Showing 162001 words to 165000 words out of 183527 words
dake asibiti kaf acikinsu babu me sauran amfanin da zai iya magana bare yasani ko ma ya fada inda Bena ta tafi.
Safnah ma dai har tsawon kwanakin Bata farfado ba sbd ba qaramar buguwa kanta yayi ba.
Ababa duka qafafunsa biyu babu me Aiki dayan bullet ya lalata dayar itace ta karye tin gidan DD babban baqin rayuwarsa da quncin Daya dabaibaiye rayuwarsa shine yau ko qafafun da zai iya daga Kansa tsaye baida,
Hande ta mutu ta bar duniya,
Ga hukuma na jiran su warke ayi gidan yari dasu ita momy ma da Safnah akwai yiyuwar ratayesu zaayi da ransu suna ji suna Gani su mutu Subar duniyar,shi kalan nasa hukuncin kuwa Kila life in prison ne sbd dumu dumu ansaka sunansa cikin tare suka maumalan qwayoyin da aka kama momy dasu Dan haka shi tasa mummunan qaddarar ta qarew yari ce har mutuwa da qafafu biyu babu ko Daya.
Daya Tina Hakan Wani irin Kuka yake fasawa wanda ke saka jikinsa daukan rawa Yana Rasa ta yanda wannan mummunan kaddarar ta samesa,Jin yake dama shine ya mutu ba hande ba ya huta da wannan biyu babun.
*********Koda Akai sallan magrib Saida likita yazo ya duba DD sbd jikinsa dake tsanani,
Bayan tafiyan likita daqyar Anne ta sakasa yaci abinci yasha magani.
Hakanan ya daure ya fita sallan magrib masallaci daga can Bai jiraba kaman yanda dd babba keyi wasu lokutan na tsayawa jiran sai anyi ishai ya baro masallacin gaba Daya.
Bedroom dinsa ya nufa Kai tsaye ya tube tareda sakarwa Kansa ruwan sanyi sbd ciwon Kansa ya rage ya samu Jin sassauci.
Ya jima Yana cikin ruwan kafin ya gama ya fito daure da towel fatar jikinsa tana Wani irin kyallin daukan Ido sbd duk yanda yake cikin tsananin damuwa da quncin zuciya fatarsa da kyansa suna Nan saima daukan Ido Dayake qarawa sbd rashin fita.
Yau jallabiya ya saka da hula ya Kalli time yaga lokacin sallan ishai yayi har na fara ya fito a natse cikin kamewa Yana nufar hanyar fita.
Yana kawowa sashen ummensa da a hango fitar Nafisat daga sashen tana nufar gate zata fice.
Kallawa yayi a natse ya Gane ita din ce Dan haka wayarsa ya fitar Kai tsaye ya kira Naseer yace yabi Nafisat gatanan ta fita Kaantes.
Naseer alwala yayo zashi masallacin Amma ya juya ya nufi hanyar babban gate na fita Kaantes
Yana fita ya hanga har tayi Dan nisa Dan haka bicycle din securities na gidan da ake zagayen gidan da ita da daddare sbd tsaro ya janyo ya hau yabi bayanta Yana kafe idanuwansa akan inda tabi.
Dap da zai cimmata can nesa da kaantes ta baya yaga napep tazo gabanta ta tsaya sukai kaman sunyi magana inda ze kaita cinikin beyiba ta jefa masa jakar dake hannunta a bayan napep din yaja y wuce ita Kuma sai datai tsayuwar mintina kusan biyar kafin ta juya ta dawo gida.
Naseer bayan napep din ya ringa bi da Keke Yana hanasa Gane ana binsa.
Dagowan tafiya sukai har sulaiman ya Isa gidansa yayi parking din napep dinsa ya fito ya shiga baya ya Ciro jakar da Nafisat ta jefa masa tambayar ta passport din Bena ya shige gida dasu.
Naseer da ba qaraman gajiya yayi ba da tuqin keken tini ya hada uban zufa guri ya nema a nesa da gidan ya ajiye kekan ya fara sauke numfashi tsawon lokaci kafin ya dawo daidai ya fidda wayarsa tukuna ya turawa DD sakon inda yake kawai.
Yana gama tura masa sakon ya saka wayar aljihunsa ya nufi masallacin anguwar ya sake alwala yashiga sallan da beyiba.
Kaman Wanda yayi gudun fitar Rai Yana sallame sallah DD ya iso gurin Dan haka Shima motan ya shiga suka zauna suna gadin gidan sbd koma menene Nafisat ta bawa me napep din dole akwai inda ze Kaisa sbd nan gidan Daya shiga matarsa da 'yayansa biyu ne a ciki a yanda Naseer ya tambaya cikin masallacin.
Kaman ma barayi haka Suka dasa zaman Jira a motar ga zazzabi sosai a jikin DD Dan haka dole Naseer ya mayardashi gida ya dawo shi ya dasa zaman Jira.
Har asuba Yana gurin a gabansa sulaiman ya fito sallan Asuba Shima ya fito suka shiga masallaci a tare sukai sallah da zasu fito ne sulaiman ya fidda wayarsa yakira Wani yaronsa Dayake napep yace yazo ya karbi napep dinsa yakaisa Tasha zaiyi tafiya zuwa Abuja yau.
Naseer na Jin Hakan ya dakata cikin masallacin Saida sulaiman ya shige gidansa.
Kallan man Dayake cikin motarsa yayi yaga tabbas ze Kaisa Abuja Dan haka wayarsa kawai ya dauka ya turawa DD sakon zaibi Naseer din Abuja tukana yaga wane abune Nafisat ta Basa kuma waye zaa Kaiwa.
*****Qarfe 7 sulaiman ya fito daga gidansa rataye da jakar matafiya tareda matarsa data biyosa har waje tayi masa Allah ya tsare hanya ta koma Shima ya shiga napep saurayin Daya kira yazo suka shiga napep din ya jasa zuwa Tasha.
Sai dasukai Nisa sosai Naseer ya tada motarsa yabi bayansu har cikin Tasha Yana kallo ba jimawa motan da sulaiman ya shiga ta cika ta tashi ta fito zuwa Abuja.
Naseer Kansa ya manta yaushe rabonsa da tuqin doguwar tafiya sbd jirgin dasuke Hawa sai yau din.
Sosai yake tattare da gajiya sbd ga kwanan mota ga tukin keken da yayi hakama ga doguwar tafiyar
Dan haka Koda suka Isa Abuja yamma tayi hakama ya matiqar gaskiya sosai Shima kaman zazzabin yake ji Amma haka yayi karfin halin bin motar har ta sauka passengers duka firfito harda sulaiman ya dauki drop ya kama hanyar gidan Bilal.
Saida Naseer yaga har gidan da sulaiman yayi ringing kofa ba jimawa aka Bude Wanda ya Gani je ya sakasa kusan somewa a motan Daman ga yanayin Dayake Dan haka da qyar ya Ciro wayarsa ko Gani bayayi sosai ya turawa DD address da house number na gida tareda saka sunan Bilal kawai karshe.
DD da tinda ya samu sakon Naseer yake kiransa baya samunsa har yamma tayi Jin yakeyi kaman zai qarasa zaucewa
Yana fitowa sallan magrib sakon Naseer na qarshe ya shigo masa dakatawa yayi cak da inda yake tareda qara Karanta sakon kusan so uku kafin ya juya kawai ya nufi sashensa ya dauko Abinda zai dauka ya fito da Kansa yakai Kansa airport ya Siya ticket cikin dare Saida ya Bata kusan awa biyar zuwa shiga a airport din kafin ya samu jirgin zuwa Abuja.
Duk yanda yaso Bai samuba sai qarfe 7 na safe Shima ya samu iso masaukin Naseer Wanda ya kwana cikin matsanancin halin zazzabi me qarfin gaske Amma ba laifi lokacin ya warware.
Qaramar tsadaddiyar luggage dinsa ya ajiye a dakin Naseer din alwala da sallah kawai yai bugun zuciyansa na qaruwa sbd har lokacin be Gane sakon Naseer ba sosai hakama babu Wanda yasake maganar komai acikinsu Yana idarwa karfe 8 suka fito Kai tsaye da mota Naseer ya nufi gidan.
*******Jikinta yayi Dan sauki sosai akan jinyar datasha ta kwanakin,jinyar jiki data zuciya wadda har yanzu ta kasa cirewa ko kasa tinaninsa a zuciyarta sbd mutuwace kawai tasan zatayi yafita ranta.
Anne da sumayyah harma da Bilal duk Wani kulawa da tattalin dasuke Bata Basu iya cirota daga damuwa da radadin zuciya ba saidai suna iya kokarinsu gurin ganin sun kula da ita din musamman sumayyah data San duk Abinda ya faru Bena ta fada mata Dan haka Suka taru suka boyewa Anne maganar Safnah din Dan gwara abarta akan yarda da Safnah ta Dade da mutuwa kawai akan baqin cikin dazata shiga idan taji Abinda yake faruwa.
Shikuwa Bilal ya yanke shawarar su tattara su dukan su koma Canada ne sbd tashin hankalin rikice rikicen da aketa Yi a Kaantes kafin hankali ya kwanta Bena din ko zata samu sassaucin halin Datake ciki shiyasa ya buqaci passport dinta.
Da safen sumayyah da momyn Abdul ne kawai a palon suna hada dining se Anne data fito da Bena wadda tayi fari fayau ta Dan rame Sosai,
Sanye take da Riga da wandon bacci masu tsantsi da hula qarama akanta Anne ta kamota cikin kulawa riqe da hannunta ta fita da ita Dan ta daure tayi breakfast tareda su sbd tsoron kada yunwa Kuma tai mata illa.
Knocking kofar Akai kafin momyn Abdul taje ta Bude Kai tsaye aka Murda kofan aka Bude Kai tsaye daidai fitowan Bena da Annenta daga bedroom din Dayake na Bena din yanzu.
Akanta idanuwansa suka fara sauka ita kuwa abinda ya Saba sanar mata da wanzuwarsa a guri ya shiga hancinta cikin Wani mummunan sanyin jiki ta juya ta Kalli kofan idanuwanta suka sauka kansa.
Shikam tsaban Abinda zuciyarsa ta kasa riqewa bare yarda dashi ya Tako cikin rufewan idanuwa batareda damuwa da duk Wanda yake gurinba Kai tsaye yana isowa ya kamota ya hade fuskarsa da tata cikin tsananin budewa da fallasa zuciyarsa ya hade bakinsa na nata hawayen Daya kasa riqewa kaman Wani baby suka fara gangaro matsa.
Daga Anne har su sumayyah da Momyn Abdul din dake palon mummunan tsoro ne ya kamasu ganin Abinda Basu taba ganiba.
##MAMUH#
*_Arewabook@Mamuhgee_*
92
ZINNIEE’s SECRET
(One stop shop for a new sensation)
Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓
Shin kina Neman kamshi da dada❓
Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki
Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.
Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar……
Room freshener
Toilet spray
Bed spray
Dish wash
Mopping mist
Kai har ma da
Feminine wash
Akwai
Glowing soup dinmu mai kyau da inganci.
Glowing cream
Face cream da kuma body scrub
domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret
Zinniee’s secret DUNIYA ne !!
Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret
TIKTOK@ Zinniee’s secret
Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number.
Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.
Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.
Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
********
Yanda yayi mata kyakyawan rungumar da yanda ya hade fuskansu da yanda yake kissing nata hawayensa na gangarowa daga cikin kyawawan idanuwansa tini ta kasa hanata Kansa ko kwacewa daga garesa sbd ita kanta ganinsa ya zo mata ne kaman a mafarkin da Bata taba kawowa a kusa ba,
Ta Riga ta cire Rai daga ganinsa har abada sbd tinanin ya haramta gareta,
Ganinsa da jinsa a jikinta yanzu ya tabbatarwa da zuciyarta bazata taba iya rayuwa babusa ba a ynzu shi din wani tsoka ce a kirjinta da bazata taba iya fitaba.
Ita kanta hawayen ne masu sanyi suka gangaro mata idanuwanta na rufewa ahankali hakama jikinta na sakewa gaba Daya a jikinsa sbd kasa yarda da ganinsa ya taho gareta.
Sake rungumeta jikinsa yayi dakyau Yana qanqameta tareda zare bakinsa daga nata Yana sake qanqameta dakyau Yana jero ajiyoyin zuciya hawayensa na kasa tsayuwa sbd sai alokacin ykejin kaman zai tsaga kirjinsa ya mayar da ita cikinsa gaba Daya ya boye ya Hana kowa da komai ko taba ta bare a sake rabasa da ita.
Shiru palon ya dauka babu Wanda ya iya magana babu Wanda ya iya motsawa Anne dake gefenta tsaya tini ta saki hannun Bena din dayake riqe a hannunta tareda matsawa gefe kadan sbd kaman bema lura da kowa a palon ba bare ita Datake riqe da Bena din,
Sumayyah da momyn Abdul Kallo dai sukai masa tin Sako Kansa palon suka fahimci shine DD qanin Bilal sbd kamarsu datai yawa.
Naseer daga kofar ya tsaya bayan shigewarsu Yana tura kofar palon ya rufe ya tsaya Yana Dan dauke Kansa daga kansu Bena din sbd Daman yasan zaayi Hakan sbd DD shi Sam baisan Yaya akeyi ko control na Kai akan lamarin da duk ya shafi Bena.
Ita kanta Bena din sai da suka jima a Hakan tsaye kafin ta Tina da akwai mutane palon ta Dan bude idanuwanta da sukai jajir tana zamewa daga jikinsa ta dago ta kallesa gabaki Daya idanuwansa dasukai laushin rashinta ya zuba mata tareda sake Kai bakinsa yayi kissing idanuwanta ahankali kafin ya dawo yayi kissing hancinta da kumatunta duk a hankali daga qarshe ya sake mayar da ita jikinsa ya rungume Yana Bude baki cikin Wani raunannan sauti yace
"Karki sake barina ko me Wani zai fada Miki,zan baki kariya ke da Annen ki, please karki sake barina,I love you,I love you"
Kasa motsawa tayi sbd kalmominsa dasuka shigeta jikinta ya sake mutuwa ta dago hannuwanta ta zagayesa dasu tareda qanqamesa tana sake shigewa jikinsa.
Kaman daga sama Bilal ya fito daga hanyar bedroom dinsa sanye cikin jallabiya fara da wayarsa a hannunsa Yana qarasowa cikin palon Abinda ya fara girgiza zuciyarsa shine qamshin da babu Wanda ya sani dashi sai mutum Daya a rayuwarsa shine DD kaante,shine ya fara shiga hancinsa shigowansa palon tareda girgiza masa zuciya a tsanake ya qarasa cikin palon ya tsaya cak daga inda yake Yana zubawa DD idanuwansa da tini suka sauya zuciyarsa na mummunan harbawa da bugawa.
Naseer Daya fara lura da Bilal din Shima kusan wutace ta daukewa jikinsa sbd jiya ya kasa yarda da cewan da gasken Bilal ne ya Gani,
Ya dauka idanuwansa ne,kenan tabbas shine,
Bilal kaante na Raye kenan?
Da sauri cikin tashin hankali ya Maida kallansa kan DD Wanda yasan zai iya samun bugawan zuciya ya sume idan yaga Dan uwansa Bilal a gabansa a Raye Dan haka ya Dan Tako kadan ya matso kusa da DD din Dan Incase kafin ya Dan Bude murya dake rawa ya danyi gyaran muryar daqyar tana yankewa ya Bude baki cikin yayyankewan kalamai ya ambaci sunan D din ya nuna nuna masa bayansa.
Budewa idanuwa DD yayi tareda dagowa batareda ya saki Bena ba hannunta na cikin nasa qanqame ya juya ya Kalli inda Naseer yake nuna masa idanuwansa suka dauka cikin na Bilal kaante dake tsaye bayansa Yana kallansa cikin firgici da tsananin so da kaunar Dan uwansa me tsananin gaske tareda Kuma tsananin mamaki da tsoron ya Akai yasan Nan din har yazo.
DD kuwa da farko dakatawa yayi dakyau Yana kallan mutumin dayake tsayen a gabansa idan Bilal ne kokuwa shine yake ganin Hakan,
Hannunsa dake riqe Dana Bena sakewa yayi ya rasa kuzarin kama komai bare iya riqewa Nan take,
Lumshe idanuwansa yayi ya sake budesu akan Bilal Wanda hawaye suka cika idanuwansa dakyau sbd yasan yanzu DD zai iya somewa idan ya tabbatarda shine sbd Kansa baya daukan shock masu girma be sababa da tashin hankali.
Motsawan Bilal ahankali tareda yowan taku daya Yana kokarin nufo DD tareda Bude baki zai kira sunan D din take DD ya fahimci tabbas Bilal ne a gabansa,
Daqyar ya iya waiwayowa ya Kalli Naseer dake gefensa Yana kokarin ganin DD din Bai shiga shock da yawa ba,
Gyada masa Kai Naseer yayi da alaman "yes Bilal dinne a gabansa Shima yana ganinsa.
Kasa riqe Kansa DD yayi Kansa yayi Wani irin sarawa qafafuwansa suka sare lokaci Daya Naseer da Bilal dasukasan zaayi Hakan dama suka taresa batareda ya Kai qasa ba
Bilal ne Kai tsaye da kansa ya cirasa da qarfi yayi kan kujera dashi Naseer na gyara masa pillows na doguwar 3 seater Turkish sofa set din aka Kwantar dashi.
Momyn Abdul kuwa na ganin Hakan tayi kitchen da sauri ta dauko ruwa me sanyi ta kawowa Bilal ta miqa masa karba yayi tareda ajiyewa gefe sbd sunyi sanyi ko babu sanyi ana saka masa su yanzu sai ya tashi da shiga Wani ciwon kan kokuma Wani abin Kuma Dan haka Naseer ne ya kalleta yace ruwan dumi zata kawo.
Bena datasan itama Daman zai iya shiga firgicin ya shiga wannan halin hawayen dake idanuwanta ne suka gangaro kan fuskarta ahankali taji qafafunta na qasa daukanta
da sauri sumayyah da Anne dasuke kallan iKon Allah sukai saurin riqota a tare suma sumayyah na rungumeta jikinta Anne Kuma na riqe da hannunta Daya tana Dan shafa bayanta da hannun Daya.
Daki sukai da ita suka zaunar bakin gado Anne ta Kalli sumayyahn tace taje ta kawowa Bena din ruwan dumi na tea itama Tasha da sauri Dan zata iya Amai da wanna firgicin sbd babu komai a cikinta.
Sumayyah kan Bena ta shafa cikeda kulawa kafin ta miqe ta fito daga bedroom din ta nufi dining ta fara kokarin hada mata tea sukuwa su Bilal na kan Dan Umme har lokacin.
Tana gama hadawa Bena din tea ta nufi dakin da sauri itama sbd Suma kokarin taimakawa tasu sukeyi.
Tana Kaiwa Anne ta karba tafara bawa Bena din wadda ta girgiza Kai tana cewa bazata iya saka komai acikintaba batajin buqatan Hakan.
Tilastata Anne tayi tareda sumayyahn suna rarrashin Tasha tea din sai alokacin sumayyah da Anne suka Kalli juna sumayyah ta zauna kan kyakyawan kujeran Dayake dakin ta Kalli Bena cikin kulawa sosai da tausasa murya tace
"Shine DD kaante din???
Anne ma shiru tayi tana jiran amsar da Bena din zata bayar sbd kansu na duhu da ganin wannan Dan madarar mara qarfin jini.
Numfashi ta fara saukewa kafin ta Dan dago ta Kalli Anne da itama ita take Kallo Dayake sun Saba ahaka suka taso basuda Wani abokai ko qawaye bayan Annensu da junansu.
Gyada Kai tayi a kasalance tareda bude baki ta furta "eh shine" ahankali tareda rufe idanuwanta hankalinta baya kanta Yana palo kan Wanda zuciyarta ke tsakanin bugawa a lokacin akansa.
Numfashi Anne da sumayyah suka sake lokaci Daya sai alokacin Anne taji kanta yayi Wani irin qato da sanyin jiki sbd kunyar kasancewarta a Palo lokacinda wannan abin ya faru,
Data sani Tim farko Hakan ze faru da yau bazata fita daga Dakinta ba zata zauna ta kame kanta acikinsa, Daman Bilal ne keta ganin Basu takura ba ko kame Kai sun saki jiki sun Saba dashi sosai yakeso sbd su zama ahali me kusanci da shaquwa da jina sosai.
Sumayyah kuwa shiru tayi sbd itama kunyar abin ne ya rufeta lokacin sbd da farkon lamarin duka shock ya hanasu Gane komai bare tinanin komai sai yanzu ne kunya da takaicin suna gurin ya shigo ke dabaibaiyesu.
Ita kanta Bena Jin yanda sukai tsit kowannensu Kansa a qasa yasata Jin kunyar komai Daya faru sbd harga Allah Bata tsammaci ganinsa ko a mafarkinta ba yanzu,hakama tasani kome zatayi a daidai wannan lokacin ko waye a gurin zai iya aikata Abinda ya aikata batareda yaji komaiba sbd Bai dauka baayin hakan ba a