Showing 111001 words to 114000 words out of 183527 words
sbd bikinsa akeyi bazai yiyuba ya tsallake ya tafiyarsa.
Hakanan ya fasa tafiyan Ya zauna Amma ba
Dan ya fasa ba matigar suka wuce sati uku
Basu dawoba zaije yaga lafiyan yarsa ya dawo.
Bikin da Akai na kece Reni da sa'a tareda
Barnar dukiyar gaske kafin aka gyara part din
Bilal tareda Maida part din sabo fil komai aka sauya daidai Amarya yar gata masu arziki.
Tafiyar su Bena da sati biyu cif aka kammala bikin Amarya ta tare cikin kaantes a part din
Bilal da yanzu yake nata.
Batada was qawaye sbd mummynta itace qawarta Kuma abokiyan shawararta da duk
Wani Abinda zatai tare sukeyin abinsu,qawarta
Daya Kuma bama bahaushiya bace 'yar Wani minister abokin daddynta Dan haka daga ita sai Mummynta da qawarta Rumah suka kawota sai Ummen DD din da Zeenah dakuma mum Khadija,Siyam Bata jeba sbd tanayin
Bena sosai Dan bayan Zeenah Bena batada
Kawa kaman Siyam din,itama Zeenah taje ne sbd zamanta dole Amma duk da haka da Bena na Nan ko tana dole bazata je ba gaskia zata zauna da ita ta rage mata radadin zuciya Koda
Bata nunawa ita Bena din.
Bayan Kai Amarya aka watse mummynta kafin su wuce ta tsaya sukai magana tsakaninsu
Mai Dan tsayi kafin ta fito suka bar kaantes kowa ya watse aka bar Safnah din ita Daya lokacin DD Yana wancan gidan nasa Yana hutawarsa sbd bayason ajiye kowace mace a wancan gidan shiyasa yace a gyara mata ta zauna cikin kaantes.
Bai dawo kaantes ba sai after 11 ya shigo da motarsa da kaf kaantes babu irinta yayi parking ya fito sanye cikin guntayen kayansa
Daya Saba sakawa Kai tsaye ya wuce sashen
Bilal din Yana shiga a Palo ya taddata
Tana ganinsa ta miqe tsaye tana ajiye wayarta data amfani da ita ta kallesa tare da masa sannu da zuwa batareda damuwa da time din
Daya shigo dinba dama kayan jikinsa dake bayyanarda daga hutawa ya fito.
Amsa gaisuwanta yayi tareda yimata barka da zuwa kafin ya Dora da yimata Saida safe ya nufi hanyar dayasan Nan ne bedroom dinsa anan ya shige.
Bata ji komaiba Dan tasan waye Dawood din game da zafin Kai da ajinsa Dan haka ta sauke Dan garamin numfashi tareda daukan wayarta ta nufi bedroom dinta itama ta shige tana wurgi da wayar kan gado ta wurgar da mayafinta Shima tana sake qaramin tsoki tace "Yana nufin haka zan kwana bayan duk
Abinda mummy ta dirka min Nasha?
Mitss"
A tsakiyan dakin ta tube kayanta ta jefar ta wuce toilet ta wanke duk makeup na fuskarta tayo wanka tanata fama tsoki a hankali sbd
Sam batada hakuri.
Tana fitowa wanka kayan bacci kawai ta saka ta fito dauka dakin ta nufi bedroom dinsa ga mamakinta dakin baya budewa sai an Bude maka daga ciki idan daga waje ne sai da password.
Wani qaramin tsokin ta Kuma ja mara sauti tareda Dan knocking kofar
A daidai wannan lokacin shikuma yana toilet
Yana wanka cikin ruwan dumi a natse Dan haka har tayita knocking ta gaji ta koma dakinta Baijiba.
Yana fitowa yayi Shirin baccinsa bayan yagama shafa tirarika da body oil kadan ya kwanta tareda lumshe idanuwansa da gabaki.
Daya babu Abinda suke bugata da son Gani kaman 'yarsa.
Washe gari daga gurinsu Umme aka kawo breakfast daga shi har ita babu Wanda ya tashi daga bacci sai 10,
Shine ya fara shiryawa ya fito cikin Giorgio
Armani classy suits navy blue da Alexander
McQueen shoes take gamshinsa ya cike palon da inda ya fito,
Bai tsaya breakfast ba ya fice sbd yau meeting dinsa nada mahimmanci sosai a office.
Bayan fitarta sai daga baya itama ta fito sanye da kayan baccin brush kawai tayi ta fito ta zauna kan dining zata fara cin Abinda Mai aikin da aka bar mata daga cikin masu aikin
Umme ta shigo a natse kanta a qasa ta gaida
Safnah din.
Bata amsaba ta fara cin abinci ahankali tana latsa wayarta Dan Kiran mummynta tace
"'Ina dayan matan D take zaune??"
Dan shiru Salma tayi kafin ahankali tace
"Tinda aka Akai auren a bangaren Umme take zaune da Amnah"
Shiru Safnah tayi sai a lokacin take tinawa da matar tasa nada shegiyar 'ya wadda aka samu
ba aure.
"Tafi naji" tafada tana cigaba da cin abincin a hankali.
Aiki Salma ta wuce zata fara duk da babu inda
yakeda alaman buqatan Wani gyara koina fes
Amma dole hakanan ta hau goge kaya tana
Shirin shara da mopping before wadata koina
da qamshi.
Ita kuwa Safnah tana gamawa wanka taje tayi
ta shirya ta nufi gurinsu Umme tayi zamanta
acan Dan maitan son ganin wadda take amsa
sunan kishiyarts a baki kawai.
*****Bena sosai ta danne ta Hana duk Wani
azaban da zuciyarta take ciki ta sake suka
ringa samun hutu da nishadi tareda kulawa
da dd babba sosai Dan kusan itace ke Basa
maganinsa da lokaci yayi maganinsa da lokaci yayi
Hakama shi Kansa dd babban duk Kiran da
DD ke masa Sam yaqi nuna masa suna gida
Daya ma da Bena Dan haka Bai taba kwatanta cewan a Basa 'yarsa ba bare Bena.
Amnah kullum sai tayi rigiman son magana da daddynta shi ya saka Bena dagewa ta danne
Abinda yake cin ranta ta saki jiki tana bawa
'yarta nishadi suna Jin Dadin qasar yanda ya kamata.
Ta bangare Daya Kuma aikinta na office Bai dakata ba tana exchanging emails sosai da
Fahad gameda ayyukan office Dan haka take sake samun kwanciyar hankali da nutsuwa.
Bata saka ranar dawowa a kusa ba San Dan karatun Amnah da hutun ta yake kokarin qarewa Dan haka sbd Amnah kawai zata koma idan lokaci yayi.
****Acan Nigeria kuwa Safnah kullum a bangarensu Umme take wuni duk da ta samu sanin Bena Bata qasar da 'yarta,
DD kuwa kusan kullum baida time na zama gida Yana dawowa yaci abinci ya shige shikenan babu Wani Abu na kusanci da juna koma fira haka ta kauna da kulawa data taba shiga tsakaninsu kullum baya Wani zama sbd ko baya office yafi zama gidansa dake highbridge, yafi samun nutsuwa da kwanciyar hankali acan
Ya kasa sabawa da zama kullum kullum da mutum a guri Daya shiyasa duk inda yake tin asali baya zama cikin familynsa yafison yaje inda zai zauna shi Daya yayi rayuwan dayakeso gashi matiqan Yana cikin gidansa ba maabocin saka kaya masu nauyi ko tsayi bane
Dan Hakan yake zaban zama gidansa shi Daya yayi rayuwansa ba takura ba damuwa.
Safnah hakurinta Yana qarewa gameda zaman
Datakeyi da mutumin da takejin zuciyarta idan
Bata samesa ba komai zai iya faruwa, Zafi da bagin ciki sosai takeyi da irin zaman dasukeyi
Babu ranar da Bata Kai kanta dakinsa Amma
Bai taba barinta ko shigaba Bare ta samu
Daman Jan raayinsa ya kwana da ita Dan a yanzu tafi buqatan suyi kwanciyar aure akan komai sbd vanda yake fitowa daga shi sai dogayen wandina ba Riga kokuma guntayen wandina ba Riga jikinsa ya sakata qara mutuwa akansa sbd ita ko a turawanta datai ravuwa cikinsu DD kaante daban yake,
Komai nasa me aji da Jan hankali ne tareda daukan Ido.
Ahaka suka shafe sati biyar babu Wani gaba bare baya Dan haka itama ta rage zama gida kusan kullum saita fita sunfita da Mummynta sbd lamarin ya fara qundurarsu gashi hakanan
Safnah takejin Bata gaunar matarsa ta dawo
Bata gama samun Kansa ko hankalinsa akanta ba Dan haka daga ita har mummynta hankalinsu ya tashi suka kasa zama suka kasa tsayi. ******Watansu Bena 2 cif suka fara Shirin dawowa lokacin suna barin Australia Umrah suka wuce suka qara sati biyu kafin suka diro
Nigeria,
Jirginsu da Asuba ya sauka Dan haka Fahad ne ma yaje da Kansa da lafiyayyan motarsa ya daukosu,
Kallo Daya yayiwa Bena ya dauke idanuwansa
Yana kore shedan daga zuciyarsa sbd yanda kyanta ya daki kirjinsa,
Tafiyan wata biyu kokuma yace uku Amma komai nata ya qaru,
Kyau, lafiyan fata,hutu,nutsuwa,aji da burgewa duk komai ta garo hakama harda cikowa tayi kaman wadda babu Abinda taje tayo sai hutawa. Dd babba ma ya gara samun qarfi da lafiya sosai harma da kwanciyar hankali sbd kulawa da Bena ke Basa da yanda ya bar gida da hayaniyarsu yaje ya huta Abinsa.
Abbakar kuwa gibarsa yayo abarsa lafiya kalau ta hutu da cima me kyau duk da Baya Wani son abincinsu acan Amma cinsa yakeyi ya koshi Abinsa ya huta ya fita yawon Shan iska yaci Dadi San ransa
Amnah ma sosai tayi jikinta da haske data garo Daman ita ba skin din mamanta ta daukoba na baban Dan haka take fara tas kaman DD.
Koda suka shigo kaantes an shiga sallan
Asuba Dan haka babu Wanda yasan ma sun iso, sai a lokacin ta Ciro wayarta jaka ta kunna ta kira Nafisat, Nafisat ce ta kwasar musu kayansu zuwa ciki shikuma dd babba Abbakar ne ya shiga nasa kayan bangarensa kafin suka wuce masallaci sallah sbd alokacin ne aka tayar.
Suna shiga Kai tsaye bedroom din Zeenan suka shige Nafisat Kuma cikin duhun Asuban ta hau gyara dakin Bena din.
Sun shiga Zeenah Bata ma tashi sallan Asuba ba motsinsu da shigowansu dakin ya tayar da ita ta tashi zaune ahankali ta miga hannu tana kunna wutan dakin taga Bena tsaye tana ajiye handbag nata Amnah kuwa gadon ta fada sbd bacci ne sosai a idonta.
Da sauri Zeenah ta sauko gadon bacci na
Sakin idanuwanta gabaki Daya ta nufo Bena suka rungume juna tana cewa "Oh ya Allah finally Bena kin dawo."
Murmushi Bena ta sake ahankali tareda rungumeta itama tana cewa
"Kin dauka bazan dawo bane?"
Mintsininta Zeenah tayi tana janyewa daga jikinta tace
"Kinsa me kikai kuwa?
Meyasa Zaki Kashe waya ki Hana kowa Jinki for more than 2months,
Kin kusa sakawa kowa heart attack da rashin
Jinku.
Wani murmushin me sauti ta Kuma sakewa tana cewa
"Ba gashi na dawo ba"
1
Kayanta tahau cirewa ta fada toilet tayo alwala batai wanka ba ta fito ta saka Riga da wandon bacci tayi sallah ta fada gadon Zeenah din ta shige bargo take baccin dake cinta da gajiya ya dauketa.
##MAMUH#
#DBENA
#TOO HOT
#MARRIAGE
#ROMANCE
#SAFNAH
#KAANTES
* Arewabooks@Mamuhgee_*
64
Zeenah ma sallan tayi Amma farin ciki ya hanata komawa bacci Dan haka karatun
Qur'an tayi a iPad kafin tana gamawa ta miqe ta hau Aiki a laptop Kuma.
Zata fita office 9 yau Dan haka time nayi ta shirya dole tabarsu suyi baccin hutu tukuna
8:30 nayi na fice.
Amnah ce ta fara tashi ta sauko gadon ta fito dakin ta nufi kitchen gurin Nafisat wadda sai alokacin ta samu ganin Amnah ta rungumeta cikin murnar dawowansu sbd lokacinda suka dawo da Asuba Amnah din na jikin mummynta sod bacci.
Itama Amnah sosai tayi kewan Nafisat din Dan haka ta Haye jikinta suka dawo zuwa bedroom din mummynta.
Dakin Nafisat tai masa Wani irin gyaran tsafta da kyau koina sai qamshi da sanyi ke tashi tareda ni'iman tsafna.
Toilet suka wuce Kai tsaye Nafisat ta taimaka mata tayi brush kafin Akai fitsari da alwala suka fito ta saka mata abayan sallah tayi sallah duk Nafisat na tsaye tana jiranta.
Tana gama sallan nata da zaa ce Allah ya
Bada Lada
Nafisat ta dauke kayan sallan ta sake gyara toilet da dakin kafin suka wuce kitchen Nafisat na cewa Bara na hado Miki breakfast naki yanzun Nan.
Cikin tsalle Amnah ta fara cewa
"a ba breakfast nakeso yanzu ba Ina iPad
Dina ki dauko ki sakamun charge inason Kiran Daddyna nayi missing nashi sosai sosai sosai Gyaran muryansa taji daga bayanta ahankali ya furta
"I miss my angel too sosai sosai.
Da Wani irin gudu ta nufosa tin Bai garasaba ta fada Kansa ya dauketa yayi sama da ita Vana
Jin zuciyarsa na samun sanyin da tinda suka tafi ya rasa shi.
Dariya sosai Amnah keyi tana farin cikin ganinsa shi Kansa murmushi yake mata
Wanda ya saka Nafisat silalewa ta kama hanyar kitchen Dan hado Abinda tasan dashi
Amnah ke breakfast wato chocolate custard fa soyayyan farin kwai da tomatoes kawai. Umme ma dariya da ihun Amnah ya sakata fitowa Daman dad kaante ya fada mata sun dawo sbd kowa a masallaci sallan Asuba
Kawai akaga dd babba da Abbakar, Shi Kansa Daddyn Amnah din a masallaci ya gansu ya tabbatarda dawowan 'yarsa.
Amnah na ganin Umme ta sake shiga farin ciki itama tayi kanta ta rungume tana cewa tayi missing nata.
Daga jikin Umme ficewa tayi da gudu zuwa palon dad kaante Yana zaune Yana amsa waya yajita Kansa ta fado dole yayi sallama da
Wanda yake wayar Yana cewa
"Zaki karyawa dad din daddynki wuya ai da
"
wannan kibar da kika qaro acan.
Dariya tayi masa tana cewa "Wuyanta baze karye ba ai yanada qarfi sosai kaman na Daddyna"
Murmushi yayi Yana zagayo da ita gabansa yace
" Wannan wuyan na Daddynki ai yafi na kowa garfi."
Shigowan daddynta palon ya sakata barin jikin dad kaante ta koma gurinsa ya dauketa Yana garasowa ciki ya gaida dad din kafin suka juya suka fice.
Palon Umme suka koma lokacin Nafisat ta gama hadowa Amnah din komai Suma sauran masu gidan angama nasu breakfast din an
Jere a dining. A dining din ya zauna shi da Amnah suna magana Yana amsa mata a hankali Nafisat na kokarin qarasa shirya mata breakfast din a gun
Daidai lokacin 9:40 ta buga aka Bude kofan bedroom din Zeenah Bena ta fito ahankali tana
Dan shafa wuyanta dataji yasamu sakewan datakeso sbd samun isashen bacci.
Kayan baccin jikinta masu tsantsi me da yanayin sanyi ya Dan sakasu lafewa jikinta tana fitowa Kai tsaye dining ta nufo tana Dan
Kiran sunan Nafisat sbd ta kawo mata tea me zafi sosai yau takesan Sha.
Tinda ta tinkaro dining din ya dago fararen idanuwansa ya zuba mata bata ankara da
Hakan ba Saida ta qaraso daf ta tsaya cak
Wani irin sanyi da bugawan zuciya na samunta lokaci Daya.
Dagashi har ita kowannensu yaga sauyi sosai a tattare da dayansu,
Kowannensu ya qara sauyawa da samun hutu da kyan yanayi musamman ita da komai na
Qarin data samu a bayyane yake.
Ahankali ta dauke kallanta da gunsa zuciyarta na Dan gara tsananta bugawa.
Juyawa take kokarin Yi Takoma Amnah tai caraf tace
"Daddy bakaiwa mummy oyoyo ba gatanan ta fito."
Bena na Jin haka ta juyo da sauri ta kallesa
Shima ita yayiwa Wani Kallo da mayun idanuwansa
Tana ganin Hakan ta daga qafa da sauri zata gudu saidai ko taku daya Bata qarasa ba ya miga hannu daga zaunen Dayake ya riqo hannunta Daya ya dawo da ita baya ta fado kansu shida Amnah Dake jikinsa.
Nafisat na ganin Hakan tayi saurin barin gurin kanta gasa
Hade fuska Bena tayi tana kokarin cire jikinta
Dana nasu Amnah tace
"Mummy ki tsaya mana oyoyo kawai zai Miki kin manta munce muni missing nasa sosai fa."
Rintse idanuwa tayi ta budesu akan Amnah cikin takaici zatai magana Amnah ta sauka daga jikinsa tana cewa
Bari na dauko iPad dina nayi muku hot kanawa mummy oyoyo.
Amnah na barin gurin ta kallesa a hankali tareda Bude baki tace
"Ina bugatan tashi ka sakeni"
Cikin idanuwanta ya zuba nasa ahankali take ta rufe nata tana kokarin Hana bugawan kirjinta Dayake fara Hawa yana sauka.
Magana ta sake Bude baki zatayi taji hannuwansa sun qara zagayeta ahankali tareda zaunar da ita da kyau kan qafafunsa suna fuskan juna.
Yanayin zaman ya sakata dagowa ta kallesa zatal magana tana Bude baki ya kamo kanta ahankali ya hade da nasa tareda zira harshensa cikin bakinta.
Batai tsammanin Hakan ba ko a mafarkinta
Dan haka ta qangamesa tana rintse idanuwanta kafin yanda yake kissing cikin bakinta ya sakata lumshe idanuwa tana Jin zuciyarta na Neman sanyi da narkewa.
Motsin dawowan Amnah ne ya sakasa Sakin bakinta ahankali tareda Ciro nasa ya jingina bayansa da kujeran dining din Yana kallanta da kasalallun idanuwansa kaman babu Abinda yayi.
Itama kasa dagowa tayi ta kallesa bare
Amnah hakama ta kasa tashi daga jikin nasa
Saida Amnah tace su shirya tai musu hoton tukuna ya Dan dago bayansa ahankali tareda daukan Amnah din ya saka tsakiyansu Akai hoton tukuna Bena ta iya migewa daga jikinsa ahankali jikinta a mace. Umme ce ta garaso itama fuskarta cikeda
farin ganin Bena din Mai tsanani tana zuwa
Bena ta rungumeta tana cewa
"Ummenah nayi kewanki sosai"
Cikin farin ciki Umme tace
"Mu da kika cinnawa hauka Bena,
Kika Hana kowa Jinki,
Amma dai koba komai kinyi kishi me tsafta
Allah ya qara Miki hakuri...
Kasa amsawa tayi tareda Satan kallansa
Shima itan ya kalla Jin kishi ne ya korata ta
Hana kowa jinta.
Kunya da nauyin maganar Umme ya sata zaunawa a Dan fuske tana basar da zancen suka fara breakfast harda ummen duk da ta
Dan ci breakfast tareda dad kaante a nasa palan.
A hankali take cin abincin batareda ta dago ba sbd idanuwansa na hanata walwala a gun.
Sama sama Shima yaci abincin Umme ta kallesa tace
"Matarka na can na jiranka kuyi breakfast kazo kayi anan.
Tsit gurin yayi har da ita ummen sbd sai datai maganar ta Tina da Bena dake gurin,.
Shima Bena din ya Dan kalla, Bena kuwa ruwan tea din dake bakinta ta hadiye ahankali sbd Neman gagara wucewa da sukai Bata dago ga ta dauki tissue fuskarta babu Wani sauyi ta goge bakinta ta dago ta
Kalli Umme cikin sakewan fuska tace
"Umme inaga yau zan koma office akwai pending ayyika sosai suna jirana,zan biya na dubo Anne kafin na tafi.
Murmushi Umme ta sake tana waskewa itama ganin Bena din Bata nuna damuwa ba tace
"Ok ba damuwa ki gaida Annen Taki tareda
Ababa Shima duk Muna gaidasu."
Bata kallesa ba ta mige daga dining din ta wuce tana Jin idanuwansa akanta har ta shige bedroom.
Tana shigewa ta tube kayan baccin jikinta ta daura towel din Amnah da yayi mata qarami sosai ko dauruwa bayayi saidai ta riqe
Nata duk Nafisat ta kwashe da safen ta wanke sbd bazata iya daurawa sai an kwanke tin Bata
Nan sun kwana biya a ajiye
Na Amnah kuwa sabo ne ta fasa yanzun ta daura itama tana bugatan shopping din sababbi da wasu daga cikin toiletries nata.
Kofan dakinta aka Bude Kai tsaye aka shigo tareda rufewa Bata juyoba tana duba undies nata strapless bra zata dauko sbd tinanin
Amnah ce sai dataii shiru ta dakata sai a okacin taji qamshinsa ya shiga hancinta sai kawai ta qi juyowa tareda fasa dauko bra din ta nufi hanyar toilet zata shige yace
"'Na dakatar na zuwa Aiki da fitanki gaba Daya." Cak ta tsaya tareda juyowa Bata shirya ba sbd rashin fahimtar zancen da kyau.
Kallanta yakeyi fuskansa ba sakewa yace
"Yes you hard me right."
Dawowa tayi zatai magana Bai tsaya sauraranta ba ya juya ya fice daga dakin fuskansa a hade sbd Bai dauka Yana zaune zata fadawa Umme fitanta da Abinda ya yankewa kanta ba batareda ko kallansa ba
Yana matsayin Wanda shine yakeda ikon da
Damar badawa din.
Wani irin bagin ciki ne me nauyi ya danne zuciyarta takasa ko motsawa daga inda take tsaye.
Ta jima a gurin tsaye kafin ta iya shiga toilet jikin na zafi da zazzabin bacin Rai Daya saukan mata a take.
Wankan ma ba acikin Dadin Rai tayosa ba ta fito ta shirya cikin Riga da skirt da coffee brown lace Mai tsananin tsadan tsiya ta Kira
Zeenah ta