Showing 39001 words to 42000 words out of 183527 words
duk da ba dubararka bace tsarewar Allah ce.
Ita kanta Sumayyah tinda ta dawo makarantar take cikin damuwa da tsarguwa tareda kunyar dagowa ta kalli mutane sbd kunyar abinda yake jikin nata ganin takeyi kaman zaa ganeta.
Dan haka rayuwar makarantar ta zamar mata kaman wani sabon qunci da damuwa dan kuwa gabaki daya a muzance take cikin mutane,
Mummunan hali ta samu kanta aciki wanda ya saka rayuwar makarantar da karatun ficewa kanta gaba daya,
Tamkar mujiya haka ta koma acikin mutane,
Tin tana daurewa har takasa damuwa da qunci yayi mata yawa dole ta dena shiga mutane kwata kwata sbd itama ciwonta dake neman dawowa.
Hankalin Benazir tashi yayi ya rabu biyu akan karatunta da kuma Sumayyah din musamman yanzu dayake tana daukeda lalurar juna biyu.
Daga ita har sumayyar karatun acikin kwanaki kalilan neman lalace musu yakeyi ga jikin Sumayyah din ciwo yau gobe lafiya tin suna iya controlling abin suna boyewa har hande tagane sumayyah dai dale akwai abinda yake damunta bayan malaria da sukace.
Ana cikin wannan matsuwar da tashin hankalin sukai exam wadda daga Benazir din har sumayyahn babu wanda ya iya karatu bare rubuta abin arziki.
Ranar da suka gama exams wani babban tashin hankali ya samesu na rasuwar mijin Ms ayshansu wadda a ranar ta bar garin zuwa jos garin mijinta inda acan zaayi janaizarsa.
Wannan babban sabon tashin hankalin yasanya jikin Sumayyah rikicewa gabaki daya sbd ms aysha itace gata da mafitarsu dasuke gani itama ta tafi ta barsu.
A ranar sabon tashin hankalin kwanan zaune sukai duka su ukun babu wanda ya rintsa sbd a yanzu kam babu mafita sai wadda ubangiji zai sake aiko musu kokuwa dai qaddarar ce dai ahakan tazo musu.
Wannan karan kukan da Benazir tayi yafi na kowannensu tashin hankali da taba zuciya sbd itace take iya hango kowannensu ciwonsa dap yake da tashi wanda tasan suna juyewa shikenan ita kadai zaa bari da dawainiya da wannan quncin da radadin wanda daqyar itama wannan karan idan bata samu mental problem dinba,
Ya zasuyi da cikin sumyayyah?
Zatayi da babyn idan aka haifa?
Me zata fadawa ababa?
Me duniya zata fada akan babyn?
Tayaya takeda tabbacin Alh bilal zai waiwayesu?
Innalillahi wainna ilayhi rajiun.
Kuka tayi sosai wanda ya saka jikin Sumayyah da Anne sanyi dan kuwa sunsan ko a gurin azabar idan zasusha nata zai fi yawa sbd itace mai lafiyar da zatafisu jin radadi da ciwo tareda qunci mai yawa.
Sai dataji hawayenta har sun qafe idanuwanta ko buduwa basayi sosai ta dena kukan ta kallesu cikin tausayawa sbd a yanzu ta rungumi qaddarar cikin lafiyarsu da abinda zai samesu idan suka rasa hankalinsu take ji yana cin zuciyarta.
Tausayin tausayi akeyi tsakaninsu
Su suna tausayinta ita kuma tana tausayinsu da babyn da zaa haifa wanda zai taso cikin uquba da masifar da uwarsu ta taso aciki suma suka taso aciki.
Abincin dare ta fito ta dora tana gamawa tayi sallah ta fito ta hau wankin hande.
Sai goma da mintina hamshin ta shigo dakin ta tadda Annensu zaune tayi shiru tareda nisa cikin tinani idanuwanta na kan sumayyah wadda baccin wahala da dole ya fizgeta.
Qarasowa tayi ta zauna gefen Anne tareda zamewa ta kwanta tana yiwa Annen saida safe cikin dasashiyar murya.
Har kusan asuba Annensu bata rintsa ba tana zaune cikin nisa a tinaninda batama san me take tinanawarba,
Ita kanta Benazir har kusan asubar batai bacci ba sai daga baya ya dan dauketa bata jimawa akai kiran asuba ta farka ta fito.
Tare sukai sallar asuba dukkaninsu
Suna gamawa Anne da Benazir suka fito
Itama sumayyar daga baya biyosu tayi suka fara aikin gaba dayansu.
Sai 11 suka dan samu saukin aiki suka zauna suka ci abinci
Ko tashi gurin basu yiba amai ya subucewa Sumayyah mai qarfi sbd cikinta daya kasa karban abincin da suka cin.
Amai takeyi mai qarfi da sauti wanda yasa dukkaninsu miqewa suna rarraba ido,
Hande kuwa da sauri tayo dakin tana tambayarsu aman lafiya ne kuwa?
Shiru sukai tayita maganarta ta gaji ta tafi kafin Anne ta wuce da sumayyan dan tayata wanke jiki
Benazir kuwa gyaran gurin tahau yi ta kwashe ta wanke gurin fes da omo me qamshin ta goge.
Acan koda Anne ta wanke jikin Sumayyahn zazzabi da ciwon ciki mai qarfi ya rufeta saida Benazir tazo suka kamata suka kai daki
Take ta juye cikin ciwo mai tsanan koina nata jijjiga yakeyi.
Anne ta zauna da ita Benazir ta fita ta qarasa aikin tareda girkin rana tana gamawa suka zauna kan sumayyar wadda take cire rai da rayuwa.
Haka suka wuni da ita a daki cikin damuwa da mutuwar jiki
Haka kuma suka kwana da ita.
Washe gari ma haka suka kima wuni da ita jikin ba dadi sam sai addua ba wanda ya kulasu
Hande ma ido ta kawo ta saka musu sbd tasan ko zasu mutu Ababa bazai saka kudinsa yakaita asibiti ba dan haka ba ruwanta tinda ba lafiyar zata basu ba bazata iya yawon sanni ba.
********acikin sati biyu sumayyah gabaki daya ta koma kaman mai ciwon qanjamau sbd rama da rashin kuzari,
Ciwonta yaqi sauki sam kullum haka suke fama da ita,
Benazir da Anne ma kaman masu qanjamau din suma dan itace take ciwon amma ramar da zabgewar dukansu ne sukai babu me dubuwa acikinsu banbancinsu da ita kawai ita cikin ne yake ajikinta amma duk damuwa da kuncin daidai yake a zikatansu.
Har lokacin babu labarin ms aysha hakama ba na Alh bilal,
A kullum yanzu sallamar ababa da tarinsa tashin hankalin na fits hayyaci yake sakasu sbd sunsan yau da gobe bata barin komai.
Babban sabon tashin hankalin dasuka shiga shine fara bullowar cikin,
Ciki dai ya bullo bazai boyu ba,
Fitowa tsakar gida yanzu kam ya gagari sumayyah indai da rana tsaka ne sbd kada hande tagani ta sanar da ababa.
Idan sun lissafa daidai watan cikin uku kenan ake magana.
Ajiyar zuciya tareda numfashi mai zafi Anne ta sake tana kallan sumayyah da benazir ke cirewa farce sbd tsayi da sukayi da wata tsohuwar rezarsu da suka siyo kwanaki a hanyar makaranta.
Sanyi jikin Annen ya sake dauka suma sanyi jikinsu yayi ganin irin kallan da Anne ke musu cikin sarewa da sadaqarwa.
Ajiye rezar hannunta benazir tayi tana dafa hannun sumayyah daya dauki rawa ganin Annensu datake sake tsinkar dasu.
A hankali anne ta bude baki cikin sanyi tace
"Ya zamuyi da cikin nan na sumayyah daya fara bayyana?"
Kunsan cewan daga wannan watan cikin nan bazai taba boyuwaba,
Tayaya zaa hana hande da Ababa ganinsa,innalillahi wainna ilayhi rajiun" tafada cikin fidda rai daba dukkanin sauki.
Sunyi kukan har hawayensu ya dena fita dan haka idanuwansu sukai jajir Benazir ta dago ta kalli Anne zatayi magana idanuwanta ya sauka kan hande dake gefen dakinsu tsaye tayi mutuwar tsaye tsaban tashin hankali da firgicin abinda kunnuwanta suka jiyo mata
"Ciki a jikin sumayyah kuma"?
Miqewa tsaye dukkaninsu sukayi cikin firgici da tashin hankali mai girma suna kallan handen.
Sai data share mintina kusan shifa a qame kafin ta iya motsawa ta rufe idanuwanta ta bude ta sake taba kirjinta taji zuciyarta na bugawa daidai bata sume ba,
Tsikar jikinta je suka miqe gabaki daya sbd tsoro dan kuwa ita kanta tsoron maganar shigarta tayi tinanin idan ababa kawai yaji zancen.
Babu wanda ya motsa acikinsu tsaban tashin hankali da tsoron yau ranar da suke tsoro tazo.
Qafafuwan hande na rawa ta qaraso cikin dakin tana kallan sumayyah da cikinta yake bayyane dan qarami a jikinta
Bakinta ya dauki rawa da yankewar kalma tace
"Cikin haihuwa a jikin sumayyah,
Ciki dai ciki dai na 'dan mutum,Qalu innalillahi wainna ilayhi rajiun,
Benazir,Benazir yanzu daman cikin mutum ne ajikin sumayyah kuke boyo?
Meya kaiku?
Wace qaddarar ce wannan?
Uban waye yayi mata cikin?
A in?
Aljanun hauka ne suka shigeku duk ku dukan ko me?
Cabdijam,babbar magana,attt.
Babu wanda ya iya magana acikinsu sbd dai rana ta riga ta baci ba gyara.
Janyo sumayyah hande tayi da qarfi tana qara kallanta cikin kunya da baqin ciki da takaici tareda mamakinsu.
Numfashi ga koma saukewa sbd bata da bakin magana lamarin ya shallake tinaninta.
Fitowa tayi dakin a rikice ta zube tsakar gida tana sake sauke numfashi a jere sbd ita kanta kwatanta tashin hankalin da zaayi a gidan kawai tayar mata da tsikan jiki yakeyi.
Duk bayan sakanni sai ta sauke numfashi mai zafi tana kallan kofar dakin nasu dasuka kasa fitowa kaman yanda kowannensu wuta ta dauke masa babu me iya magana.
Kaman masu jiran sakamako haka suka kasa ko zaunawa dukkaninsu suna a tsaye har akai magrib sukai sallah babu wanda zuciyarsa ke harbawa daidai har handen itama ranar tana idar da Sallah ta fito tsakar gidan ta dasa kejera ta zauna jiran dawowar ababa.
#MAMUH#
#MARRIAGE#
#LOVE#HOT#LITTLE BENAZIR AMNAH KAANTE#DD KAANTE#ZAFIN KAI
ZAFAFA BIYAR🔥
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma
-FURAR DANKO
Billyn Abdul
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Send your Shedan biya Anan👇
09032345899
MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070
Yan Nijar kuma ga inda zaku biya👇👇👇
+22799643131
Zafafa🫶🔥🔥
22
*_Arewabooks@Mamuhgee22_*
Dagowa Anne tayi ta kalli Benazir da sumayyah tsawon mintina tana rasa tinanin kamawa kafin ta tsaida tinaninta akan Sumayyah dake dauke da juna biyun zatafisu zama cikin hadari idan suka fara cin dukan azaba.
Benazir ma tinaninta akan Sumayyah dake dauke da cikin yake sbd tsoron hadarin da zata iya shiga idan Ababa ya kasa controlling kansa.
Suna nan zaune akai sallar ishai suka miqe sukayi ba jira sbd basu sani ba ko idan ababa ya dawo zasu samu lafiya ko kuzarin yi din.
Hande ma miqewa tayi ta shiga dakinta tayo sallar
Tana gamawa ta sake fitowa ta zauna tana hadiye wani yawun tsinkewa sbd itama tasan tau balain sai Allah idan ba har akanta zaa dora laifinba tinda itace ya barwa saka musu ido akan kowane motsinsu ta sanar dashi halin dasuke ciki
Amma ace har sumayyah tayi gogewar sani wani namijin har yayi mata ciki bata fahimta ba kuma da alama ba fyade akai mata ba da bazasu boye ba kuma da tini Ababan ya qaddamarwa wanda yayi fyaden ko dan uban waye gashi ciki yanzu ya dauko hanyar girma suna gida daya basuda labari,
Ababa kafin tashin masifarsa mamaki ma kawai ya isa ya kashe masa jiki shi kansa.
Qarfe tara saura mintina shida Ababa ya turo kofar gidan ya shigo yana amsa waya hannunsa riqe da ledar lemu daya siyo zai sha.
Ganin hande zaune tsakar gidan tana kallansa tana masa barka da dawowa yasashi taqaita wayar yayi sallama ya kashe yana saka wayar aljihunsa yana amsa barkan datake masa yana gaidata itama.
Satar kallan dakinsu Benazir tayi tana jin shakkar fada masa itama sedai kuma dole ya sani dan idan bata fada ba ciki dai baya boyuwa
Ranar daya gansa da kansa idan ya qara girma kilan wuta zai cinnawa gidan ya kona su duka.
Shima dakin nasu ya kalla tareda bude baki ya daga murya ya kira sunan Sumayyah.
Lokaci daya a tare gabaki dayansu har Hande kansu yayi mummunan sarawa tareda bugawar zuciyar data kusa sakawa hande hearts attack sbd bata saba da wannan tashin hankalin tsoro da fargabar ba.
Su kuwa acan daki take jini ya tsinkewa Sumayyah mummunan bugawar da zuciyarta tayi tareda sarawar kai mai qarfi.
Benazir da Anne ma kusan kowannensu daqyar ya samu yawun hadiyewa sbd makoshinsu daya bushe take qam hakama yawun sun kafe basu ma ankara da jinin daya fara zubowa sumayyah ba wadda itama bata tsars lura da jinin ba sbd zuciyarta data tsinke.
Cikin mamakin rashin amsawarta da fitowarta ya juyo ya kalli Hande wadda ta kasa kallansa tana dan dauke kanta zuciyarta na sake shiga wasi wasin fada masa.
Kallan kofar dakin yayi yana matse fuska ya sake qwala kiran sunan sumayyar.
Daqyar da wani irin mummunan yanayi ta iya bude baki ta amsa kiran nasa tareda miqewa tsaye qafafunta na rawa ta nufi kofar
Sai alokacin su Benazir sukaga jini a kayanta da sauri Anne ta miqe tayi gaba Benazir ta tsaya bayanta suka sakata tsakiya sbd dare ne duk da akwai wutar nepa amma idan suka dan kakkare ba lallai yaga cikin ba harma da jinin sbd ba hijab jikinta tinda basu saba zama da hijab cikin gidanba sbd basuda sitira da yawa shiyasa suke lallaba wainda sike da.
Yanda suka jero masa kaman kashin awaki yasashi tsayawa da kyau yana kallansu cikin sake tsuke fuska da mamakin sabon salon nasu na samun guri.
Sun zuwa suka tsaya gabansa dukkansu kansu a qasa
Anne ce kawai ta dan kallesa tayi masa sannu da zuwa cikin girmamawa kafin suma cikin girmamawa mai tsanani sukai masa barka da dawowa.
Ledar hannunsa ya miqawa sumayyah yana cewa
"Ki gyaro lemu ne ki kawomin banason manyan yanka kuma kin sani......Maganarsa yankewa tayi ganin yanda hannuwanta ke tsananin rawa gurin karban ledar.
Janye ledar yayi yana kallan hannuwanta dasuka sake rikicewa da tsananta rawa,
Fuskarta ya maida kallansa fuskarsa na sauyawa da mamaki yaga fuskarta na hada wani irin gumi da kasa motsa idanuwanta dan kada su dago.
Kan Anne ya maida idanuwanta yana kallanta itama zufan take cikinsa sharkaf hakama hannuwanta rawa sukeyi harma da qafafunta.
Juyar da kallan yayi kan Benazir datake a kame batai gumin ba amma yanda kirjinta ke bugawa yana iya gani da kuma yanda takasa dogowar itama.
Wani numfashi mai zafi ya sauke bayan ya gama karance yanayinsu duka
Ya dawo da kallansa kan hande zaiyi magana yaga itama a jiqe take da zufan yau itama takasa dagowa ta kallesa da kyau.
Sake kallan kowa yayi acikinsu daya bayan daya
Gurin yayi tsit ko sautin numfashinsu baka ji
gyara tsayuwa yayi a hankali,
"Meyake faruwa zaa fadamun yanzu nan"...sukaji saukar muryarsa kai tsaye.
Idanuwansa akan Hande suke sbd daga bakinta yake buqatan ji menene dayasa take hada zufa itama.
Kallansa hande tayi kafin ta kalli sumayyah data riga ta saddaqar su dikan ma sun saddaqar din.
Maimaita tambayarsa yayi hakurinsa na qarewa sbd tini kansa ya fara daukan zafi.
Wani nannauyan numfashi hande ta sauke tareda kallan sumayyah a karo na farko dataji tausayinsu ya dan saukan mata a rai sbd tasan suma duk yanda akai mummunan kaddarar samunsu tayi bada son ransu sbd yanda suke tsoro da kiyaye dokokin Ababa bazasu taba irin wannan aikin da ganganba.
Muryarta ba qarfi da kuzari ta bude baki tace
"Ciki ne a jikin sumayyah gashinan harya fito".
Shiru gurin ya sake dauka wanda wannan karan har dashi Ababan ya dauke wutar ba zata sbd saukan zancen kaman tsawa me qarfi haka ya jisa.
Hande dataji shiru dagowa tayi ta kallesa taga yayi shiru kaman baiji abinda ta fada masa ba dan haka ta miqe tsaye tana kallansa cikin dan daga sauti takira sunansa tana cewa
"Kaji abinda na fada kuwa?
Nace Ciki ne a jikin sumayyah gatanan na haihuwa,
Da alama kuma zekai wata uku koma fiye,
Kuma wallahi tallahi bansaniba sai yau dinnan nake kamasu suna maganar,
Duk ciwon datake ta fama dashi duk tsawon lokacin nan ashe laulayin ciki takeyi bamu saniba daga uwarta sai yar uwarta suka sani sunata boyan abinsu da saidai idan an haihu munji kukan jariri a gidan mu ankara.....
Ledar lemun hannunsa data subuce masa ce yasata yin shiru tana kallan lemun dasuka watse tsakar gidan kowannen na ganganrawa nasa gefen.
Rintse idanuwansu dasukai jajir dukkaninsu sukai suna sauke numfashi mai dumi.
Ababa ma numfashin ya ringa jerowa yana kokarin sanyaya wutar data kunno cikin zuciyarsa tana cin jininsa sbd yasamu fahimtar komai daki daki akan abinda handen ke fada sbd yasan dai ciki a gidansa ba magana me yiyuwa bace sbd soyayyama ya fada musu sun sani bame yiyuwa bace haka hukuncinta me girma ne,yanzu kuma yaji ana maganar cikin haihuwar dan mutum a gidansa,
Wannan ba labarin da zai taba yarda dashi bane sbd bame yiyuwa bane acikin gidansa dai Kuma a tsakanin yayan nasa.
Gyara tsayuwa yayi yana sake calming kansa sbd Kai tsaye zancen Mai shigesa ba kafin ya kalli hande yaga lafiyarta kalau da alama ba soki burutsun zancen take ba,amma ai akwai tsufa a tareda ita Kuma tsufa nasaka zance mara kan gado,
Da Annensu ce ta fada masa da sai yace haukartace ta tashi.
Benazir dayasan gidan kaf ita kadai ce me cikakkiyar lafiyar qwaqwalwa ya kalla kai tsaye yace
"Ke Benazir fadamun meye hande take fada,kuma komai nakeson ji dalla Dalla ba irin wannan rikicin zancen data fada ba yanzu Kuma idan kika yiwa kowane zance kwaskwarima gurin fada wlh saina karya wuyan uwarki gatanan a tsaye gefenki."
Mutuwa jikin benazir yayi ta sake boyayyan numfashi mai zafi sosai ta dan dago kanta kadan batareda ta kallesa ba ta bude baki muryarta na rawa ba wahalarda Kai Kai tinda komai ya Riga ya fito Kai tsaye tace
"Eh ciki ne wata uku".
Shiru gurin ya sake dauka suna jiran wata tambayar saidai tsit ababan baice komaiba sbd har lokacin dai Bai yarda da abinda kunnuwansa suke jiba Dan kuwa ko Anne ta dauka cikinsa a yanzu dukan tashi Kisha ruwan gishiri zai mata bare,
Sai daya Dan gyara tsayuwa ya sauke numfashi Yace,
"Annen ce da ciki kuke magana kokuwa"??
Shiru sukayi zuciyar kowannensu na kokarin Faso kirjinsu ta fito har handen wadda take sake qarewa cikin na sumayyah kallo ranta na tafasa.
Jin shiru yasa shi dagowa kallo daya yayiwa Benazir tayi qasa da Kai qafafunta na sake daukan rawa tace,
"Aa ba Anne ba"
Cikin zafi da tafasan Rai a hasalce Yace
"Waye yake da cikin Dan a gidan Nan ita kadai Ce aure"
Saida Benazir ta fixgi numfashinta Dake Neman daukewa sbd tsananin tashin hankali da tsoron dasuke ciki na tinanin Ko Basu rasa ransu duka ba Kila sai daya ko biyu sun tafi lahira sun bar daya muryarta na fita da karyewa tace
"Sumayyah Ce ta.... Bata qarasa ba sai jin tayi ya shaqurota da hannuwansa biyu yana kokarin rabata da numfashinta da karfin gaske cikin wani irin zafi da fushin da basu taba ganinsa dashi ba da murya me qarfi da zafi yace
"Zaki fadamun komai danace kokuwa uwar taki kike jiran na balla,
Cikin mutane ne kokuwa na aljanu?
Dan kuwa sai dai na Aljanu suka shafeta sukai mata shi.
Cikin azaba da neman cetan ranta dayake neman rabata dashi tafara wintsila qafafu tana Neman barin duniya idanuwanta take suka firfito suna neman rufewa.
Wurgi yayi da ita qasa tareda saka qafarsa daya ya take cikinta cikin masifar data saka Sumayyah sakin qaramin fitsari jinin dayake zubar mata yana dan qara gudu sbd masifaffen masifar datafi qarfin balain da sika saba gani.
Cikin wahalalliyar muryar da bata fita sosai Benazir tace
"Na mutum ne a makarant ta hadu dashi,
Yace ze aureta,bamusan da cikin ba sai daga baya.... Marin daya saka bakinta fashewa da jini ya sakar mata na bayan hannu, take ta kife a gurin kunnuwanta na dauke ji kwata kwata haka idanuwanta na ganin wasu irin taurarin wuta jinin bakinta kuwa kaman wadda ta fasa kai.
Sumayyar ya damqo yana kallan cikinta zuciyarsa na