Showing 51001 words to 54000 words out of 183527 words

Chapter 18 - Zafin Kai Book One Complete Hausa Novel

Mamugee   

26 Oct 2025

311

Securityn ya Dan matsosa Yace

"Bismillah malam ko¿Mu Dan je daga waje sai naji abinda ya kawo ka zaa duba matsalarka,muje Bismillah.

Girgiza kai Ababa yayi cikin sake bayyanarda Yana cikin balai da masifar rayuwa Ya sake Maida kallansa kan Dd babba dayake shafa adduarsa daya gama Yace

"Ranka ya Dade Dan Allah ka saurareni,
Kai kadai ya kamata yaji matsalar data kawo ni,
Ina cikin tashin hankali da masifar da bazan iya kallan jamaa ba,
Ni nawa mutuncin ya Riga ya fara rauni a idan duniya,
Banda zabi ne shiyasa nazo Dan kaima kasa muguwar tsautsayi ko kaddara zance data faru tsakanin 'dan gurinku da 'ya.....

Bai qarasaba Dd ya juyo ya zuba masa idanuwansa masu kwarjinin arziki da dattako sbd a duniya idan akwai abinda Dd babba ya tsana Ji shine hada Kalmar
"wani abu ya faru tsakani"

Ababa kuwa sake qasqantar dakai yayi idanuwansa na bayyanarda hawaye masu bayyanarda radadi da zafi tareda quncin rayuwar tsaka me wuyar dayake son nunawa Dd babba Yana ciki.

Shiru Dd babba yayi tsawon mintina Yana nazarin Ababa da kukan dayake Yi a matsayinsa na dattijo kafin ya dago kalli Securityn Dake tsaye a kansu cikin nutsuwa Yace
"Ba komai kaje kawai"

"Yes Sir" Yace tareda kallan Ababa ya juya ya bar gurin ya fice masallacin gabaki daya.

Saida securityn ya fice gabaki daya
Dd babba ya Dan sake kallan Ababa Bai basa Daman magana ba sukai shiru sai da limamin masallacin ya gama nasa lazimin ya fice ganin alaman magana zasuyi Kila Mai mahimmanci musamman duk Wanda yasan Dd babba yasan baya wasa da tattali da Hana kowa yaji sirrin ahalinsa,
Bai yarda ko yayane wani yaji sirrin kaates ba sbd a yanda suka kafu Allah ya girkasu da sanin sirrinsu Kawai zaa iya ganin an rusa su,
A baya hakan yaso faruwa dasu Amma ya tsaya tsayin daka Allah ya taimakesa ya Hana matsalar rusa ahalin daya wahala yagina,
Ginin da har jikokin jikokinsa inshallah bazasu San meye talauci wahala da quncin Rashi na arziki ba saidai wata jarabawar ta rayuwa daga ubangiji.

Kalman Ababa ta cewa "wani qaddara ko tsautsayi tsakanin ahalinsa na kaantes da nasa" ya sakasa basa Daman sauraransa dan farajin koma menene idan ba mahaukaci bane lullube a cikin kaya Bai sani ba.


Bayan ficewan malam liman Dd babba ya Dan sake kallan Ababa daya share hawayensa hannuwansa na rawar tashin hankalin dayake tattare dashi da damuwa ya sunkuyar da Kai cikin rawan murya wani kukan na son sake zuwar masa Yace

"Ranka ya Dade 'dan gurinku Alh Bilal kaante Yana soyayya da 'yata bansaniba sai cikin qaddara kwatsam muka tsinta a jikinta,
Ranka ya Dade ku taimakeni kumin Rai wlh mutuwa zanyi idan ta haife wannan cikin a gida,
Bazata taba samun mijin aurena rayuwarta ta lalace,ta gurbace,ta nakasa,ta.....Jin shiru ba motsin Dd babba ba maganarsa ya Saka Ababan dagowa Ya kallesa kafin yaci gaba da bayaninsa.

Kallansa Dd babba keyi cikin wani irin yanayi na mamaki da Hana zancen kaiwa zuciyarsa bare shiga cikinta,
Yama rasa yanda zai juya zancen bare ya karba cikin Kansa Dan haka ya Dan sauke numfashi a hankali Yana Dan gyara zamansa sai alokacin ya Bude Baki cikin nutsuwa yace

"Meye sunanka?
Daga Ina kake?
Kasan Bilal kaante din Da kake magana akansa?
Ka taba ganinsa a zahiri?
Maana ka taba ganinsa tare da 'yar taka?

Wani zufa ne ya yankowa Ababa Amma Kuma a yanda ya zo ba gudu ba ja da baya wlh sai ankarba cikin yarsa ko kowa yasan Dan kaantes yawa yarsa fyade.
Dan haka sake tattaro nutsuwa yayi cikin daidaita murya Yace

"Sunana Ababa Sulaiman,
Daga kauyen bairi iyayena suke ni anan na tashi anan nake zaune da iyali na,
Alhaji Bilal din Kuma ban taba ganinsa ba a zahiri,
Amma ita ta san shi farin sani,
Ni dai rokona A yimun adalci ya duba lamarin sbd nine a cikin cutatarwa da qunci da bacin Rai,
'yata na asibiti yanzu haka Rai hannun Allah..


Shiru Dd babba ya sake Yi sbd zancan yafara basa mamaki da shakku Kuma,
Meye hakan yake nufi?
Ciki Bilal yaiwa wata ko me?
Sam ba halinsa bane,
Baya kula mata ma bare nemansu da fasiqanci,
Tayaya Rana tsaka haka kawai kaman almara kokuma aikin rashin hankali azo masa da zancen bama yanzu ne ake zarginsa da laifin kebewa da macen ba aa cikin ma gabaki daya aka zo da zancen har ansamu,

Wani nannauyan numfashi ya sauke zuwa lokacin zuciyarsa tafara sauyawa duk da haka dai zancen sam Bai shigesa ba bare karbuwa
Yafara saka Ababan a jerin batan hanya yayi kokuma ansamu kuskuren gurin zuwa sbd sunan Kila yazo daya da wani Bilal din ba nasu ba.

Amma baya garage Sam a rayuwarsa Dan haka komai nasa yake yinsa a tsari da lissafi Shima kaman Ababa saidai nasa lissafin daya baya wasa dashi shine akan suna da mutuncin ahalinsa, sbd yayansa uku duk Maza Babu qaramin mutum a cikinsu,har senator akwai aciki hakama jikansa daya Minister ne tayaya zai bari mutuncinsu da sunansu ya tabu daga shi har 'yayansa qasa zasuyi Harma da sauran jikokinsa Dake dake cikin lokacin nasu sunan da mutuncin tinda sun zama Manyan mutane suma Dan haka lissafi indai akan ahalinsa ne baya batan lissafi ko garaje.


Kallan Ababa yasake ya sake sauke numfashi Mai dumi kafin Yace

"Ba damuwa naji zancenka,
Zaa warware Maka kuskuren fahimtar da aka samu akan lamarin duka,
Bilal kaante dakake Ji daban Wanda yanzu kake magana akansa daban,
Allah ya tsare gaba ya kare Yakuma shirya mana yayanmu duka,
Wannan sabanin fahimta ne kayi.

Da sauri Ababa ya Bude Baki zaiyi magana Dd babban ya dakatar dashi sbd shi ko sunan zancan baisan ana dangantawa da Bilal din dan ma dah da DD aka danganta zancen bazai iya danne bacin ransa ba ko Hana fushinsa bayyana akan wannan mutumin.

Miqewa yai tsaye a hankali cikin nutsuwa Yace Ababan ya biyosa
Suka fice masallacin zuwa cikin gidan Kaantes din.

Abinda yasa zai tafi da Ababan dan warware masa fahimtarsa da tinaninsa akan ya cire zancen sunan kaante ne kwata kwata acikin zancen basuda alaqa ko daya da maganar.

Securities na ganin Ababa bayan Dd babba suka Dan taso Dan dakatar dashi Amma Dd ya dakatar dasu Yace su barsa kawai zai gansa ne.

Ciki suka shige Kai tsaye
Gate din na farko yasa hankalin Ababan tashi suna shiga gate na biyu asalin Inda harabar gidan take makekiya komai a tsare da kyau da aji kaman ya baro qasarsa yaji,

Motocin dasuka kunce masa lissafi yake kalla idanuwansa kaman zasu fado qasa,

Take lissafinsa gabaki daya kwata kwata ya kunce wlh bazai yarda ba cikin nan ya zube,
Idanma ya zube bazai yarda ba sai anbiyasa diyyar keta haddin yarsa da dirka mata cikin farko ba aure.

Wata firgita ya sake Yi lokacinda suka Isa office din Dd babban Dake cikin gidan Dake gefe daya daga bangarensa dayake farko farko.

Sanyin Ac daya tarbesa yasaka shi Saka lissafin Ac take a budget dinsa na gaba cikin abinda zaa kasafto masa.

Italian office set din dasuka qayatar da palon yake kalla Yana sake kokarin yaqi da Hana zallan zalamansa fita ya danne Kansa da nutsuwa da kame Kai.

Gurin zama Dd babba ya nuna masa daya daga cikin kujerun alfarmar Dake jere.

Zama yai Yana sake Satan kallan wata drawer dafi komai tsayi da wani glass a office din zuciyarsa na kissima masa Kila uwayen daloli ne a ciki.

Numfashi Dd babba yasake sakewa a karo ba adadi tin farkon Jin zancen dake tafe da Ababan kafin ya miqa hannu kan wayarsa Daya bari kan stool na set din kujerun dakin dazai fita sallah take ya nemo numbern Bilal ya Saka kiransa.

Yana dauka Kai tsaye Yace ya samesa Daman yasan da dawowansa Bai nemesa bane Dan ya bari ya huta kafin su zauna maganar aikin dayayo acan tsawon watannin biyu.

Jin Bilal aka Kira yasa Ababa Jin fargabarsa ta fada Dan kuwa gwara ayita ta qare din
Dan tin farko da yasan ya dawo ai shi zai fara tinkara kafin su qaraso gurin Dd din.

Shiru sukai Babu mai magana kowannensu yayi Nisa a nasa tinanin da shakkar yanda zata kasance.

Shidai Dd babba fatansa daya kawai duk tsanani kada ma ya kasance Bilal yasan wanna mutumin bare 'yarsan dayake magana Akai,
Zaifi farin cikin ace anzo masa da labarin sunyi asarar miliyoyin kudi masu yawan gaske akan wannan labarin ya sake kasancewa a zuriarsa,

Ya karbi jikan farko ta wannan hanyar bazai yarda ya rungumi tattaba kunnen farko ba ta wanna qaddarar sbd wani tabo da ciwo ne Mai qarfin gaske da haryanzu yake dandana ciwonsa duk da qaddarar ta banbanta da wannan.

Ya kasa karba Bilal zuciya Dari bisa Dari sbd baida shedan auren da 'dansa ya daura boye da mahaifiyarsu Bilal din farko har aka samu cikin,

Madaurin auren ya mutu masu shedan auren sun mutu tayaya zai yarda da auren nasu?

Ya kwato mutunci da sunansa daqyar yayiwa zancen lullubi da wata irin dukiya Mai yawan gaske da har kullum yake shakkar fitarsa sbd baisan ta wace fuska mutane zasu karbi matsayin Bilal din ba jikansa na farko,A matsayin Dan gaban fatiha ko a matsayin Dan Sunna.

Wannan dalilin nasa yasa har ko yaushe DD ne asalin Wanda zuciyarsa ta karba ta riqe bari bisa Dari fiyeda duka sauran jikokinsa sbd Saida ya sake daura auren Fatima da dayyab din tukuna hankalinsa ya karbi auren nasu kafin haihuwa DD da sauran kanwarsu.

Ta Ina yanzu zai fara da wannan Shima idan ya tabbata cikin ne daga ahalinsu wannan mutumin yake magana.
#MAMUH#
For more pages Kuyi joining VIP or Arewabooks

#DD KAANTE
#BENA ABABA
#CRAZY
#LOVE/MARRIAGE/ROMANCE
#SUMAYYAH ABABA
#BILAL KAANTE
#ZAFIN KAI
#MAMUHGEE

*_Arewabooks@Mamuhgee_*
29
Zaman shirun yake sake girmama tinani da burikan Ababa game da lamarin komai ya sauya na lissafinsa Kuma,
A yanzu baida burin daya wuce su karba cikin kawai ya Dora sharidansa kai tsaye ba batawa juna lokaci.

Dd babba zuwa lokacin jininsa yafara kokarin Hawa Amma dayake jajirtaccen mutum ne Mai qarfin zuciya da Iko sai ya danne ya Hana Kansa karban zancen Tako Ina daga zuciyarsa har cikin Kansa.

Bilal kawai yake jira a datse zancen ya sallami mutumin tareda gargadin ko sunansu karya sake shiga cikin zancen ko gun Bada labari ne na yayi sabanin fahimtar zuwa gurinsu.


Knocking kofar da akai yasa gaban Ababa daka tsalle zuciyarsa na tsinkewa take shakku da fargaba Kuma Mai tsanani yashigesa na abinda Bilal zai fada akan cikin yanzu shine zai tabbatarda matsayin samunsa da rashinsa yanzu kam,

Dan idan Bilal Yace Bai san sumayyah ba kokuma cikin to tabbas ta tabbata daga yau yakoma Nobaba,
Idan Kuma Yace yasan da sumayyahn ko Bai san cikin ba wlh sai sun karba Dan ko ba nasa bane sai ya maqala musu kafin ya koma gida su fuskanci juna shi da sumayyahn Harma da uwarta da Benazir.

Shi kansa Dd babba sai daya sauke numfashi ahankali Mai sanyi kafin ya Bada izinin shigowar.

Kaman yanda suka tsammata Bilal dinne
Gabaki dayansu idanuwansu akansa suna kallansa a tare kowannensu da fata da abinda yake buqatan Bilal din ya tabbatar.

Shi kuwa Bilal hankalinsa akan Dd babban yake sbd baisan Ababan ba Dan Bai taba ganinsa ba sai so daya Kuma da yamma ne daga nesa Dan haka Bai qarar da kamanninsa ba dan haka Yana shigowa cikeda nutsuwa da ladabi ya qarasa ciki ya Isa gaban Dd ya zauna ya gaidasa cikin girman da nutsuwa kaman yanda ya saba.

Numfashi Dd ya sake saukewa kafin ya amsa gaisuwar cikin kulawa ya masa barka da dawowa.

Amsawa yayi Yana kokarin danne tasa damuwar da tashin hankalin dayake ciki na zancen sumayyahn sbd baisan ta inda zai bullo ba Dan yasani Babu maganar karban wannan qaddararriyar maganar a cikin dictionaryn Kaantes din Dan haka yake cikin tsaka me wuyan da baisan Ina zai Saka Kansa Harma da sumayyahn ba.

Gyara murya Dd babba yayi da kyau cikin nutsuwa kafin ya fara da cewa

"Ga bako Nan a bayanka zaune ka duba da kyau ko ka Sansa Dan bakon kusan na ke."

Juyawa yayi cikin nutsuwa ya kalli Ababa ya gaidasa jiki a mace tareda dawo da kallansa ka Dd babba Yace

"Ban Ganesa ba gaskia sai an tinatar Dani."

Magana Ababa zaiyi Dd babba ya daga masa hannu fuskarsa ba sauki ko sakewa ko kadan
Take kwarjininsa ya cika masa Ido gabaki daya dan haka dole yayi shiru zuciyarsa na sake tsinkewa da zancen da Bilal yafara dashi.

"BILAL" Dd ya kirasa Yana kallansa Kai tsaye da son tabbatar masa mahimmanci maganar da zaiyi masa.

"Na'am"
Shima ya amsa cikin nutsuwa da jikinsa dayake bayyanarda sanyinsa a yanzu.

"Bilal wannan bawan Allah gashi Nan yazo tin safe Yace Yana son ganina bai samu damar ba sai da magrib ya Dana fita ya sameni a masallaci da wani babban zancen daya sami yarsa,

Magana yakeyi akan 'yarsa ta hadu da tsautsayin qaruwa ta juna biyu Kuma Wanda yakeda alhakin hakan sunansa Bilal.,

Yazo ne Nan akan Kai Bilal din yake zargi da hakan kokuma Nace yazo ne kan 'yar tasa ta basa tabbacin ka Bilal kaante din ne yayi mata wannan cin mutuncin.

Tinda Dd yafara maganar maqoshin Ababa ke motsi kaman ya karbi zancen ya qarasa sbd ganin Dd babban yakasa fitowa ka tsaye yai maganar data Tara su din sai alokacin da yakai qarshen maganar Ababan ya saki ajiyar zuciya a boye Yana zubawa Bilal idanuwansa kirjinsa na harbawa da jiran amsar dazai Bada.


Sunkuyar da Kai Bilal yayi ahankali a karo na farko dayaji kunyar Kansa data Dd babba Harma data iyayensa da basa gurin,
idan har wannan shine Ababa mahaifin sumayyah to tabbas komai ya Riga ya bayyana gaban Dd Babu sauran tsimi Babu dabara.

"Sumayyah sunanta,nine Ababa mahaifinta"...suka Ji muryar Ababan Yana fada Shima muryasa na rawa sbd matsiwa da fargaba.

Wata sabuwar kunya da damuwa Mai qarfin gaske Ce ta lullube Bilal a gurin Dan kuwa ya tabbata dai Ababan ne yazo gurin Dd babba da zancen.

"Innalillahi wainna ilayhi rajiun"
Wannan shine iya Kalmar da ya iya furtawa cikin zuciyarsa Dake harbawa da karfi.

Jin shirun Bilal da yanayinsa daya bayyanar da tsananin kunya,Dana sani da baqin ciki ya kasa dagowa ya kallesa yasa Dd babba tsayar da kallan sa akansa Yana jiran amsarsa.

Cikin kame murya fiyeda farko wannan Karan dan sirkin zafi kadan a sautin Yace

"Kayi magana a sallamesa ba zancen batawa Kai lokaci tinani bane,
Idan baka sansuba ba buqatan tsayawa nazari ko wani tinanin
ka fada Kai tsaye a sallamesa."

A karo na biyu ya sake Jin hawaye game da kaddara sun ciko idanuwansa duk da kasancewarsa babba bame qananun shekaru ba Amma Kuma tinda komai ya zo a qaddarawan ubangiji baida kaucewa bayan fadan gaskiar.

Ba iya dago Kansa ba yakalli Dd babba ya Bude bakinsa cikin Rauni Yace

"Na Santa,Kuma qaddara Ce ta gifta Banda niyar cutatarwa ko keta mutuncinta,
Da niyar zan aureta na bibiyeta tin farko,Ina matiqar Dana sani da Bada hakuri ga wannan qaddarar data shigo.

A jejjere Ababa ya ringa jero ajiyar zuciya a boye Yana hamdala kala kala ga ubangiji Yana Jin wani farin ciki da sanyi na mamaye ransa.

Bai taba sakawa sumayyahn albarka ba sai yau din yaji zuciyarsa na Saka mata albarka da Bata fada masa karya ba,
Tinda dai Bilal ya tabbatarda ciki nasa ne ai komai ba zai zo da sauki.


Dd babba kuwa shiru yai Bai iya cewa komaiba
Suma duk sukai tsit gurin ya dauke sauti ko motsi Babu.

Minti kusan hudu a hakan kafin Dd ya motsa ahankali ya dauki wayarsa ya Saka kiran Abbakar yaransa tin na shekaru har yanzu.

Abbakar din na dagawa Dd Yace yazo yanzun nan.

Ajiye wayar yai Yana kokarin Hana Kansa bayyanarda attack din daya riskesa take a gurin Saidai daga muryarsa Bilal yagane ya samu attack take ya miqe da sauri yai Kansa Yana Kiran sunansa cikin kulawa
kafin wani yunqurin tini numfashin Dd din ya fara kokarin daukewa saiga Abbakar Yana ganin hakan hankali tashe yayo Kansa Shima.

Ababa ma hankalinsa tashi yayi ya miqe tsaye Yana fatan kada komai ya samu Dd babban a samu matsala Dan haka dashi aka hau yi masa firfita Bilal kuwa likita ya fara kokarin Kira hankalinsa a matiqar tashe.

Cikin mitinan da Basu wuce qalilan ba tsohon yake Neman rasa ransa Dan haka kasa jira sukai take Akai kaante specialist dashi.

Ababa kuwa silalewa yayi dole ya tafi gida bayan an dakatar da kowa shiga Inda Dd babban yake.



Kai tsaye gida ya wuce Baima samu biyawa asibitin ba Dan jikinsa koina ciwo yake Shima yau din yaci wuya Amma tinda dai buqata kusan ta samu shiga komai yazo da sauki.

Anne data kusan haukacewa a kwana daya da wuni biyu sbd rashin ganinsu benazir da rashin sanin wane Hali sike ciki yasa gabaki daya Bata hayyacinta gashi Ababan yaqi fada mata komai bare taji dan sanyi aranta.

Dan haka ma da Daren yana shigowa ya shigewarsa ko abinci Bai samu damar ci ba ya kwanta sbd gobe sammako zaiyi zuwa asibiti da Kansa zaiyi jinyar sumayyahn shi da Benazir.


******A asibiti kuwa sumayyah da Benazir sun Dan samu sassaucin zuciya Dana jiki tinda basa aikin komai sai zama da bacci,

Tinanin Anne ne kawai yake tsananin damun benazir ita datasan halin data barota
Amma koma yayane tinda bataji Ababa Yace ta mutu ba to tasan tasamu tsira kenan.

Sunyi ta zuba idon dawowan Ababa Basu gansa ba har suka kwanta dan haka suka fara addua da fatan Allah yasa lfy ba wata masifar Ce acan gida annensu take Sha ba.

Jinin da aka Saka mata ishashe da magani masu kyau da lafiyayyan abinci wadatacce Harma da gurin kwanciyar me kyau yasa jikin sumayyah samun sauki Sosai tanata samun bacci.

Benazir kuwa ganin samun saukin sumayyah yasata Jin samun saukin zuciya itama dan haka suka dasa jiran tsammanin mekuma zai faru gaba.

Qarfe Tara na safe Ababa ya shigo dakin nasu da aka sauya musu wata nurse ta rakosa tana fada masa Wanda ya Saka a sauya musu dakin sbd Bai saniba shi bayanan.

Dakin yaqarewa kallo Yana mamaki da lissafin kudin da Bilal din ya kashe musu daga jiya zuwa yau din.

Baqin ciki da takaici ne yazo masa wuya ya tsaya wato dai ta tabbata yaran na sun jima suna cin arzikin Bilal baida labari.

Benazir data miqe daga zaunen datake ta gaishesa kanta qasa ya jefawa wani irin kallo zuciyarsa na tafasa ya jefeta da ledan ruwan tea da bread din daya siyo musu Dan karyawa.

Tanaji ruwan zafin ya Sauka qafarta Allah yasa ledan Bai fashe mata a kafa ba dan haka ta durkusa ta dauke ledan tana sunkuyar da Kai.

Sumayyah na ganin hakan ta rakube kan gadon tana jiran nata jifan,

Zaiyi magana aka bubbuga kofar dakin aka shigo.

Sulaiman ne tareda maaikancin babban hotel din kaante bangaren restaurant dauke suke da Manyan ledojin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login