sabo da nima bazan hakura ba.

wata tsohuwa tukuf ta shigo gaisuwa gidan Shukura wacce ta gama rama sallolinta Tana kuka ta Kalli tsohuwar tace ai gwara da wannan ce ta mutu tunda ta tsufa bata da amfani mene amfaninki,wata ma cikin dangin Baffa na sallama tace ga wannan Ma shekara nawa kullum cuta takeyi ai da ita ta mutu,matar tace Allah sarki yar nan kowa na can ne lokaci nane baiyi ba.
Wasu yan mata su biyu sunzo gaisuwa Zaraf shukura tace ga Baban wannan Ma shanyashi ake a Rana sai an kwantar sai an tayar mene amfaninsa Ai ni wlh iyayena sunfi na kowa Amfani, ana mutuwa amma mutuwar su Baffa ta musamman ce..ba shiri Nasuru me Chemist yazo ya kara dannawa Shukura allurar bacci da Drip, bata farka ba sai washe gari,ba laifi ta dan dawo hankalinta amma sai taji masu zaman makoki dangin Baffa suna lissafa mutanen da arnan suka kashe a garin,nan Sai ko akaji Shukura ta kece da dariya tace Alhmdllh uban kowa ya mutu wlh tunda ubana ya mutu uwar kowa ta mutu tunda na rasa tawa,yanzu har Dantani Baban Aishalle ya mutu?kai Alhmdllh amma Allah na gode maka,yawwa gwara Kowa iyayensa su mutu duk mu zama daya,ai wlh bazan Kara jimamin mutuwa ba, Ni mutum ya sake yace min ubansa ko uwarsa ta rasu sai dai aga ina nishadi wlh.
Wani ne ya rafka sallama tare da cewa bayin Allah Ashe arnan Jos har rigar yan jalo suka je sunyi kashe kashe da yawa yafi na wannan kauyen namu,ayyiriri nanaye akaji Shukura tace yawwa su dandana suma suji Me naji.
Kwana uku kullum sai anyiwa Shukura Allurar bacci bata ci bata sha sai an mata Jan Ido har akayi Bakwai.

Kullum Shukura bata daina kuka tana Tuna iyayenta zata fashe da kuka,haka har aka kwashe 40days Dan abinda Baffa da Inna suka mallaka aka siyar gaba daya har gidan da Shukura ke ciki,dangin Baffa dama tunda akayi bakwai suka tafi da Shukura gidansu,haka aka raba gado yanda Allah yace aka bawa shukura kudi dubu Dari biyar kasancewar Kauye ne filaye da gonaki basa tsada,Shukura ba kunya ta karbe kudinta a ledar Viva tana kukan su Baffa.
nan ta samu Kudin nan ta Fara dagargazar dadi,ba irin shawarar da yan Uwa basu ba shukura ba yanda zatayi da kudinta ta Samu ci gaba amma tace a'a Sabo Da tun farko bata da mafadi sai abinda taga dama take yi ba a sata ba a hanata, gashi bata daukan ko tsinke a gidan dama sun San halinta ganin maraicin da take ciki suke daga mata kafa,ga shegen iyayi wajenta, kudinta ta sasu gaba tayi kyauta taci dadi,yauma da Yamma liss taga wani katon zabuwa Tana yawo tace nawa wannan Zanbon Goggo ko na uban waye zan siya a siyar min shi,Goggo ta tabe baki tare da cewa nawa ne kuma ni dubu biyu zan siyar,nan ta zaro 2k ta biya tasa yara suka Kama mata shi aka yanka Sabo da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login