Showing 48001 words to 51000 words out of 96510 words
Chapter 17 - Jin Dadi Sabo Book 1 Hausa Novel Complete
lallan,Kuka tayi sosai har aka tashesu Shukura aiki takeyi da suka Sata,Ahleef bai san ta tafi schl ba yazo suka gaisa da Umma da Baba anan yaji ta tafi schl, abin ya bata masa rai amma ya danne,taya za ace jiya a daura aure washe gari Amarya ta fita ita ba exam ba Bare ace dole,Mota kawai ya fada kamar zai tashi sama haka ya Isa makarantar.
Shukura sai shara da wanke toilet take faman yi tana kuka Sabo da ta gaji likis, idonta yayi jajir,kamar ance ta juyo sai taga motar Ahleef shima ya gane itace,tsintsiyar ta jefar ta nufo wurin Ahleef tana kuka,ba zato ta fada a kirjinsa tana Kuka wiwi hade shagwaba tace Yaya ta kara fashe masa da uka, hannuta ya kalla sai yaga lallen daya fiso har ya lalace,what ? Ya furta kana yace me ya samu lallen?labari ta bashi sannan tace sai da na fada maka ni bana son makarantar amma kaki yarda dani, Ahleef yaji haushin abinda aka yiwa Shukura,Office din pc ya nufa ya dinga masifa sannan yace schl zai canja mata daga yau.Shukura Murna kawai takeyi da sauri ta yi wurin motarsa yazo zai bude ya shiga,da sauri ta zagaya tare da bude masa tana cikin nishadi za a canja mata schl, murmushi ya saki wanda ke rikitawa yan mata tunani,Shukura tace sai ni matar me kudi wlh wa ya isa yaja Da ni ko lecturer ne dan ubansa,wlh Badan yar gidanku bace sai nayi sharia da ita a kotun koli,kotin daga ita sai Allah ya Isa.
Dariya ta kama Ahleef ,kai gani kake wasa nakeyi hmm,na tuna ma Yaya ana bina kudin lalle da wasu kaya dana siya,da hannu ya nuna mata inda yake ajiye kudi ta dauka ta vile 30k ta maida sauran, idan basu isheki ba kara,sun Isheni Allah ya kara budi na gode dan Umma.
Ya fara driving ba tare da ya kalleta ba yace mene ne aure Shukura ? Yanzu ka rasa tambayar da zaka yi min sai ta aure,aure waye bai sanshi ba bare ni da nake katotuwa, ba surutu nace kiyi min ba,tambayarki nayi mene aure ? Shukura ta kalli saman cikin motar ta tafi dogon tunani sannan tace Kaga idan kayi aurenka to shike nan kayi aure,sai mace ta dinga girkinta me dadin tsiya Tana cinyewa,sai kaga tayi kiba da haske,sannan kuma idan kayi aure Inna tace sai a dinga tararrayar mijin,ni yanzu yaya taya zan iya tarairayarka kayi girma da yawa sai dai na goyaka,Gaskiya ne Amarya cewar Ahleef,sai kuma me ? Uhmm ayi wanka da kwalliya,Ahleef yayi dariya tare da cewa zero baki ci ba tunda baki San mene aure,Allah na fada dai dai kaine dae baka Sani ba,tunda haka kace to bari na sake Sabo, ai dai ance mace ta dinga....sai ta rufe idonta wai kunya a hankali tace tana yiwa mijinta wanka tana silleshi da sabulu,haka aka koya mana a schl, yanda Shukura ke fada masa ya gane Bata ma san mene aure ba,a fili yace ai kuwa kin cinye Gaba daya,murmushi ta saki tare da cewa dama na fada maka ina ja,kwakwalwata na ja,babban kai ne dani,Dariyar da bai shirya ba ya shiga yi,baki ta turo gaba tana Shagwaba Haba Yaya dan Allah shike nan na daina fadama ai,Sorry na daina fada min inji.Shuru tayi wai tayi fushi,saida ya biya ta gidansu Fauziyya aka basu kudin data ranta sannan suka wuce har Maman Fauziyya ya gaisar tare da bawa Fauziyya 20k kauta.
Hafcy tun tana bin Niima har ta gano da kanta gwara ta nemi hanya da kanta,ita kuma Zahra tunda ta samu labarin da Shukura aka daura ta rantse Baza ta kara kula Shukura ba har abada. Malam Hari da Jamilu Bayan anyi musu sha tara ta arziki suka koma kauyensu, Shukura ta basu tabbacin Zata zo watara. Umma kuwa ganin Shukura Bata da gata sai ta fara gyara Shukura da tsumi masu inganci da kuma yanda Zata kula da mijinta sannan kullum Shukura ma tana zuwa wurin gyaran fata,Ahleef kullum sai ya shiga wajen Umma wai lafiyarsu yake dubawa.
4:30pm ya dawo daga Office a gurguje ya shirya Momee tana palo tare da Niima ya wuce da sauri yana tafiya yana sannu da hutawa Momee,tabe baki Momee tayi tare da cewa ga sallamamme an gama shanyeshi wlh da Abba baya kasar nan korarsu zanyi baki daya kawai ka sha wahalar rainon yaro sai yanzu za a nuna min iko,Niima tace ki bari idan Abban yayi tafiya Ahleef ma Sai ki kirkiri kasar da zaki turashi kafin ya dawo an gama komai.
Harara Momee ta bugawa Niima tare da cewa aike kika jawo tunda kika fasa aurenshi,na rike yaro a hannuna za a nuna min iko a kansa.
Ahleef direct part din Umma ya nufa cikin tafiyarsa me matukar birgewa,Door Bell ya danna Umma ce ta bude taga danta wai ita kunyarsa take ji, shi kuma Ahleef kunyarta yake ji lokacin da take ce masa Alhaji tana gaidashi ashe uwarsa ce guda,,Umma ce ta katse masa tunani da cewa shigo mana,cikin Ladabi ya durkusa tare da gaisheta,ta amsa da sakin Fuska sannan ta nuna masa bedroom din da Shukura ke ciki,ya nufi dakin ya kwankwasa Shuru kawai ya murda Handle din kwance ya ganta saman Bed tana sheka baccinta hankali kwance,sanye take cikin wata yar guntuwar Vest iya rabin cinyarta dark blue tayi mugun kyau cinyoyin kukuta lukuta gasu farare kar suna sheki,bai taba ganin Shukura haka ba.a hankali ta bude idonta fes a kansa yana tsaye sai kare mata kallo yakeyi,mikewa tayi ta zauna Gefen bed kafafunta suna lilo a kasa,Hannunta ta daura saman bed gefenta ta dan bubbuga kadan wai ya zauna,ita Shukura fa Bata San ana wani abu ba idan anyi aure ko tsoro Bata ji,sabo da bata da frnds tun asali, gefenta ya zauna.yana shakar kamshinta, itama haka,sai Mutsu mutsu takeyi kunya ta gama rufeta yana kallonta da guntayen kaya a jikinta.
Tana so ta mike domin dakko zani ta kare jikinta amma tana kunya ya kalle mata Mazaune subu subu wanda suke Masu matukar kyau kamar an zana mata su, shi kuma gogan ya ganeta sai gyarawa takeyi ta duburbuce amma sai ma kwanciya yayi abinsa saman Bed, Shuru tayi masa sai wasa take da yatsunta, shi dai kallonta yakeyi kawai,Kamar Baza tayi magana ba sai kuma tace bari naje na dawo,Ok kawai yace da sauri ta dakko Hijab kato har kasa ta saka, a ransa yace aiki ya sameki, 5mt ta dawa dauke da katon tire na abinci,ta jikin kofar tace dan bude min pls, yana budewa ya ganta da tire kato ta shugo a ransa yaji dadi kamar tasan yunwa yake ji sosai,so yake su hada ido amma taki Yarda,zuba masa tayi komai sannan tace gashi,ta bashi mamaki bai San tana da hankali haka ba sai yau abincinsa ya shiga ci ita kuma ta shiga wanka abinta.
Yana gamawa ya Gaji da jiranta bata fito daga wanka ba,sai ya koma dakin Umma, Baba ma yana nan suka shiga hirarsu ,Shukura kwalliya taci kamar Zata je biki,cikin wata atamfa me tsada dakyau fitowa tayi tana kamshinta.
Ya fito zai tafi Shukura kuma zata shiga,sai da numfashin Ahleef ya dauke na wasu lokuta sabo da kyan data yi, Murmushinta ta sakar masa me gigita maza,a hankali yace 11pm ki kawo min tea banda madara,Shukura tayi rau rau Zata fara kuka tace da dare haka part din Momee fa Allah ni dukana zasuyi bare naje har part dinka kai maka abu, ki kawo ba abinda zai faru, shagwaba ta fara kamar yar jaririya Allah ni...ni... Kunya... nakeji zafa ace min dadi miji tun ba a kaini ba ina bin miji,wani bala'in birge Ahleef tayi da wannan shagwabar tata,a ransa yace wai meke damuna ne yarinya karama Zata hallakani abinfa nema yake ya fi karfina,shike nan zan kasa Control,a fili yace
Ni nace kizo baki da tsoro nasani kawai kizo.
Shukuru tace tam zanzo amma wlh indai shegiyar Niimar nan ta tsokaneni sai na wanke mata kumatu fes da maruka Momee kawai zan kyale,amma Latifa kam ai sai na balla mata hannu, Ahleef dariya ya saki kadan,kuma Innata tace indan akayi aure to kar mace ta sake a taka mata birki wajen kula da mijinta,Ahleef yana Murmushi yace gaskiya ne, to ka gani ai dole ma na ci mutuncin duk wanda ke kokarin hanani tarairayar mai gida, Ahleef yace ashe zanji dadi na, Shukura tana murmushi tace kai Ni Allah ya gani bazan iya goyaka ba bare tarairaya, Akwai wata kawarmu a kauye aka yi mata Aure wai muka je ganin Amarya in baka lbr me zamu gani murjejen kato wai ya kwanta a cinyar matar,kuma idan ka ganta wata yar tatsitsiya da ita,Ahleef ya dinga dariya yanda take labarin, baka ganshi ba kamar ya hadiyeta sabo da girmansa ai idan nice Yaya kayi min haka wullarka zanyi.
Ahleef yace zaki kasheni da dariya My lollypop,Fari tayi da ido tace alawar yarace wannan ai haka kawai kace min wata lollypop alawar tsinke ,Alawar yara fa kenan yaya sai kace wani maye.Hmm yace na tafi sai kinzo zaki bani labari me dadi,Shukura tace tab yo ni me kake so na zama shike nan bazan ja aji ba?,zanzo amma ina baka zan gudu,Ahleef a ransa yace ina zamana ma zaki bani labarin ya wuce a binsa yana dariya da Nishadin daya dade bai samu ba, ita kuma ta kunna kallo abinta,Bayan kamar 10mnt sai ga Hafcy,Zahra tare da Niima harda Momee sun banko kofa kamar zasu ballata.
🥰😘🥰😘
Fans kuyi hakuri kwana biyu baku jini ba,ina busy ne,ba halina bane rashin typing akan lokaci kun san in dai baku jini ba to akwai dalili Inshallah baza ta sake faruwa ba.
YAU NA AJIYE TYPING SAI BAYAN SALLAH INSHAALLAH,ZAN TA SAMBADO MUKU BA TSAYAWA SAI ANGAMA.
AYI MIN UZURI FANS.
THANKS ALOT FANS.
LOVE U ALL. 🥰😘😍
AsmaBaff
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
31-35
Official
By
AsmaBaffa
ASMABAFFA FANS CLUB GA NAKU PAGE SABO DA KAUNA,ACI GABA DA SHARHI PLS.
Momee ce ta kalli Saudatu kallon wulakanci tare da nunata da yatsa tana kumfar baki kunyi kadan wlh kunyi tsararo inci kashin yaro,inci fitsarinsa sannan sama ta kai kuzo ku ruguza min farin ciki ,ku rabani da farin ciki to wlh karyarku tasha karya dai dai lokacin Ahleef ya manta wayarsa a dakin Shukura yazo zai dauka yaji abinda Momee ke fada, Momee kuwa taci gaba wa ya sani ma ko ba dan halak bane dan shegene kuka jefar ko kuka siyarwa da yan mafiya Allah yasa aka damke yan mafiyan,na raini yaro a hannuna kuzo zaku nuna min Isa Akan kawai kun haifeshi, da can me yasa baku nemeshi ba, sai yanzu,baku san cinsa ba bare shansa har zaku zo da wannan gantalalliyar yarinyar wacce aka haifeta a gona kan titi, me shegan hadama da son abin duniya an baro kauye an tattare to wlh bari kuji Ahleef ko gware kukayi kuka zo duniya to wlh sai ya sakeki verysoon,idan ma bai sakeki ba to Auren kuwa sai ya kara da Hafcy ko Zahra yanda na rike Ahleef wlh idan na tsine masa sai ta bishi.
Niima tace Momee na fada miki fa Ahleef ba irinda yake ba, yanzu neman mata yakeyi Akan naki aurensa,cikin shege yayi mata fa shine suka hada plan aka daura musu aure, Hafcy wacce jikinta ya fara mazari jin cewar Saudatu da dan dako sune iyayen Ahleef nan take cikinta ya duri ruwa sabo da tunano yanda take cin mutuncinsu,yau gashi dansu take so kamar ta mutu,taya zasu sota a matsayin suruka,shi yasa a duniya wulaknci ba abin yi bane akan kafi wani shima yana da baiwarsa ta musamman, Allah bai halicci dolo ko wawa marar amfani ko wanne akwai nasa baiwar.
Cikin karfin hali Hafcy tace Momee ni kadai zan iya gyara musu zama, ta kalli Shukura data kafesu da ido cike da fitsara,Hafcy tace munafuka saida kika jawo yayi miki ciki kika aureshi mayya dan aci dukiya,Niima ta kara da cewa anji kunya bariki tayi riba harda ciki, Shukura murmushi tayi tace wa yaki karuwa?an samu karuwa ai abin dadine tashin farko yayi min ciki da wuri uwar wata ko saida ta tsufa ta samu da kyar kinga ni abin na godewa Allah ne,kuma...Ahleef ne ya shigo a fusace tare da kwashe Shukura da maruka har biyu,Momee zaki fadawa magana haka,are u Mad? Saudatu da Baba basu ce komai ba kawai suka zauna suna shan kallo,Niima da Hafcy suka kyakyace da dariya,Momee ta kalli Shukura tace ki taka a sannu yarinya yanzu a baki takarda fara kal,u better watch ur tongue.
Wayarsa ya dauka ya fita a fusace zuciyarsa na zafi da jin maganganun su Momee sannan ya mari best frnd dinsa Shukura taya zai iya lallashin sarkin shagwaba kuma yasan gaskiyar komai amma ya take ya hukuntata,su Momee ma suka koma part dinta cikin tsananin farin ciki,Shukura ta kame a tsaye dafe da kumatunta,sai kuma ta fashe da kuka wiwi ta fadi a kasa yi take ba ji ba gani Saudatu sunyi lallashi har sun hakura.
Idonta ya kumbura har 11pm tayi yana jira ta kawo masa tea din da yace amma Shuru, a waya ya kirata bata fasa dagawa ba tace hello!ina tea din? Ya furta ransa a bace,Shukura ga zuciya ga tsoro, haka ta dafa tare da hada komai a tire,Umma tace haka zakije wajen mijin?da sauri ta fada Bedroom wanka tayi ta danyi kwalliya sama sama yanda Umma ke koya mata,Umma tace ki canja kayan bacci,haka dole ta shafa turaruka tasa katon Hijab har kasa ta fito kamar Zata fashe sabo da bacin rai,Umma tace ki tabbatar kin bashi hakuri kinyi laifi, baki ta turo tace kawai dan dankine shine ake nuna min banbanci kawai,dariya ma ta bawa Umma tace ae naji dan dana ne jeki maza dare nayi.
Shukura tana isa part din taci karo da Latifa tana karatu,ajiye tiren tayi gefe cikin sanda ba zato Latifa taji wawan dundu a bayanta har guda uku, bata zaci Shukura bace tunaninta Aljanune kawai ta kwashe da gudu tare da fadawa dakin Momee.Na rama nima cewar Shukuru ta dauki tire dinta har part dinsa,knocking biyu ya bude fuskarsa cike da farin ciki,a gabansa ta ajiye zata fita ya jawo Hijab dinta tare da dawo da ita ciki,burburwa ta fara masa zata kwace sabo da haushinsa take ji sannan gashi daga shi sai Boxers a jikinsa,surarsa me matukar kyau da birgewa a bayyane Bata Saba gani ba, kunnenta ya daura dan lips dinsa me taushi ya furta Ki tsaya ko nayi maganinki kin San ban son musu
ko so kike na kai kararki wurin Umma? wani yarrrr taji bata san sanda ta lumshe ido ba tana shakar kamshinsa,a kunne ya kara rada mata Shuk...kafin yace komai Shukura tace wayyo Allah wash kamar wacce aka cakawa Allura,shi kansa yaji tsoro,again a dai
kunnenta ya sake cewa lfy? noke kunnenta tayi tare da cewa dan Allah ka daina wani iri nakeji ba dadi ni gaskiya zan fadawa Umma,Murmushi yayi tare da rike hannunta zuwa Bedroom dinsa na alfarma wanda ya kai karshe a haduwa..
tsakiyar gadon ya hau yace bani tea baki ta turo irin ta gaji ita haka ta hado masa a cup tare da mika masa ta tsaya masa akai,Zauna mana, kafada ta makale tare da cewa ni fa bacci nakeji tafiya zanyi,Tea dinsa ya kurba kadan ya fara latsa wayarsa,da sauri tace laaaa dan kamo min game dama ita mayyar game ce ko a kauye haka take kwace wayar Baffa tayi ta yi,saman Bed din ta hau ta manta fushi take dashi tana leka cikin wayar taga chat yakeyi a whatsapp kara matsowa yayi jikinsu na gugar juna, Ahleef jininsa ya amsa sosai wani zirzir yake ji, Shukura ma hakan take kuma ta kasa tafiya,game ya kamo mata da kyar Sabo da jikinsa ke mazari,zallar shaawarta yake ji tana taso masa.
Tea dinsa ya shanye ya kasa samun nutsuwa,Shukura kuma ko a gyalenta,Wai baza ki cire hijab dinba?kai ta daga tana game dinta,a hankali ya daga hijab din ya shige ciki yana shakar kamshinta,tana jinsa tace pls ka fito,bai saurareta ba tana game dinta ba ji ba gani haka ta fisge kanta ta karfi tana ungo wayarka indai akanta ne kake min leke leke ga abinka kai Yaya sai kana abu kamar zaka cinyeni ni karbi wayarka nayi tafiyata,Murmushin da bai shirya bane ya subuce masa yace na bar miki wayar cire sim dina ki bani,Baki ta tabe tare da cewa bana so ka kyaleni da yar nokia ta idan nayi kudi na siya ina sa rai da wasu kudade kwanan nan, kana min leke Akan na ari wayarka ina ga kyauta kabani.idan ma ba rashin zuciya irin tawa ba,me zai sa na kulaka bayan ka zabga min Mari.
Kallonta yake cikin nutsuwa yace bakya mantuwa I'm so sorry ban kyauta ba na mari best frnd dita, da sauri tace kana rage min mukami da matsayi matar me kudi zaka ce ina matarka kana lika Min frnd kai wasa kakeyi da auren nan,cike da nishadi yace ai ke kika sa aka daura....kafin ya karasa tace kuma ya dauri hakkina na kanka baja baja kuma sai kasa na zama me kudi idan ba haka ba walakiri kai zai jibga lokacin ni na tsufa a aljanna.
Kwanta kiyi bacci kina ta surutu gashi har Umma ta rufe