Showing 36001 words to 39000 words out of 183527 words

Chapter 13 - Zafin Kai Book One Complete Hausa Novel

Mamugee   

26 Oct 2025

360

ba dan haka ya daga cikin tattaro nutsuwarsa datake kokarin barin jikinsa sbd komawan sumayyah gida da wannan cikin a yanxu babban hadari ne ga rayuwarta sbd komai ma zai iya faruwa idan Ababa ya sani.

dd babba dake babban lafiyayyan office dinsa na gida yanajin Bilal ya daga wayar kai tsaye yace yazo yanzu yanzu yana nemansa.

Rintse idanuwansa yayi cikin damuwarsa dake bayyana yana kallan su Benazir data miqar da sumayyah har sun kusa kofa yana jin kansa na sarawa da ya biyo bayansu ya bude musu mota yana kallan Benazir da idanuwanta sukai jajir cikin kulawa da sanyin jiki tareda kunyar kansa yace mata gobe da safe zasuyi magana idan ya taho daukansu amma ta kula da Sumayyan kafin goben.

Kai kawai ta iya gyada masa sbd bazata iya magana ba kuma bazata iya dagowa ta kallesaba.

A motar ma babu mai iya magana hankalinsa yayi mummunan tashi zuwansu gida da abinda zai iya biyowa kafin safiyar gashi dd babba na masa neman gaggawa wanda bai taba jin hankalinsa ya rabu biyu akan zuwan kiran dd babba ba sai yau din.

Yana ji yana gani dukkaninsu sukai shahadar rabuwa ya ajesu ya wuce yana sake jin fargaba na shigarsa na barinsu ya nufi gida.

Suna shiga gida suma kai tsaye dakinsu suka nufa sbd ba kowa tsakar gidan Annensu na bangaren dabbobinsa tana shara batasan dawowarsu ba,hande kuma tana daki tana baccin rana.

Kwantar da sumayyah tayi har lokacin bata ce mata komaiba sbd batasan me zata fada din ba sbd zuciyarta data kasa dawowa da bugawa daidai.

Zubewa tayi gefen sumayyar tareda rafka wani mummunan tagumi nauyin idanuwanta na qaruwa,

Sumayyah datake kallanta cikin nauyin idanuwan itama tashi tayi zaune tana kallan Benazir din da damuwa ta bude baki cikin taushin murya mara karfi tace

"Bena meya faru?
Meyasa kike cikin yanayin nan?
Wani abin ya faru ne?

Juyowa Benazir tayi da jajayen idanuwanta ta zubawa Sumayyahn sai alokacin taji hawaye na ciko idanuwanta.

Cikin mutuwar jiki da damuwa mai tsanani sumayyah ta dafa hannun Benazir din dake rawa muryarta na shiga tashin hankalin ganin hawayen dake ciko idanuwan Benazir tace

"Meya faru Bena?
Dan Allah fadamun meya faru,
Meya sameki?

Wani irin kuka mai ciwo da radadi ne ya kufcewa Benazir din mai qarfi da rshin sauti ta sunkuyar da kanta tana kasa magana.

Kukanta ya saka jikin Sumayyah daukan rawa sosai cikin tsoro da fargaba mai girma sbd duk abinda ya saka Benazir hawaye babba ne bare kuka mai qarfi irin haka.

Annensu data shigo dakin tayo alwalar sallar laasar zatayi tana ganinsu ta qaraso tana kallan Benazir datake kuka mai ciwo da radadin rai.

A tare cikin rudewa suka sake jefa mata tambayar abinda ya faru.

Annensu ta dago ta kalla tausayinta ya kamata saidai babu abinda zasu tare daga qaddarar da ubangiji ya doro musu saidai tasan wannan qaddarar mai nauyi ce garesu musamman Annensu da bazata iya daukan wata azabar ba da ciwon lamarin a matsayinta na uwa kuma mahaifiyar sumayyah.

"Menene Benazir ki fada mana,meya faru?"

Takardar da aka basu a asibitin ta cikin Sumayyah ta ciro daga cikik rigarta ta miqawa sumayyah sbd Anne bazata iya karantawaba, taja wani numfashi mai zafi da mutuwar jiki Muryarta a sanyaye ta bude baki tace

"Anne ciki ne kaman yanda kikai tinani......

Kasa qarasa bude takardar Sumayyah tayi ta tsaya cak tareda dagowa tana kallan Benazir datake hana kukanta dawowa tana kallan Annensu data dauke wuta.

"Anne, Anne, Anne" tafada hankali tashe tana taro Annen jikinta sbd yankewan da jikinta ne neman yi.

Tashi tayi hankali tashe koina jikinta na rawa ta taro Annen tana sake kiran sunanta cikin sabon tashin Hankali murya qasa qasa sbd ba daman daga muryar kada a jisu.

Sumayyah da itama tayi mutuwar zaune ta juyo ta kalla cikin tashin hankali tace kawo ruwa Anne zata siqe.
Sumayyahn bata san me Benazir take fada ba sbd suman datayi a zaunen itama.

Tashi Benazir tayi da sauri ko gabanta bata gani tana kimfewa ta sake tashi da sauri ta fice ta debo ruwa tana zuwa ta zubawa Annensu kofin ruwan gabaki daya kafin ta sake fita qafafunta na hardewa ta debo wasu ta zubawa sumayyah ta wurgar da kofin tayi kan Annensu dake jan numfashi daqyar tana dafe kirjinta dake toshewa.

Cikin tashin hankali da tsoro mai tsanani Benazir take shafa mata bayanta tana karanto mata adduoi tana kiran sunanta a hankali.

Sumayyah data dawo hayyacinta kuwa wasu hawayen tashin hankalin da baa saka masa rana bane suka tsinke mata tana jin tsoron da bata taba jinsa ba a rayuwarta yana shigarta sbd tabbas lokacinta yayi.

A hankali Anne ta dawo daidai ta dago ta kalli Benazir da idanuwanta sukai jajir ta maida kallanta kan sumayyah take suka fashe da wani irin kuka mai tsananin ciwo da tashin hankali duka su ukun a lokaci daya.

Kuka sikeyi sosai mara sauti kowannensu na rasa abin fada tsawon lokaci mai tsayi kafin Benazir ta dago tana share fuskarta sbd jin motsin fitowar Hande tsakar gidan tana kwada kiran Annensu dan batasan suma sun dawo ba.

Kowannensu taqaita kukansa yayi suka share fuskokinsu babu wanda yace komai suka fito daya bayan daya fuskokinsu a qasa sbd yanda idanuwan kowannensu yayi jajir ya kumbura.

Kallansu Hande batayiba bare taga halinda sike ciki kai tsaye ruwan datasa a debo mata a bokiti Benazir ta debo mata takai mata bandaki ta fito sukai alwala sai alokacin suka samu damar yin sallolin dake kansu itama Annen me alwalar laasar saida ta sake wata.

Koda suka gama sallah jigum jigum sukayi har lokacin babu me magana sbd bude bakinsu ma a yanzu tsoro sukeji dan basusan ta inda zasu faro wannan maganar ba a cikin gidan da fitar maganar daidai take da tsayuwar alqiyamarsu.

Har akai sallar magriba aka fito babu wanda ya fita acikinsu da alwalar sukai sallar suka sake komawa zaune kowa yayi shiru yayi nisa a tinaninda babu komai acikinsa sai tashin hankali da tsoro tareda tinanin makomarsu a gurin Ababa.

Abincin dare da aka basu a ranar haka ya kwana bar safe babu wanda ya sake kallan inda yake sbd masifar da suke ciki.

Suna gama sallar asuba Anne ta kalli sumayyah da a daren guda ta zabge sbd tashin hankali.

Dukkaninsu babu wanda idanuwansa basu fada ba sukai jajir sbd duk kasancewar bacci barawo a ranar ya kasa sace su ynda suka ga rana haka suka dare.

"Waye yayi miki haka Sumayyah?
Wane qaddara ce wannan sumayyah?
Tsautsayin menene wannan?
Meyasa sumayyah?
Waye ne??

Tsit dakin ya dauka bayan numfashin dake fita a sarqe da damuwa mai tsanani babu abinda akeji a dakin.

Sunkuyar da kai Sumayyah tayi wasu hawayen na gudu kan fuskarta quncinta na tsananta tareda kunyar kanta dana mahaifiyarta da 'yar uwarta sbd wannan qaddarar masifarta ba iya kanta zata tsaya ba dukansu ukun ta tabbatarda sai sun mafi munin halin quncin rayuwa a gurin Ababa.

"Alh Bilal"  tafada muryarta na yankewa sbd kuka mai qarfin dayazo mata.
#MAMUH#
#DD KAANTE#
#LOVE#AMNAH KAANTE#BENAZIR#crazyinlove#

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim

Send your Shedan biya Anan👇
09032345899

MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070

Zafafa🫶🔥🔥

*_Arewabooks@Mamuhgee_*
20
Shiru dukkaninsu sikayi sbd daman sunsan bazai wuce Alh bilal dinba dan haka kowannensu ya sake shiru sbd basusan mafitar wannan qaddarar ba data rigayi fata.

Cikin rudewa da tashin hankali Annen batama san me dame take fada ba ta fara fada ciwonta na neman tashi sbd kanta da yayi nauyi neman juyewa yakeyi
Benazir ta taso ta dawo gurinta da sauri tana kwantar mata da hankali sbd kar ciwon ya tashi komai ya lalace asan halinda suke ciki.

Har gari yayi haske suna daki suna fama da kansu ba sauki ko kadan dole Benazir ta fito ta hau aikin gidan gabaki daya ba maganar zuwa makaranta sbd tsoron fita takeyi ma tabarsu kada kafin ta dawo Ababa ya sani ta dawo ta tadda babu su ga kuma yanayin Annen daketa surutai cikin tashin hankali da fita hayyaci
Sumayyah ma idanuwanta sunkai ko budewa basayi sosai sbd kumbura ga yanayinta na rashin lafiya.

Abincinsu na dare da basu ci ba haka suka zauna su ukun suka turasa cikinsu da sanyinsa harma ta sakewar daya fara yi sbd kada su fitar a san basu ci a fahimci suna cikin wani halin a gano.

Babu mai dadin rai ko nutsuwa a cikinsu haka kowa ya ringa diban abincin yana turawa bakinsa bame magana suna gamawa Benazir ta dauki kwanon ta fice taje tafara wanke wanke.

Annensu zaune take a dakin nasu ta kasa fitowa idanuwanta sunyi ciki ciki tsaban kuka da damuwa ta rafka tagumin da basusan yanzu kuma yanda rayuwa zatayi dasu ba.

Sumayyah kuwa ciwo ne yake cinta sosai amma tashin hankali da damuwa ya hanata nunawa itama tagumin ne ta rafka dukkaninsu kaman wainda ke jiran sakamakon mutuwa.

Benazir ma ayyukan gidan takeyi ba'a cikin cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali ba kowannensu tinanin makomarsu yakeyi.

Sai bayan sallar Azahar ta kammala aikin tayi wanka da alwala tazo tayi sallah aka basu abincinsu data gama girkawa ta kawo ta ajiye musu dole sukai sallah suka zauna suka turawa cikinsu babu me jin dandanon komai a bakinsa cikinsu kowa 'dacin bakinsa yakeji musamman Sumayyah da nata ya hada dana ciwo da laulayi.

Tsit Hande taji gidan yayi suna daki babu me iya motsin kirki sbd damuwa da tinani dan haka ta fito tana qwala kiransu tana tambayar lafiya suke zaman daki kaman masu abin kunya.

Tsinkewa cikinsu yayi Anne ta kalli Benazir da itama ita ta kalla suka kalla sumayyah a tare kafin Anne ta bude baki cikin mutuwar jiki tace

"Ki zauna a dakin karki fito"

Gyada kai Sumayyah tayi tana rintse idanuwanta sbd kunyarsu dake cin zuciya da ganganr jikinta gashi ta kasa ko bude baki ta fada musu kaddara ce da shedan daya shigo ciki.

Anne da Benazir ne suka fito sbd kada hande ta tsananta maganar.

Kallansu tayi taga duk sun jeme a dare daya kaman wainda sukai kwanan zaune,
Fuskar Benazir ta kalla taga yanda ta sauya kwata kwata da alamar bata rintsa ba kuma harda alaman kuka bayan rashin baccin.

Kan Anne ta maida kallanta taga itama fuskarta tayi jajir ta kumbura,
Shiru tayi tana nazarinsu sbd da alamar akwai abinda ya samesu dan duk wuya duk tsanani su biyun nan basu cika kuka ba sbd Anne ta dade da samun rashin lafiyar rashin kuka sbd shekarun data debo a rayuwar gidan zuciyarta ta mace bata iya kukan hakama Benazir sbd taurin rai da juriya ba qaramin tashin hankali da masifa ke sakata kuka ba amma yau gashi da alama kukan suka kwana yi..

"Kodai sumayyah ta mutu ne tsakar dare?" Tayi tambayar kai tsaye tana kallan hanyar kofar dakinsu da mamaki.

Anne wani numfashi mai sanyi ta sauke zuciyarta na sosuwa da abinda Handen ta fada tayi qasa da kanta tana kasa cewa komai.
Benazir ma numfashin mara sauti mai dumi ta sauke tana girgizawa handen kai tace

"Tana nan lafiya ce batada tin jiyan"

"Shine kuka kwana kuna kuka ko me? Ta sake jefa musu tambayar tana kallan Benazir da idanuwanta ke sake yin qasa.

Shirunsu yasata rufesu da fadan batasan dabiar koke koke a cikin gidan da ba mutuwa akai musu ba.

Fada ta ringa yi sosai sai data gaji ta dena tace su wuce ga wankin shagon Ababa can an kawo.

Wucewa sukai inda manyan kullin kayan wankin masu yawa suke suka warware suka ringa kwashe kayan zuwa inda suke wankin.

Benazir ce ta fara debo ruwa masu yawa ta tara musu
Suna fara wankin Anne ta sunkuyar da kanta qasa wani irin kuka mai sauti na subuce mata mai tafe da tsananin ciwo da quncin da zuciyarta take ciki.

Benazir radadin sautin kukan mahaifiyar tata ya sata kasa wanke kayan dake hannunta tayi qasa da kai itama wasu hawaye na tsinke mata,
Me zasuyi?
Meye mafitar halinda suke ciki?
Ya Allah ka dubi maraicinsu" shine abinda zuciyarta kawai ta iya fada sbd sunsani sun tabbatar mawuyacin hali ne suke ciki mai nauyi.

Saida sukai kuka sosai kafin suka hakura suka fara wankin babu mai magana har suka wuni sunayi sai gab da magriba suka gama sbd abincin dare da Benazir ta dora tanayi tana tashi.

Daki suka shige bayan sunyi Alwala abincin dare kawai sukaci sukai ishai da akai suka lafe dakin babu wanda ya sake fitowa saida Ababa ya dawo Benazir ce ta fita taje takai masa abinci da ruwa ta dawo dakin suka cigaba da zaman damuwa.

Washe gari ma hakan ce ta kasance babu wanda ya fita makaranta cikinsu haka suka wuni cikin mummunan yanayi na damuwa.

*****kusan kwanaki hudu sika share a hakan cikin zallan damuwa da qunci tareda tsoro da firgici mai tsanani,
Sumayyah na daki jikin nata sai tsanani yake qarawa amma basa barinta fitowa sai idan zata je bandaki kokuma idan Ababa ya dawo sbd kada ya saka musu idon zargin wani sai ta daure ta fito dan kawai ya gansu yasan suna nan kalau ba matsala,

Hande data ankara da yanayinsu gabaki daya ya sauya a kwanakin sai ta saka musu ido sosai ga Benazir data dena zuwa makaranta sbd tsoron kada ta fita a ganosu tinda daga Anne har sumayyah idan bata nan zasu iya firgicewa suyi abinda zai bayyanarda halinda suke ciki.

Ta bangaren Alh bilal kaante kuwa a cikin kwana biyun da baya ganinsu duk zuwan dayake yi kullum dan daukansu kaman zaiyi hauka a cikin kwanakin sbd gabaki daya shima ya shiga tashin hankali mai girma rashin ganinsu,
Tsoron Ababa da abinda zai iya yi musu yasashi komawa kaman mai tabin hankali shima dayake mutum ne mai nutsuwa da kamun kai take aka gano yana cikin mummunan yanayi na damuwa da tashin hankali,
Dad kaante da dd babba tini suka fahimci yana cikin mawuyacin hali sukaita tambayarsa ko lafiya amma sam zurfin cikinsa baya barinsa fada musu komai dan haka ran dad kaante ya baci ya kira Mahaifiyarsu Bilal din ya bata lokacin dawowarta idan ba haka ba damuwa zata kashe mata 'da a banza tana can gurin wancan da baya buqatan kowa tinda shine ya zabi zama baa cikin family dinsaba.

Dd babba kuwa ganin da gaske lamarin yayi yawa sai kawai ya tura bilal din wani aiki Kenya dole Bilal ya tafi bayan kusan har kwanciyar jinyar kwana biyu yayi sbd rashin sanin halinda su Sumayyah suke ciki,
Yayi yawo anguwar yafi so hamsin a kwanakin amma babu alamarsu gashi yana gudun ya tinkari Ababan kai tsaye kila bai saniba tukuna kada ya janyo musu fitina wanda ya san da DD ne da tini zai tinkari Ababan duk abinda zai faru ya faru kowama ya dade bai saniba.

Ms aysha ce Aminiyarsa da zata iya masa komai ko baya nan dan haka ita ya sanarwa komai tareda rokonta taje ta dubo masa su tareda kular masa dasu.

Ranar daya wuce washe gari cikin saa sai ga Benazir tazo makarantar itama sbd Ababa yafara fahimtar ta dena zuwa hakama suna neman mafitan yanda zasuyi da cikin daga Bilal din tinda basuda kowa basuda gurin zuwa hakama bayyanar cikin dede yake da basusan ma me zasu ce ba.

Zuwan Benazir makarantar ya hana ms aysha zuwa gidansu ta zauna da Benazir din cikin kulawa ta tambayeta lafiyarsu da yanayin Sumayyar.

Shiru Benazir tayi takasa magana sbd kukan dayazo mata a hankali
Ta sanar da ms aysha mafita suke nema basuda yanda zasuyi da rayuwarsu.

Kukan Benazir ya taba zuciyarta sosai kusan saida idanuwanta suka ciko da hawayen itama dan haka
Cikin tausayi da baqin cikin qaddarar itama ta ringa rarrashinta tareda yanke shawarar zaa  cire cikin kawai kokuma dole Alh Bilal ya fito fili a yi maganar aure tin kafin maganar cikin ta bayyana.

A gaban Benazir Ms aysha ta kira Bilal sukai magana sosai ta nuna masa damuwar dasu Benazir suke ciki.

Kai tsaye kasa amincewa yayi da cire cikin sbd hadarinsa da cutatarwa ga Sumayyah zatayi yawa.

Bai taba jin karfin soyayyar data danne tsananin tsoro da shakkar dd babba da dad kaante ba sai a yanzu dayake jin zai iya daukan hukuncinsu dana familyn kaantes gabaki daya akan sumayyah.

Kaman yanda Benazir da Anne suke neman mafitar lamarin Ms aysha da Alh Bilal din sun musu alqawarin yana dawowa zai nema auren Sumayyah batareda Ababa yasan da maganar cikin ba hakama duk dukiyar dayakeso yayi alqawarin basa dan ya basa auren sumayyah din.

Wannan alqawarin yasa Benazir daurewa ta tsaya makaranta bayan Ms aysha tayi mata alqawarin tsaya musu har qarshen rayuwarta insha Allah.

Ana tashi makaranta ms aysha ce ta dauketa ranar da kanta ta kaita gida kuma cikin saa Ababa bayanan hakama hande tana baccin ranar data saba dan haka har cikin dakinsu dayasa ms ayshan zubda hawaye suka shiga ta duba sumayyah tareda yiwa Anne Alqawarin zata kula dasu Benazir kaman yayan data haifa a cikinta da yardar Allah.

Kudi ta basu amma tashin hankalin dasuka shiga ma na ganin kudin yasata maidawa jaka ba shiri sbd tsoron kudin.
Tanaji tana gani ta tafi batareda bar musu komaiba sbd sunqi karban kudin.

Tana ficewa Hande ta tashi data fito ta ringa mitar qamshin tiraren manya take jin ya cika gidan koina.

Shi kansa Ababa daya dawo saida ya tsinci qamshin musamman dakinsu dan haka aka bincike kayansu tsaf baa ga komai ba dole aka hakura sedai saka idanun da akai akansu sosai sbd sam hande ta kasa yarda dasu a kwanakin.

Benazir dole ta koma makaranta kullum tana zuwa
Sumayyah dai dole aka hakura saita warke tukuna.

Kullum idan taje sai tayi magana da Alh bilal din a waya yaji ya jikin Sumayyah ta fada masa da sauki ta wuce karatunta.
#MAMUH#
#BENA#DD#ZAFIN KAI#

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim

Send your Shedan biya Anan👇
09032345899

MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070

Yan Nijar kuma ga inda zaku biya👇👇👇

+22799643131

Zafafa🫶🔥🔥

*_Arewabooks@Mamuhgee_*
21
Taka tsantsan suka hau yi da duk wani abin da zai saka a fahimci halinda sike ciki komai qanqantar kuskure kiyayesa sukeyi,
Sumayyar ita kanta dole ta ringa tilasta kanta tana nemo kuzari da qarfin hali tana fitowa wasu ayyukan sbd saka idon Hande akansu yayi yawa.

Benazir ma datake zuwa makaranta tini sukaiwa kansu fada komai na Alh bilal harma dana ms aysha sun dena karba duk tsananin yunwa da rashin lafiya sun dena karban abincinsa da maganin dasuke fitowa daga garesa duk da bak dawo din ba kawo musu akeyi makaranta amma sam Benazir ta dena karba.

Saida suka share sati kusan uku suna fama da jikin Sumayyahn kafin ta fara fita makaranta.

Annensu duk suka fita harsu dawo hankalinta baya jikinta sai taga dawowarsu sbd yanzu tsoron mutanen waje ma takeyi,
Benazir yanzu takeji duk da tasan ita tanada kame kai da hankali fiyeda yayarta Sumayyah din

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login