Showing 18001 words to 21000 words out of 183527 words

Chapter 7 - Zafin Kai Book One Complete Hausa Novel

Mamugee   

26 Oct 2025

338

isa asibiti dan kuwa daga Benazir din har Bilal babu wanda yake tina komai bayan samuwar sumayyar da rayuwarta daga halinda take ciki.

Kaman wancan karon take aka kwantar da ita nurse da likita suka fara abinda ya kamata akanta Bilal din da Benazir suna waje babu mai iya magana a cikinsu sbd Benazir datake neman zauncewa da tashin hankali.

Haka sukai zaman jira bayan an barsu a dakin su kadai suna tsimayin farfadowarta.

Guraren qarfe goma numfashinta ya dawo daidai alaman bacci mai qarfi ya dauketa daga wahalar,
Kallan Benazir Sir Bilal yayi yace mata zai tafi office yanada masu jiransa zai dawo ba jimawa.

Gyada masa kai kawai ta iya yi harya fice bata iya motsawa ba.

Zaman jira ta dasa har bayan azahar ta samu tayi alwala a toilet din Amenity room din dasuke ta futo tayi sallah tana idarwa Sumayyah din na farkawa ta taimaka mata zuwa toilet tayo fitsari da Alwala tazo a zaune tayi sallah tana idarwa Akai knocking kofar dakin tareda turowa aka shigo.

Kallon wanda ya shigo sukayi dukkaninsu a tare harda Sumayyah dake cikin mutuwar jiki.

Kallansu yayi shima cikin yar girmamawa yace Sir bilal ne ya aikosa ya kawo musu sako,
Ajiye ledojin hannunsa yayi gaban Benazir yana juyawa bayan yayi musu fatan samun sauki ya fice daga dakin tareda rufo kofar.

Kaman bazasu taba ledojin ba tsawon mintina kafin Benazir ta bude ta duba taga take aways ne masu dauke da sunan tsadaddan restaurant din KAANTEs Hotels & Suites.
Wasu irin tsadaddun Deserts ne da crispy chicken sai chicken biryani da kuma salad sai drinks marasa sanyi sosai da ruwa katan daya.

Wani tsinkakken yawu ya wuce maqogwaransu su duka biyun sbd wani irin kamshi da basu saba ji ba dayake shiga hancinsu.

Kallon juna sikai kowannen hanjinsa na fidda wani sautin kukan yunwar datake tauye dasu.

Babu wanda yayi magana a cikinsu abincin sike sake kalla Sumayyah na jin kaman zatayi amai sbd yunwa da matsuwa taci abincin,
Ita kanta Benazir yawunta sun kasa tsayawa sai tsinkewa sikeyi suna wucewa maqogaranta.
Sun jima suna shawarwari da zuciya da hanjinsu kafin daga karshe dai suka afkawa abincin da bismillah suka cinye komai tas sbd Nama wani abu ne da a iya shekarunsu bazasu iya fadan so nawa suka taba cinsa ba,layya Ababa bayayi,baya siyo nama gidansa baya yanka,idan kaga yaci nama iya wanda zaici ne shi kadai sai Hande dayake bawa dan haka a rayuwarsu dai bakinsu bai wani san dandanon namaba dan haka yau din suka ci kaman ba gobe.
Suna gamawa Nurse ta shigo ta bawa Sumayyah magani tareda wasu allurai take sumayyah din takoma bacci.

Ita kanta Benazir din sbd hutu da Cimar da basu saba ba take bacci ya dan dauketa daga kujerar datake zaune.

Basu farkaba sai bayan laasar da sauri Benazir ta tashi ta fada toilet din dakin ta wanko fuskarta tareda Alwala ta fito ta kama Sumayyah tayo Alwala itama suka fito babu bata lokaci sikar sallar laasar suna idarwa sika fara tinanin tafiya gida sbd ba laifi sosai Sumayyah din ta samu sassauci daga mummunan azabar datake ciki,

Babban abinda yasa duk ha'darin hakan Benazir ta yarda suka zo asibitin shine tinawa takeyi da hadda qonuwar wuta ne yayi sanadin Rasuwar Samirah,
Idan ta tina hakan jin takeyi zauncewa zatayi daga ita har Annensu idan wani abu mai kama da hakan ya samu Sumayyah sbd a yanzu da suka debo shekaru iya su tini sika manta da komai da kowa bayan junansu,

Wata irin kauna ce mai tsananin gaske da qarfi take sukewa junansu,
Tin shekarun baya da suke tareda sauran yan uwansu daman Kaunar Benazir a ran sumayyah daban ce hakama ita kanta Benazir din sumayyah daban take a ranta bayan Annensu,sai samirah da itama suke ji da ita sbd tana kaunar yan uwanta sosai da zuciya daya,Safnah ce zasu ce basu tabbatarda tasu kaunarba a ranta amma a nasu ran itama suna kaunarta har cikin zuciyarsu amma daga ranar datayi amfani da Annensu ga gudu suka rufeta daga zuciyoyinsu dan bazasu iya ciretaba jininsu ce kuma suna sonta gaskia.

Kokarin barin dakin sukeyi Nurse ta shigo ta hanasu tareda sanar dasu sai Sir Kaante ya dawo umarninsa ne.
Babu yanda basuyiba su tafi aka qi barinsu haka suka zauna suna jiransa har Sumayyah ta sake komawa bacci sbd akwai abinda yake sakata baccin tsakanin allurar da aka saka mata a drip nata kokuma maganin  da aka bata.

Benazir zuwa lokacin hankalinta ya dawo jikinta gabaji daya bata cikin nutsuwa tsoro da bugawar zuciyarta gabaki daya sun zaburo,ko wane iskar numfashin datake shaqa tafe yake da zallar tsoro da fargaba.

Wani abincin aka kuma kawo musu wannan karon snacks ne,Samosas manya masu kyan gani sai doughnuts masu girma da taushin gaske sai cup cakes da wata kalar crispy chicken din,
Ladar daya kuwa drinks ne sai Apples.

Numfashi ta sauke sbd wannan karon kam Asarar kayan zaayi dan bazasu iya cinyewa ba haka bazasu iya zuwa gida dashi ba.

Sumayyah data farka kadan taci sbd maganinta akwai me saka cin abinci sbd ganowa da akai akwai yunwa tareda uta sun dauka itace batason cin abinci basusan samun abincin ne batayiba taci ta koshi.

Benazir kasa cin komai tayi sbd fargaban zuwa gida da abubuwan gashi a yanayin ciwon sumayyah da maganinta tana buqatan abinci.

Tana cikin shawarwari akazo tafiya dasu gida ba Bilal din bane aiki ya riqesa suna ganin hakan suka saka ya ajiyesu makaranta daga can suka hau mashin suka koma gida.

Cikin tsoro da fargaba mai tsanani suka shiga gidan
Hande na dakinta Annensu ce kawai tsakar gidan tana aikin wankin kayan Hande dasu zannuwan gadon Ababa.
Suna ture ture sbd rawar jiki da tsoro suka fada dakinsu
cikik rawar jiki Benazir ta fidda ledan kayan ta tura cikin kayansu na sakawa dake daure a gefe
Sai alokacin ta saki ajiyan zuciya gabanta na tsananta faduwa tinda ba cinyewa akai ba har lokacin suna cikin hadari mai girma.

Sumayyah da zuciyarta da jikinta suka kasa dena rawa itama kallon Benazir tayi murya a sarke tace

"Bena ki shigo da Anne tin Ababa be dawoba a cinye kayan nan mu saka ledojin a bra tsoro nakeji sosai wlh,
Idan tsautsayi da kadda yasa Ababa yaga ledan nan sai rasuwar samirah tafi tamu sauki da rahama.

Ita kanta Benazir bata cikin kwanciyar hankali idan ba kawar da komai akai ba tunda mummunan kaddara tasasu shigowa gidan da kayan sbd Annensu sukeso itama yau taciwa cikinta abinda zai koshi tinda abune da basu taba ba arayuwarsu ci a koshi.

Sallar magrib sukayi suna idarwa suka fito Benazir ta kamawa Anne wankin suka qarasa ba bata lokaci suna gama shanya suka shigo daki.

Benazir ce ta zauna setin kofa tana hango mai tahowa suka fidda kayan tareda budewa Anne suka ce tayi sauri taci ta koshi.

Wani tsalle zuciyar Anne tayi kaman zata fado sbd tsananin tsoro da firgita muryanta na rawa qasa qasa tace
"Ina kuka samo?
Menene wannan din?
Meyasa kuka taho dashi gidan nan?
Kusan kashemu Ababa zaiyi idan yaga wannan kayan ko Hande.

Sumayyah ce ta dauko doughnut hannunta na rawa sbd tsoro ta tura mata a baki itama murya na rawar tashin hankali tace

"Anne kiyi sauri kici zamu fada miki daga baya inda muka samu"

Laushinsa da qamshin mai dadi tareda azababbiyar yunwar cikin Annen yasata yagar rabinsa tafara ci take taji cikinta yana kukan yunwar ya samu abinci.

Hannu baka hannu qwarya takecin kayan musamman kazar me shegen dadi tana gamawa ta shanye orange drink din dasuka juye a leda suka dauro mata sbd bazasu iya shigowa da robar gidan ba.

Hamdala Annen tayi bayan da cikinta ya cika sosai
Ta hada wani irin uban zuba sbd tana cin kowace irin loma cikin babban tashin hankali da rashin kwanciyar hankali da nutsuwa,
Yanda kasan barayi haka dukkanin idanuwansu suke a waje kowannensu na hada gumi suna kallonta ta koshi.

Sauran abinda ta rage Sumayyah taci ta bawa Benazir sauran itama ta cinye suka nade ledojin kowacce ta tura cikin rigarta dasu suka kwana ajiki dan abincin da aka basu ma dole suka turasa sbd kar a gane sunci wani abin.

Washe gari ba laifi jikin Sumayyah saidai akwai zazzabi data kuma tashi dashi sbd yanayin makwancinsu basuda kofa a dakinsu shiyasa kusan kullum ko lafiyansu kalau kusan da zazzabi suke tashi kowannensu sbd sanyi dan duk zafi su yanada wahala sujisa sosai sbd anguwar tasu kaman daji take ba mutane dan haka akwai sanyi sosai.
#MAMUH#
#BILLONAIREROMANCE #DD KAANTE
#CONTRACT#HOTLOVE#ABABA#BENAZIR ABABA KAANTE.

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
09033181070
09032345899

Zafafa🫶🔥🔥

_Mamuhgee 12_

*_ASSALAMU ALAIKUM JAMA’AR KWARAI JAMA’AR ZAFAFA BIYAR_*

*_KAMAN KO DA YAUSHE DA MUKE KAWO MUKU ABABEN AMFANI GANGARIYA KUMA DAKI BARI MASU AMINCI A KUDADE KALILAN_*

*_YAU MA MUN ZO MUKU DA TALLAN BABBAN SHAGON NAN DA KE KAWO MU KAYAYYAKI NA KASAR GERMANY!! KUNSAN DAI GERMANY SUNE AGABA A FANNIN KAYAYYAKI MASU KYAU DA KARKO_*

*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*
*_MAAB LUXURY HOME_*


*_SUN KAWO MUKU DALLADALLAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAWATARWA DANA KITCHEN MASU HASKA DAKUNAN GIRKI… KWASHA KWASHA_*

*_SU DIN KARSHE NE A DUNIYAR KAYAYYAKIN GIDAH DANA KITCHEN NA KECE RAI NI… INA UWAYEN GIDAH, AMARE? ANTOCI, KAWUNNI, YAYYU MAZA, KANNE DA MA IYAYEN MU MAZA?_*

*_KU ZO A DAMA DA KU A WANNAN DAMAR ME DAUKE DA DIMBIN KAYAYYAKI MASU KYAU A KUDI DEDE MISALI WANDA KOWANE ZAI IYA MALLAKA IYA KARFIN SA_*

*_KU ZIYARCI SHAGON DA KE A KANO.. TITIN AHMADU BELLO WAY_*

*_KO KUYI ORDER DA GA SHAFUKAN SADARWA TA INSTAGRAM:@Maabluxuryhome_*
*_FACEBOOK:@maabluxuryhome_*

*_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH,, INGANCI DA RAHUSA, KYAU A DADE ANA AMFANI DA SU SAI KAYAYYAKIN MAAB LUXURY HOME_*

*_A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY ORIGINAL HOME DECORS AND KITCHEN UTENSILS_*

*_MAAB LUXURY HOME GOT YOUR HOME AND YOUR KITCHENS COVERED… JUST A VISIT/CALL/DM AWAY_*

*_08034631010 MAAB LUXURY HOME👈🏽_*


******
Sauran ruwan zafin lipton da Ababa yasha shayi aka basu babu bread haka suka shanye zallar ruwan zafin da ko sugar baijiba sukai shirin makaranta suka fice.

Suna fita yauma tafiya kadan sukai motar Bilal daya kwana dasu a ransa baida sukuni ta tsaida mashin dinsu a kunyace suka sauko sbd overload dinsu ba kyan gani itace a tsakiya sun matsu iya matsuwa suda mai mashin dayake jin tudun kirjinta wanda kusan hakan suke zuwa makarantar kullum babu ranar da har akai makaranta ba cikin baqin ciki da quncin yanda jikinsu ke manne dana mai mashin din ba.

Shi kansa Bilal dake cikin motarsa qarewa yanayinsu dana mai mashin dain yayi yaji wani irin abu ya tokare kirjinsa musamman yanda kowaccensu dazata sauko kusan daida jikinta dana mai acaban ya hadu.

Rufe idanuwansa yayi ahankali tareda dauke kai daga kallon gurin glass ya aka sauke drivernsa ya miqawa mai mashin din 2k yace ya wuce kawai.

Drivern da kansa ya fito ya bude musu bayan motar suka shiga sbd Sir bilal din yana seat din gaba.

Suna shiga aka bar anguwar dasu babu wanda ya iya magana acikinsu bayan gaisuwar da sukai masa cikin girmamawa da nutsuwarsu dake sake samar musu da gurbi a zuciyarsa.

Hanyar asibiti suka nufa kai tsaye
Yau babu bata lokaci dubata akai aka canja dressing din qafar wanda suna kama hanyar gida suke ciresa su yar sbd kada a gani.

Ana gama dressing gurin aka bata magani tasha suka fito ya ajiyesu makaranta bayan yasa akawo musu abinci daga restaurant dinsu na Kaante hotel and suites.
Suna fitowa first lectures dinsu aka kawo musu abincin har kofar hall dinsu sumayyah din sbd Sir bilal ya sanar dashi hall din dazai sameta tinda ba waya ne dasu ba.

Sumayyah ganin mutane dakuma tsoron jawa kai attention yasa ta karba da sauri tabar gabansa ta nufi gurin Benazir da itama tsoron ganin abincin yasata jan sumayyah suka bar cikin mutane.

Nesa da mutane suka boye suka zauna tareda zubawa ledojin ido hankalinsu tashe sbd zuwa lokacin har ga Allah taimakon ya ishesu tinda sumayyah din tasamu sauki ba laifi.

Har aka tashi basu ci abincin ba suka fito saiga driver yana jiransu a gate suka dauke kai suna shigewa mutane sbd kada ya gansu amma haka ya ringa binsu yana sanar dasu Sir bilal yace kada abari su hau mashin.

Benazir kaman zatai masa sujjada ta ringa rokonsa ya dena binsu shima kaman zai musu sujjadar ya ringa rokonsu akan umarnin mai gidansa ne.

Sumayyah datafi shiga tsoro tana kalle kalle tace su shiga kada wani yagani tinda ba tafiyar zaiyi ba.

Haka suka iso anguwarsu kaman zasuyi zawon kayan cikinsu sbd tsoro.
Yana ajiyesu suka fito qafafu na rawa suka nufi hanyar gidansu suna waiwaye sbd ledan dake cikin hijabansu.

Yauma cikin saa Hande bata tsakar gida sukai saurin isa daki.

Na yau basu ci ba sbd yanada qamshi zaa iya jinsu dan haka suka boye cikin kayansu sai tsakar dare suka tashi yunwa na neman kashesu suka hau ci kaman wainda sukai shekaru ba abinci.

Suna gama ci ko ruwa kasa fitowa su sha sikai sbd fargaba dan haka a hakan suka kwana yauma ledojin a cikin jikinsu suka kwana dasu.

Anne da sukaiwa bayanin Abinda yake faruwa tsorone yafara shigarta sbd ranar ra zaa ganesu take tsoro dan kuwa ranar ruwan masifar fa zaayi a gidan hakama shi kansa mutumin dake taimaka musun Ababan ba barinsa zaiyiba da balainsa dan haka ta ringa musu nasiha da gargadin su kiyaye su nesanta kansu da abinda zai qarasa kashe musu dan kwanciyar hankalin dasuke samu wasu lokutan idan masifar Ababa da hande ta kwanta.

Tamkar wanda aka wajabtawa haka Alh bilal kaman yanda su suke fada yafara sauya rayuwarsu daga wahalalliyar azababbiyar yunwa,
Kullum sai ankawo musu abinci a boye suke karba suna isa dashi gidan sunaci su da mahaifiyarsu wadda a yanxu ciwon yunwar daya gama cinye hanjinta yafara dan sakewa sbd a baya haka take kullum a mokade kaman ledar da aka jefa cikin tafasasshen ruwa.

Aduk sanda suke shigowa da cin abincin cikin masifaffen tashin hankali da firgici mai tsanani sike cinsa su gama dan kuwa sun sani na lahira sai yafisu jin dadi duk randa mummunan tsautsayi yasa kaddarar tonan asiri ya kamasu.

Shi kansa Alh bilal din daya sake fahimtar yanayin da suke ciki na ba qaramin taimakawa abincin ke musu ba daya fara fahimtar yunwar dake tareda sumayyah tafara sakinta kaman yanda likitan dake dubata yafada sai ya dage da ciyar dasu din a boye ta yanda shima nasa familyn basu san rayuwar daya jefa kansa ba.

A yanzu da ya zama kaman biyayyarsa shima kusan tilas ce garesu sbd kyautatawarsa garesu sai ya zama wani irin girma da darajarsa suke gani gashi shima din sai ya dena tinkararsu kai tsaye cikin mutane sbd fahimtar suka tsananin shiga firgici da tashin hankali idan yayi hakan dan haka haduwarsu sai ya zama a sirrance sukeyi.

Hawa Mashin din zuwansu makaranta daya tsana fiyeda komai sai ya siya musu napep kai tsaye sbd kaisu kawai da daukosu tinda basa son shiga motarsa koyaushe suka shiga cikin yanayi na mummuna suke dan haka wanda ya bawa napep din aikinsa kawai kaisu da dauko su.

Da farko tsoron hakan sukeji sosai sbd basu san yanda zasiyi da kudin mashin din da ake basu ba,
Basu iya boye kudi ba sbd ko sun boye basu san me zasiyi dashi ba tinda basu taba sakawa ransu tinanin guduwa subar gida ba bare su ringa boye kudin gashi idanma sun gwada boyewan tinda suka fara zuwa makaranta akai akai Ababa ke sawa hande tana bincikesu da kayansu dan haka basu taba tinanin boye wani abin ba ko ba kudi ba
Abincinmq dasuke shigowa dashi dan suna cinyewa ne a take dasun shigo dashi, dan haka kaman yanda Allah ya kawo musu mai taimakonsu a boye sai suma sike bawa wani tsoho makaho kudin a hanyarsu ta tafiya kullum sbd baida kowa shima yana cikin mawuyacin hali.

Tsohon daya gama wanyewa dasu kullum shima a duk lokacinda ya bude bakinsa Benazir yakewa addua sbd itace mai fitowa ta basa,
Adduarsa kullum Allah yakaita matsayinda bata taba tinanin zuwaba tareda rayuwa mai Albarka da kwanciyar hankali tareda zuria dayyaba.

Exams dinsu aka fara dan haka hankalinsu ya rabu sbd kowa karatunsa yake kokarin maida hankali akai musamman Benazir sbd lectures da dama data ringa rasawa a lokutan sbd sumayyah da ciwon datayi bayan nan dan haka idan suka shigo makaranta sumayyah bata sake ganinta sbd Sosai karatunta ya samu ci baya shiyasa ta dage sosai kafin ta fadi Ababa ya kusa kashesu su dukan gwara a samu mai taimakawa wani acikinsu.

Sumayyah da kanta ya daure matiqa sbd exam din farko da suka fara babu abinda ta gane sunanta kawai ta rubuta sai questions din data maimaita masa a booklet bayan question daya babu abinda ta amsa said ta fito idanuwanta cike da hawayen tausayin kanta da yanda rayuwa zatai mata idan ta gama shekarun nan biyu duka a fail,
Wane mataki Ababa zai dauka akanta?
Siyar da ita zaiyi ga 'yan qwaya da gaske ko me?

Inda suke zama ta nufa ta zauna ahankali tana sauke kanta qasa dukkanin jikinta na mutuwa hakama tsoron dake mamaye zuciyarta na qara bayyanuwa a kan fuskarta.

Haka ta jima a gurin tana saqa da warwara cikin damuwa har lokaci yayi suka sake shiga wata exam din nan ma kusan biredi ne ke dukan fanke bata tsinano abin arziki ba dan haka wannan karon tashin hankalinta da tsoronta qaruwa yayi sbd azabar datasha wancan karon data fadi exams din a hannun Ababa.

Tana fitowa kasa riqe zuciyarta tayi taje maboyarsu ta zauna hawaye na tsiyayo mata ta saka fuskarta tafin hannuwanta tana sakin kuka mara sauti gashi bazata iya fadawa Benazir ba ta sakata damuwa nata karatun ya fita kanta,
Bazata so hakan ba sbd ko yayane tanason Benazir ta samu kammala karatun da sakamako mai kyau.

Tana gurin zaune har yamma Benazir ta gama suka tafi gida a napep gurin komawarsu Benazir ta lura da yanayin Sumayyah din ta tambayeta exams dinta.

Kasa magana Sumayyah tayi sbd hawayen dasuka cika idanuwanta kafin tayi wata magana Benazir ta fahimci komai cikin damuwa da tausayin yar uwarta tayi shiru ta kasa cewa komai sbd itama tasan suna dagewa ne suyi karatun sbd azaba da hukuncin Ababa,ita kanta idan ta tina da azabar da zata biyo bayan faduwa jarabawar tashi hankalinta keyi bare Sumayyah data dandana azabar hukuncinsa na faduwan.

Shirun Benazir yasa hawayen sumayyah saukowa tana rufe fuskarta da hannuwanta sbd kukan dayake zuwar mata zuciya a karye.

Har suka isa gida kuka sumayyah din keyi itama Benazir kukan zucin takeyi jikinta a mace,
Mai napep na jiyesu suka nufi hanyar gida sumayyah na goge hawayenta dan kada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login