Showing 18001 words to 21000 words out of 96510 words
gobe zai fadawa masu gyara gidan su kara gyara gidan,kudinsa ya duba ya gansu yanda suke ba a taba ba, shakira halayenta ba sata a ciki,ko nawa zata gani komai talaucinta baza ta dauki abinda ba nata ba bare kudi.
Bayan yayi shirin bacci sai ya fito zai duba gidansa tare da kashe Light lokacin Shukura ta shiga kitchen dinsa ta kwaso su Apple da sauran kayan Fruits tana wucewa shi kuma ya fito yaji kamar an rufe kofa da gudu yabi bayanta amma kafin ya kamata tuni ta boye shi kuma gani yakeyi kamar mutum kamar ya gani,a hankali yace lallai aljanu ne a gidan nan masu yawan gaske,amma akan na koma gida da zama gwara nayi rayuwa da Aljanu Sabo da Niima ta dawo gida yanzu,bazai iya canja gida ba Sabo da yafi son gidan da yake ciki, to ko Security camera zansa koma mene ai zan gani,to ai aljanu ne kuma ba a ganinsu idan kuma ya gansu zai tsorata,motsi yaji kamar an bigi wani karfe da sauri ya juya baya fara gudu gudu sauri sauri ya kulle kansa a Bedroom tare da kudundunewa cikin bargo yana addua iri iri har bacci ya kwashe shi,Shukura tana kallonsa tana ta dariya kasa kasa lallai wannan matsoraci ne na gaske.
Saudatu yau Alhajin da suke aiki a gidansa zaiyi baki zasuyi Meeting na business Ogansa me gidansa tare da Dansa zai kawo masa ziyara gidansa a nan zasuyi Meeting Sabo da Alhaji Dauda abokin Abba ne kuma suna Business da Ahleef yana ta musu mitar sunki zuwa gidansa,gaba daya gidan yan mata da samari tare da iyayen duk Sun rude Sun gigice sai kwalliya Suke zubawa kamar zasu je ganin sarki Sabo da Dan Abba yace yana sonsu,Mama Cewa take yawwa yan matana kuyi kyau sosai so nake Ahleef ya zabi daya a cikinku ya aureku burina ku auri me kudi irin babanku Wanda zai dinga kaini Makkah da kasashen turawa,wanda zai dinga siyo min super England ba wanda zai siya min Nichem ba,gidan da zaku huta gidan Naira,Ko Abban ne yace yana Son daya dole na bashi komai tsufansa,Yan mata suna dariya tare da cewa ai sai Mama Allah bar mana ke, Wani Saurayi zai kai shekarun Ahleef Mubaraq yace ni kaina da Abban yana da budurwa lallabawa zanyi nayi Auren jari da ita,Karaf Mama tace tana nan sunanta Niima har Company gareta ban San me yasa aka fasa aurenta da wani ba ban San kan lbr ba Amma tana nan batayi aure ba kaje kayi duk yanda zakayi ta soka dama gaka kyakyawa da kai duk yarana babu me kyanka,duk abinda suke fada Saudatu tana goge goge tana jinsu sai da gabanta ya fadi da taji an ambaci Ahleef me sunan jaririnta Amma tasan shekaru 31 ba wasa ba, tuni ta hakura tasan danta yan mafiya Sun yankashi tuni,Har so take a duniya ta ga waye wannan me sunan danta daya bace gashi sai rubibinsa akeyi Sabo da yana da kyau da kudi.aranta tace ai kuwa sai ta labe ta ga waye wannan baza tayi nisa ba.
tsawa taji wata budurwa ta buga mata me suna Hafsy,Hafsy itace budurwa Babba a gidan kuma tana da dan kyau kadan shi yasa Momee tace lallai ta makalewa Ahleef har ya aureta,gashi kuma duk gidan ita ke wulakanta Saudatu fiye da kowa, watarana har marin Saudatu ta taba yi, tafi kowa fitsara,daga ita sai Mubaraq a rashin mutunci,sai kanwarta Zahra sauran suma ba tarbiya amma mutum uku sune kan gaba, Mama kuwa itama haka take har Alhaji Dauda amma bai fiye wulakanci ba shi sai kadan kadan.Hafsy ce ta watsawa Saudatu Harara dalla malama wuce inda kika fito sai sa ido,Mama tace hmm kuma dai kwa fada suka sheke da dariya gaba daya,Saudatu ta riga ta saba kawai sai ta wuce abinta a ranta tace duniya ce, tazo zata wuce ta kofa Zahra ta bangajeta ta wuce abinta.
Yamma 5pm kowanne dake gidan yaci kwalliya yana jiran manyan baki suzo,Hafsy sai kwarkwasa akeyi,5:30pm motoci laba laba Sun kai 6 ne sukayi parking a cikin gidan,Yan mata fa ansha kyau,Guards ne suka fara Budewa Abba ya fito sai Salman da Suhail Sun dau wanka suna zuba Kamshi,Wata rantsatsiyar mota suka sake budewa sai ga Ahleef yaci uwar uban Wanka kamar baza a mutu ba,cikin manyan kaya farar Shadda kal tasha dinki fitted ta samarin Abuja, sai kyalli da sheki yakeyi,Yana uban taku kamar Sarki yana basarwa ga kyau kamar wankin Engine,kamshinsa duk ya cika gidan,yan mata sai leke suke ta Window,Hafsy tace wai...wai... Zahra na riga ki wannan me farar shaddar nake so,Zahra ta hayayyako da masifa wlh na rigaki shine nawa,ai wlh baki Isa ba,Babba sai babba,yaro kuwa na yaro ne, Jamila wacce suke kira Jamcy itama tace Ahleef take so suna leke ta window,Nan fa fada ya kaure a tsakaninsu sai da Mama ta raba su da kyar, Mama tace ku nuna min akan Wanda kuke fada naga kyan nasa da kuke fada,Zahra tace leka ki gani Mama gashi can da Farar Shadda tunda muke bamu taba ganin me kyau irinsa ba a duniya,Mama ta leka nan take ta hangame baki tare da cewa ina ma ana tariyo baya nima na dawo yarinya Akan wannan wlh sai nayi kisan kai,Dama sun San Mama akwai budurwar zuciya duk harkar charting baya wuceta,Mama ta wuce tace na tafi tarbar baki anjima kuzo ku gaisheshi.
Alhaji Dauda yana tare dasu a katafaren Palonsa suna ta Hira daga nan suka fada harkar Business,Mama ce itama ansha wanka taje suka gaisa taci kitson attach kamar arniya tana zaune a palon kusa da mijinta,bayan 30mt sai ga su Hafsy suna ta layin gaishesu suna karairaya,daga nan Mama tace suzo aci abinci,Ahleef kawai waya yake dannawa Ko kallo basu isheshi ba,babu wacce ya amsawa gaisuwa sai Mama kawai,su Salman kuwa harkar gabansu sukeyi suma,Jikin yan matan yayi sanyi amma basu hakura ba.
Bayan nan Ahaji Dauda yasa aka kawo musu abinci a nan Palon ba sai anje Dining ba,duk Sun zagaye ciki harda Zahra da Hafsy, Mubaraq yana ciki sai Mama da Jamcy.
Yan aiki aka bawa Umarnin kawo abinci ciki harda Saudatu sabo sunfi yarda da tsabtarta,Saudatu ta kawo katon Flask ta ajiye a saitin Ahleef cikin Nutsuwa tana Tsoro karta yi ba dai dai ba, tsaki Hafsy taja tare da cewa dan Allah madam ki ajiye ki tafi ke kullum baki San aikinki ba,Zahra ta kara Jan dogon tsaki uwar kinibibi tsohuwa dake,Mama maimakon tayi fada sai tace hmm Saudatu kenan Uwar Iya,Alhaji Dauda ne yace ku fa bakwa kyautawa Allah kyauta abinda yace kenan,Mubaraq ya shekawa Saudatu harara.
Abba dama shi ya dade da sanin gidan abokinsa ba tarbiya baiyi mamaki ba, yana Allah wadai da halayensu,Salman suma mamaki ya kamasu dattijuwa kamar wannan ana zaginta,Ahleef kam da sauri ya kalli matar da akayiwa tsaki dattijuwa sosai irin wannan ita kuwa ta bar aikin mana idan ba son kudi ba, ana zaginka kana zaune,Su Hafsy yaji ya kara tsanarsu yanzu sosai,Saudatu ya gani ta kawo wasu cups,Mama ta daka mata tsawa zubawa baki abinci mana,su duk ganinsu birgewa sukeyi su masu kudi.
Saudatu jiki na bari ta fara zubawa Su Abba,zata zubawa su Salman yace no na koshi ni,Suhail ma yace bazai ci ba ruwa zai sha kawai,Saudatu da fara'a ta kalli Ahleef tare da cewa kai fa Alhaji me za a zuba maka ? Ahleef ya kalleta aiko sai ya saki murmushi kamar ya santa yace Umma wanne kika dafa da hannunki ? Ta nuna masa kala uku harda Zobo Drink me dadi tace wannan nayi da kaina,yace zuba min su zan ci ni,Ita dai Saudatu sai tana ganin kamar ta San Ahleef amma ta kasa ganewa,Mama kuma da Su Hafsy sai kallon Ahleef sukeyi suna kallon Saudatu sai suka ga kamarsu daya har tayi yawa ma, komai nasu har hakoran kusan iri daya,Bayan ta zuba masa ya karba da kansa, har zata bar wajen Ahleef yace zauna mana Umma idan na gama sai mu tafi na jirasu a waje,Tsoro ya kama Saudatu tasan yau tata ta kare a gidan,tana zaune ya gama cin abincinta me shegen dadi sannan ya Mike Saudatu tabi bayansa suka fita har waje,yace Umma haka kuke rayuwa ke yar aiki ce ? Saudatu tace ae wlh rayuwa kenan,Ahleef yace ke da mijinki duk nan kuke aiki Saudatu tace ae a takaice ta bashi labarin irin zaman da suke a gidan,da wulakancin da suke fuskanta ita da mijinta,Ahleef ya tausaya musu yace watarana idan na samu time zan daukeki ki dinga dafa min abinci ina biyanki albashi Kin yarda? Murna ta kama Saudatu ta dinga godiya harda durkusawa har kasa,yace mijinki kuma sai na kaishi Office dina yana min goge goge ina biyansa,Zan baku wajen zama a gidana zan dawo na daukeki nan da 3wks.
Godiya kawai Saudatu keyi masa,yace haba Umma ki daina godiya haka ya zaro 10k ya Bata.
Abba ya fito tare da yan gidan suka rakasu suka tafi,Mama lokacin suka rufarwa Saudatu da balai da masifa iri iri suka ce gobe sai Sun bar musu gida,Asiri take wa bakinsu kowa yana sonta,tana mallake musu masu kudi,sai kace wata budurwa ita me zatayi da wasu maza masu kudi Saudatu ta furta a ranta, Babu hakurin da Bata basu ba har mijinta da suka sa masa dan dako Sam suka ce dole gobe su bar musu gida.
Tunda Shukura taga Ahleef ya bar gidan ta fito ta gyara gidan Neat har samansa yana ta kamshi ko ina ta canja tsarin gidan yayi Masifar kyau, tayi girkinta taci ta koshi ta dauki remote tana ta danne danne har Allah ya taimaketa ta kunna TV ta kamo tashar American film tana ta kallo har ta gaji ta mike ta shige bedroom din Ahleef toilet dinsa ta shiga tace dole na dana,ta fesa wankanta da kayan wankansa,ta fito ta shafa Body lotion dinsa,kayan gyara gashinsa da su ta gyara nata yana kamshi, Cikin sip dinsa ta bude ta duba cikin wankakkun shaddojinsa ta zabi wata ruwan toka ta dauki iya rigarsa wata yar fitted hannun links ne ta sa abarta shar tayi kyau kuwa,bata sa da wandon ba, turarensa iri iri ta fesa sannan ta kara gyara masa komai na dakin ta fito ta baje a palo tana kallon film tana shan lemo abinta,Ahleef har ya dawo Bata Sani ba, sai ji tayi ana kokarin bude kofa da gudu ta kashe TV ta arce inda ta saba buya,tun daga waje Ahleef ke Jin karar TV amma abin mamaki yana shugowa yaga TV a kashe,sai kwalin lemo,gashi shi yasan bai sa a gyara masa gida ba amma yaga gida sai kyalli yakeyi da sabon kamshi,tsoro ya kamashi ya haura sama yasha mamaki kalar gyaran dakin na musamman har Bedsheet an sake masa,Ya fito ya duba gidan kaf ko ina yasha gyara, ya tambayi security ko wani ya shigo ? Yace shi ba Wanda ya shigo,ya dawo ciki a fili yace wlh idan na kara ganin abin Tsoro guduwa zanyi na bar gidan.
Kwana uku tsakani kullum sai Shukura taje wajen da suke soya doya amma ba Saudatu ba labarinta,ta tambaya amma babu Wanda ya San inda Suke,har gidan Da Saudatu ke aiki taje amma akace an koresu daga aiki har kuka Shukura tayi sannan ta dawo gidan Ahleef taci Gaga da buyanta.
Yau Misalin 12 na dare Ahleef yana gida,Shukura ta sa rigar Shaddarsa wata Milk color Garin labe labenta ta daki wani karfen motsa jiki ta fadi Tim a kasa,kafarta ta dauje Jini yana fita,Kuka ta fashe dashi sosai ta manta Sam da za a kamata Bata kaunar ganin jini na fita sai ta fara kuka,kuka ta shiga rerawa,Ahleef Tsoro kamar ya sume,ya dauki katuwar kujerar Mirror yana lallabawa da niyyar duk Wanda ya gani ko aljanine fasa masa kai zaiyi,yana lallabawa a tsorace har ya bude kofar inda yake Jin kukan na fitowa a hankali ya Shiga,Yaga Gashin mace ai ba shiri ya jefar da kujera zai gudu regarsa ta makale a kujera ya fasa kara,Shukura kuka ya dauke dif tasan asirinta ya tonu shike nan korarta zaiyi kwanan kan titi ya ganta,Fuskarta ta dago suka hada ido da Ahleef yana kokarin guduwa rigarsa ta makale,Cak ya tsaya da yaga kamar yarinyar da suka kwanta a Hospital da Momee,kuma wacce ya gani sanye da Jallabiya irin tasa,tabbas itace ashe dama Kusan 2wks kenan tana gidansa ashe itace take sawa yana tunanin Aljanunee,wani bakin ciki ya kamashi,tana jira taji saukar duka sai taji cikin fushi yace Amma kin zalunceni kin cutar dani,all ths While ashe kece,why baza ki fada min ba ki rokeni na baki inda ya dace dake,hawaye ya kwararo mata na tsoro cikin rawar murya tace uhmm..tsoro...tsoro naji karka koreni wlh zan baka labarina ni marainiya ce,Hey...u better stop tht nonsense ina ruwana da maraicinki Who even care,Mikewa tayi ya kare mata kallo wato kayana ma kike sawa Sabo da kin rainani,ashe duk abincin nan kece kike cinyewa,shuru tayi ta wani turo lips Gaba,tace Allah baka hakuri, dan Allah kayi hakuri bari na bar ma gidanka,ta kwaso kayansa sunkai kala bakwai da take ta sawa tace ga kayanka,mamaki ya cikashi ashe barnar har ta kai haka ji yake kamar ya kasheta,rokonsa tayi dan Allah ka taima kamin da wajen kwana kafin na samu kudi,Kin San da haka me yasa baki rokeni ba tun wuri,har Ya juya zai tafi ya dawo yace sai kiyi ta zama Mayya,ya Leka lungun da take boyewa tana bacci yace hmmm tare da bude Bedroom din da take shiga toilet din ciki tana wanka yace ga daki nan kuma wlh kina min shirme sai kin bar gidan nan tunda bana ubanki bane,Murna ta kamata ashe haka yake da mutunci, bata taba zato ba gashi ya bata daki ma tsantsarere, kallonsa tayi baki a washe tace ashe mutunci ne da kai haka na gode,Allah yaji kan magabata,Allah kara budi da arziki ya biyama bukatunka na alkhairi yasa Aljanna makoma,Baki ya tabe tare da cewa yar Maula,Shuru tayi murna ta isheta Bata ma ta ciwon da taji tace ba dadewa zanyi ba ina samun wasu kudi zan bar ma gidan,ina sa rai da wasu kudade naji a jikina zanyi kudi kwanan nan sai na barma gidanka karka damu saura kadan.tsaki yaja yayi gaba abinsa yana cewa sai kinyi kudi ma zaki barmin gida? Ba rana kenan ya barta a wajen tana murna harda tsalle.
AsmaBaffa
[7/22, 1:12 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
7
Official
By
AsmaBaffa
ZAMA NA AMANA 2 FACEBOOK wannan page naku ne,na gode Allah ya bar kauna.
FLOWER jinjina gareki wajen Sharhi ba daga kafa tnx alot.
Fans bana son tnx fa Sharhi nake bukata ni.
Bedroom din daya Bata ta fada ciki tare da kwanciya saman Bed tana faman murna,yau ba wani tsoron Aljanu yayi bacci sosai shi kanshi washe gari yayi mamakin baccin daya kwasa ya nisa tare da cewa amma yarinyar nan ta cuceni wlh yaushe rabon da nayi bacci haka,ko gidansu zai maidata wajen Momee ina shi ina kwana gida daya daga shi sai budurwa ina bazai iya ba, wani tunani ne ya fado masa sai kuma yace no Momee zata kwasheta tace zata zauna a wajenta har abada shi kuma bai Son kwashe kwashe kawai ta gama kwanakinta ta bar masa gida shike nan,Saudatu ce ta fado masa a rai yace dama dawo dasu yayi gidan suka fara aikinsu kawai yace da yamma zai tura Driver ya dauko masa su.
Saudatu kuwa tunda aka koresu basu da wajen zama sai can karkashin gada suka koma suna kwana ita da Alhaji Amadu,ruwa,iska komai a kansu yake karewa suna Cikin yan cirani suna fadi tashi,Babu wurin kwana ina wata sana'a idan ma Sun bar gari to basu da wajen zuwa, Ahleef yana ranta Sabo da yace zai daukesu aiki dan haka Kullum Saudatu da mijinta sai sunzo kofar gidan Alhaji Dauda Sun yini Ko zasu ga Ahleef yazo daukansu,Saudatu da ta gaji da wahala Duk dauriyarta Yanzu kuka takeyi sosai wai su me yasa tuntuni rayuwarsu a wahala suke ne,yau ma suna nesa da gidan Alhaji Dauda ta tsuguna a kasa Bata San sanda ta fara hawaye ba, shi kuwa Alhj Amadu kusa da ita ya zauna yana tausaya wa kansu matarsa balarabiya talaucinsa yasa duk ta tsufa, da yasan hakane da bazai aure ta ba, tunda yasan talauci a jininsu yake gashi har yau ya jawowa masoyiyarsa ma, Lallashinta ya fara suka samu wurin inuwa suka zauna Kafadarsa ya miko mata tare da cewa kwanta Saudat ki huta,ita kuwa dama dake balarabiyace ko a jikinta ba ruwanta da mutane ta lafe a kafadar Alhj Amadunta.
Haka yauma suka karaci zamansu har dare ba Ahleef ba alamarsa suka hakura suka koma Karkashin gadarsu inda yan cirani ke taruwa su kwana mata da maza babu iya shegen da ba ayi a wajen sai dai ka sharesu kawai.
Yau da safe da wuri sai ga Shukura da shishigi har kitchen din Ahleef anan ta soya doyarta da kwai Irin yanda Saudatu keyi,ta dafa tea yasha kayan kamshi ta ajiye a Dining ta wuce dakinta domin yin Wanka, Ahleef ya fito cikin Shirinsa na fita Office yaga an shirya abu a Dining,budewa yayi yaga doya ta soya yanka biyar ta cikin mutum daya,wato kanta kadai ta Sani, sai ya zauna yasha tea dinsa tare da cinye doyar tata tas bai bar ko kwallo ba
Ya Mike ya koma Bedroom dinsa yana amfani da System Kafin ya fita,Shukura Ansa jallabiyar Ahleef Milk ta fito zata kwashi girki ta bude plate wayam ba komai,tace to ko shine ya cinye min? Bari naje na tambayeshi naji