Showing 78001 words to 81000 words out of 183527 words
Yara Kuma kowa ya shedesa da Hakan,
Amma ayau ranar farko babyn farko dayaji tashiga ransa,
Duk buqatan karban babyn Dayake Yi a baki sai Daya rungumi babyn yakejin Abinda ma yafi buqatan ta a kusa,
A rayuwarsa kwata kwata yake buqatanta sbd bazata taba maraicin Mahaifinta ba matiqar Yana Raye shine Mahaifin dazai nuna mata soyayyar Uba,uncle harma da uwa idan ya tafi da ita.
Masu buqatan pages da Akai Nisa sosai follow me at mamuhgee Arewabooks kokuma suyi joining VIP
09033181070
#MAMUH#
#HOT
#MARRIAGE
#ROMANCE
#DBENA KAANTES
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
44
Sai yamma aka Maida baby Amnah gurin mamanta tareda da kayan da saidai aka Kai wasu dakin Ababa dakinsu ba guri,
Ababa kuwa shanun da aka yanka haka ya kama fiyeda Rabi ya siyar sauran Kuma yayi sadakar Rabi sbd Amnah tayi albarka Wanda ya rage kuwa aka Soya suka ringa cin abinsu hankali kwance,
Su benazir din Suma wanna Karan anbasu me Dan yawan dasuka ajiye Dan bazasu iya cin ba,
A cikin damuwa suke da sanyin jiki Dana zuciya na rabuwar da zasuji da juna,
Daga hande sai Ababan ne suke cikin tsananin farin ciki da murnar auren Dan haka yanzu baa musu Horan yunwa abinci yake Basu sosai tareda yiwa Benazir alqawarin idan ta Kwantar da hankalinta a auren take ta zama hamshaqiyar da zata ringa Basa dukiya kaman batasan metake ba shikuma yai mata alqawarin Annenta zatai rayuwar 'yanci da kwanciyar hankali.
Idan ta je ta Saba umarninsa kuwa Annenta ce zata dauki hukuncin babu tausayi ba sauki tasan halinsa.
Abincin dasuke samu ana Basu tareda saka su cin dole harma da kayan gyaran jikin da ake gyarata ya saka Benazir Dan cikowa daga bushen Datake.
Hande kuwa ita dai matse take da ayi bikin su huta Dan haka ta ringa gayyata tana shelan gidan da 'yarsu zatayi auren.
Kayan lefen aure Mum Khadija ita Daya ta kawo sai Zeenah da Siyam sbd Basa buqatan daukaka bikin komai a kaman sirrance zaayi sa
Sai daga baya idan Sbb ta dawo zata tare ayi bikin da kowa zaiji ayi gayyatar da aka San bazaa ji kunya ba.
Lefen da aka a cikin akwatinan lv set ne Dan
situran alfarma da kaf gidan har Ababa baisan kudinsu ba da darajansu aka kawo mata bare ita da batama San wata sitarar ta alfarmar ba,
Breeziers da panties da komai na cikin kayan foreign ne masu tsada designers Dan gashi kusan komai daidai na matashiyan mace ne aka Sako hande naji tana Gani babu abin dauka aciki sai laces data kwasa da atampa kusan guda goma.
Anne kuwa komai batada shaawan mallaka a kayan bare Kuma ma me kayan benazir da kasa ma kallan kayan tayi bayan da dare yayi suka shige.
****Ta bangaren Kaantes babu Wani biki bayan daurin aure Dan haka babi Wani hidiman dasuke Yi sai jiran lokaci.
Umme wata damuwan ta sake shiga a lokacinda Dan uwanta yace a boyewa Sbb maganar auren Dawood da wata bayan nata tinda bata qasar Dan haka Umme taketa Jin damuwa kada Sbb din taji ta tada rigima da tashin hankalin da zai saka hajiyarsu taji ba Dadi kokuma laifin Dawood akan zai auri wata lokaci Daya da Sbb dinsu.
Ita kuwa sbb din acan farin ciki takeyi Mai tsananin gaske Jin zaa daura aurenta da DD kaante kafin daga Baya ayi bikin tarewarta idan ta gama sauran karatun nata ta dawo.
Ango DD kuwa babu Wani Abu na farin ciki ko baqin ciki Dayake ji gameda aurensa,
Abinda ya sani shine aure ne zaa daura masa da matan da babu wadda yake so aciki,
Daya zabin mahaifiyarsa,
Daya zabin kakansa Kuma baby mamah dinsa Dan haka duk Wanda Bata sakawa Kanta tinanin dayafi karfinta ba itace zata zauna kaantes lfy.
Ana sauran kwana daya daurin auren Ababa yaje Kaantes da maganar kayan daki Kai tsaye suka sanar dashi babu Abinda suke buqata nasa bayan benazir da babynta.
Daman yasan zaayi Hakan Dan haka ya dawo yaci gaba da shirye shiryensa cikin farin cikin samun cikar burinsa.
Benazir kuwa kullum dare sai sunyi Kuka sosai itada Annenta na rabuwar da zasuyi da juna Bada San ransu ba,
Duk yanda Annen takeson daurewa da dannewa kasawa tayi Dan haka duk dare take Shan kukanta a boye
Itama benazir duk dare tareda Annen take kukan daga kwance batareda Annen tasan Benazir tasan tana Kukanba kullum.
Ta bangare Daya a Dan qanqanin lokacin Reno tamkar da uwar data haihu yariga ya shigeta Dan idan ba nono da Bata Hawa Amnah ba tini itama ta sakawa ranta itace ta Haifa Amnah kaman yanda Ababa ya fada.
Renon Amnah yasaka yanzu aikin gidan tini aka dauke mata sai ga me Aiki hande ta saka ankawo mata wata bazawa daga kauye.
*****
Ranar Friday 6 ga watan Sept aka daura auren DAWOOD D KAANTE Dana BENAZIR ABABA kafin daga Baya aka sake daura na DAWOOD D KAANTE din da SAFNAH BASHEER BULAMA.
Daga lokacinda aka gama daura auren Benazir da Dawood Ababa a cikin bainar jamaa ya zube qasa yayiwa ubangiji sujjada ya miqe ya sake Yi Yana miqa godiyarsa ga Allah.
Sunan Safnah da aka ambata gurin daura auren ba biyu ya saka Ababa dakatawa daga farin cikin Dayake yi yana Tino tasa Safnar data gudu Yana jin baqin ciki tareda fatan wannan Safnar ta gudu daga auren Nan kaman Yanda Safnar gidansa ba a gudu.
Taron daurin dauren ya hada manyan mutane masu yawa daga garuruwa daban daban.
Fadan Taron da aka samu a gurin bazai yiyuba
Securities kuwa koina na anguwar da kewanta hakama jiniyas na motocin tsaro koina.
Akwai mutanen DD dasuka halarci daurin dauren da damansu Dan haka dole ya tsaya ya amsa adduoin mutane da dama kafin ya bar gurin daurin auren Kai tsaye gidansa ya wuce sbd Yana buqatan hutu daga mutane.
Naseer ne Daya kasa yarda da benazir din Dayake bibiya ce tin makaranta aka daurawa DD aure da ita sbd yasan dai itace Benazir Ababan.
Suna isowa a natse ya fito mota Kai tsaye ya wuce ciki Yana cewa Naseer kada ya bari kowama yasan Yana gida hutawa zaiyi Yana fama da headache.
Shi Kansa Naseer Yana fama da headache din Dan haka kashe wayar DD din yayi ya ajiye masa ita a palonsa ya fito yabar gidan ya tafi gida Shima ya samu Kansa ya warware Shima.
Yana shiga bedroom dinsa kayan jikinsa na sky blue tsadaddiyar shadda ya ciresu gabaki Daya tareda shiga closet room dinsa ya janyo drawer da towels ke jere aciki ya Ciro Daya ya daura a qugunsa da babu kaya a jiki ya nufi toilet.
Komai Dayake toilet dinsa na musamman ne domin buqatansa sbd baya iya sharing toilet da kowa,baima taba ba duk tsanani baya amfani da toilet koina sai gidansa sai kuwa na part din Bilal Dayayi amfani dashi a kwanakin dayayi Kaantes.
Ahankali ya sakarwa Kansa ruwan dumi Yana lumshe idanuwansa ahankali sbd relief dayaji yafara samu daga gajiyansa.
Bai dauki time sosai ba yagama ya fito jikinsa da toilet din gabaki Daya ya cika da sanyin qamshin English pear shower gel na Jo Malone.
Daurin towel din qugunsa kaman yanda ya Saba daurawa a sassake kaman zai Fadi yabarsa ya nufi mirror Bai tsaya batawa Kansa time kaman Wani mace ba body oil na Aesop kawai ya shafawa lafiyayyan fatansa dake daukan Ido kaman baby da baya shiga Rana kwata kwata.
Spray kawai ya fesa Wanda ya sake kashe dakin da sanyin qamshinsa ya bar gaban mirror yaje ya saka black Calvin Klein sleeveless shirt da black quarter trouser da slippers masu taushi ya fito Palo ya wuce kitchen ya Bude fridge ya dauko ruwa mara sanyi ya Sha kadan ya koma daki ya kwantawarsa Daman Bai Wani Yi baccin safen ba sbd daurin auren.
Yana kwantawa sbd rashin damuwa da gajiya take bacci ya daukesa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.
*******A gidan Ababa kuwa ranar ce ranar farko da Ababan ya sakawa tasa haihuwar albarka Dan kuwa benazir din ya dinga zundumawa albarka ba kunyar Allah bare ta su Benazir din da Annenta.
Kaman yanda akewa kowace haka Anne ta zauna da benazir da idanuwanta suka bushe sukai jajir Bata iya cewa komai sbd ayau nauyin zuciyarta yafi na kullum,
Bata taba tinanin ta wannan hanyar zata rabu da Annenba,
Kuka takeson Yi na barin mahaifiyarta da itama zatayi su barta a hali da rayuwar ukubar da basusan ya zamu sameta a gaba ba.
Kwata kwata takasa kuka tin lokacinda aka tabbatarda an daura auren,
Jajir kawai idanuwanta sukai suka bushe jikinta ne kawai yake rawa a boye Shima sbd halinda zuciyarta ke ciki.
Ita kanta Annen daurewa kawai takeyi tana Hana rauninta bayyana gashi akwai mutane a gidan,
Kaman marayu daga benazir din har Anne babu me walwala ko kuzari suna rakube a daki cikin mawuyacin hali gashi Basu Saba shiga mutane sosai ba Daman.
Su kansu yan bikin duka mutanen hande ne da wasu daga danginta dasuka zo daga kauye Dan haka baa damu da nemansu ba har sai yamma da Ababa ya dawo gidan lokacin kusan duk an watse ba kowa sai su sai baqin hande na kauye mutum uku da suka taho Kuma suna can sunata faman Aiki kaman wasu injin baji ba Gani.
Ana gama sallar magrib Ababa yayi kiransu take gabansu a tare ya Fadi lokaci Daya Anne tayi qasa da kanta tana hade hannuwanta dake rawa ahankali ta damqe tana kasa dagowa ta Kalli benazir data juyo ta zubawa Annen idanuwanta da take suka ciko da wasu ruwan hawaye masu tsananin zafi.
Anne najin daukan hawayen benazir a hannunta ta miqe tsaye tareda juya baya bazata iya kallan benazir din ba hannuwanta na tsananta rawa tana Hana kanta kukan Dayake yanka zuciyarta fitowa ta sunkuyar da kanta.
Benazir data ga Hakan kukanta ya kufce ta kasa motsawa itama sbd Bata taba Jin radadi irin Wanda take jiba a lokacin ba.
Hande dataji shiru shigowa dakin tayi Kai tsaye Bata Jira komaiba ta kamo hannun benazir ta fara Janta tana kokarin ficewa da ita, sai alokacin ne benazir ta iya Bude baki ta kira sunan Annen a hankali.
Kasa juyowa Annen tayi sbd hawayenta dake saukowa da gudu kan fuskarta zuwa kirjinta,
Bazata iya Kallon a rabata da benazir a tafi da ita ba duk da tanason Hakan tamafi Ababan buqatan benazir dinta ta tafi tasamu 'yanci da rayuwa Mai kyau.
Benazir na ficewa daga dakin ta fasa Wani irin Kuka Mai tsananin ciwo da qarfin gaske tana Jin wannan rabuwar tafi mata ciwo akan ta sauran yan uwanta sbd su tasan mutuwa sukai suka bar duniyar
Annenta kuwa batada tabbacin rayuwar da zatayi a gidan cikin lafiya sbd tafiyarta kawai zata iya tayarda ciwon Annen Kuma babu me iya ko kallanta bare ya taimaka mata.
A palon Ababa suna shiga hande ta dire Benazir din tana cewa
"Kuka takeyi a daki itada uwarta kaman wadda muka siyar gidan wahala."
Tsoki Ababa yayi sbd baida lokacin duk Wani sabon renin hankali ko Bata masa lokaci Dan haka ya Kalli benazir din fuska a daure babu rahama ko kadan yace
"Babu Abinda zan fada Miki
Kinsan daidai sbd ganganci Daya zakiya akan asalin waye mahaifiyar Amnah ki nema mahaifiyarki ki rasa bat zan batar da ita wlh,
Kiyayewanki shine zaman uwarki lfy,
Gangancinki kuwa a jikinta zataji,
Duk Abinda Zaki zama a Nan gaba kada ki manta uwarki na hannuna itace alqalamin juya rayuwarki a duk inda kike,Dan haka bazance komai ba sai Allah ya Bada zaman lafiya da sa'a,
Kuma wlh karki yarda naji ko naga kinje kin zama baiwa ko wata wawuya a gidan,
Kaantes Zaki zama ki koma hamshaqiyan matansu ta yanda zan Riga fada da alfahari 'yata ce a gidan ba baiwa na siyar musu ba mata na Basu."
Masu buqatan pages da Akai Nisa sosai follow me at mamuhgee Arewabooks ko suyi joining VIP
09033181070
#MAMUH#
#MARRIAGE
#ROMANCE
#CRAZYINLOVE
#DBENA KAANTES
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
45
Benazir kasa ko motsawa tayi da maganganunsa hakama Anne data biyo bayansu ta tsaya daga wajen palon tanajin duka Abinda yake fadawa Benazir tayi qasa da kanta tanajin inama itama ta mutu ya rasa Abinda zai juya rayuwar Benazir a gidan aurenta ta samu tayi rayuwar kwanciyar hankali kaman kowa.
Wani Abu me nauyi ne ya tsaya kirjin Annen tana Jin jikinta na sake sanyi tinda masifar Bata qarewa benazir ba kenan,.Tayaya zata taimakawa 'yarta qwalli Daya data rage mata a duniya?
Tayaya zata Hana Ababa juya rayuwar Benazir a gidan aurenta.
Wani numfashi ta sauke ahankali hannuwanta na Dan rawa daga tinanikan da zuciyarta ke Bata.
Benazir kuwa numfashi itama ta saki boyayye Wanda yasakata qarasa sarewa daga duniyan gabaki Daya hakama tinaninta ya koma empty Bata ma iya Gane komai yanzu bayan maganar Ababa dake ta amsa sauti cikin kanta.
Kaman makauniya haka hande ta sake kamata ta tayar suka fito
A lokacin ne suka tadda Anne a kofa wadda ta share hawayenta daga idanuwanta da babu sauran hawaye Kuma.
Ga mamakin hande Anne da kanta ta amsa Benazir ta nufi daki da ita ta shiryo benazir din da itama Bata iya komai sai yanda Akai da ita.
Duk yanda hannuwan Anne ke rawa sosai gurin shiryata Benazir na ji Amma Bata iya ko motsawa bare kallan Annen har suka gama ta itama ta sake shiryawa ta dauki Amnah da ta shirya itama ta dorawa benazir din a jiki ta rungumeta ahankali ta suka miqe Anne da riqe da hannun benazir din Daya suka fito.
Hande kallan mamaki takewa Anne data nuna qarfin hali da juriyar shiryo Benazir ta fito da ita da kanta.
Ababa baiyi Wani mamaki ba Dan yasan dole suyi Abinda yace din,
Baiyi mamaki ba sai lokacinda Anne da kanta ta Bude baki tace zata raka Benazir har gidan aurenta idan anbata dama.
Shiru Hande tayi tana kallan Annen Shima Ababan kallanta yayi Yana Maida kallansa gun hande yace
"Ciwonta Daman ya tashi ne shine baku fadamun ba?"
Lumshe idanuwa Benazir tayi batareda ta motsa ba
Itama Anne Dan rufe idanuwan tayi ta Bude ahankali tareda girgiza Kai cikin sanyi tace
"Bai tashiba lafiyata kalau,kawai so nake na Rakata din sbd bansan yaushe zamu sake ganin juna ba."
Kallanta hande tayi zatayi magana cikin fada Ababa ya katseta da cewa barta ta tafi din tinda Daman ba kowa ne ze raka Benazir din ba ke kince bazaki ba gwara ita ta rakatan.
Da wannan hande tayita fadan waye ya taba ganin uwa ta Raka 'yarta gidan miji sai akan Annen wadda ita ta tabbatarda haukarta ce ta tashi shiyasa,Daman idan bakada hankali komaima zaka iya Yi.
Anne kuwa hannun Benazir kawai ta kama Bata dago Kai ga fadan hande ba suka fito.
A BMW 7-series aka Aiko Abbakar daukan benazir tareda mum Khadija wadda da kanta ta amso benazir Suka shigo mota harda Anne wadda dukkanin jikinta rawa yakeyi da Abinda yake zuciyarta datasan zai iya zama sanadin rayuwarta Amma tayi na'am da hakan Koda ta rasa ranta tasan ta taimaki 'yarta takuma tseratar da ita inshallah ta yanda ko bayan barinta duniyar Benazir zata rayu cikin aminci da kwanciyar hankali.
Har suka Isa babu me ko motsi bare magana a motar.
Tin a gate din farko jikin Anne ta tsananta rawa numfashinta na fita da sauri maqoshinta na bushewa tana Jin kanta na juyawa kaman ciwonta zai tashi Dan kusan duk ta fita Hakan takeji matiqar ba komawa gidan Ababa tayiba.
Daga benazir din har Anne babu Wanda hankalinsa da tinaninsa yake kan aljannar duniyar dasuka shigo sbd kusan babu Wanda yake hayyacinsa cikinsu.
Zeenah ce da wasu baqin suka fito suka tarbi benazir Amnah na hannun Mum Khadija suka karbeta cikin farin ciki sukai ciki suna mantawa da Anne dake mota, benazir Kuma Daman babu Abinda take Ganewa sbd kanta ma Dayake Neman juyewa duk inda Akai da ita can take zuwa.
Anne data kasa fitowa hannuwanta da qafafunta na tsananta rawa Wani busashen yawu ta hadiye daqyar kafin ta Bude baki muryarta na rawa tana kallan Abbakar daya Bude mata motar Yana jiran fitowar ta tace
"Inason zanyi magana da dd babba Dan Allah ka mun iso"
Kallanta Abbakar ya juyo yayi cikin mamaki da tinanin lafiya Kuma bayan anyi musu Abinda suke so an auri 'yarsu.
Kaman zai Bata hakuri akan Hakan sai Kuma dai ya Ciro wayarsa ya kira wayar dd babban ya sanar masa Abinda yake faruwan.
Shi Kansa dd babba shiru yayi Yana nazari sbd baya buqatan ganin kowa yanzu Yana Dan fama da jikinsa da isashiyar lafiya na duk tashe tashen hankalin da akaita shiga a Dan lokacin dakuma auren da aka daura yau Dan haka yace baya buqatan ganin kowa.
Yanda jikin Anne ke rawa tana cikin matsanancin tsoro da ficewan hayyaci ya saka Abbakar cewa ta sanar dashi sakon zai isar mata.
Rawa jikinta ta tsananta ta kallesa tana tattara nutsuwarta ahankali tace zancen yanada mahimmanci sosai dd babban kawai zan iya fadawa gameda gaskiyar haihuwar Benazir ne.
Da sauri Abbakar ya dakatar da ita Yana juyawa koina sbd kada Wani ya jisu yace ta fito ta biyosa.
Kai tsaye palon dd babba ya nufa tana bayansa qafafunta na hadewa cikin tsananin tsoro da fargaba tareda zuciyarta dake hanata Amma bazata iya barin Benazir dinta ta gidan rayuwar aurenta cikin tsoron ranar bayyanar gaskia da Ababa ya ringa juyata kaman babyn roba ba duk da tasan hukuncin Hakan mutuwa ne gareta idan Ababa yaji.
Suna shiga palon Abbakar ya sakawa kofar key ya nuna mata guri ta zauna ya wuce ciki Dan sanar da dd babban.
Zaune take Amma duk sakan zuciyarta dap take da Faso kirjinta ta fado,
Hakama rawar da qafafunta da hannuwanta keyi qaruwa takeyi.
Fitowa dd babba yasakata sauke Kanta qasa Hana Dafe hannuwanta dake qara rawa sosai kirjinta na bugawa.
Zaunawa yayi ahankali cikin nutsuwa Ya dago ya kalleta yana ganin yanda jikinta ke kakkarwa gabaki Daya da alama tana cikin mawuyacin hali na shakkan Abinda zata fada Daya danganci gaskiyar haihuwar data fada.
Shi Kansa zuciyarsa Neman sauya masa tinani takeyi sbd son sanin wace gaskiyar ce take magana Akai.
Daga ita har shi kasa gaisawa sukai da juna ahankali ta Bude baki tafara da fadin Asalin maraicin data taso acikinsa zuciyarta na rawa hawayen Datake riqewa suna cika idanuwanta Amma radadinsu ya hanasu saukowa fuskarta.
Halinda dasuka taso ita da 'yayanta tafara jero masa muryanta na rawa Yana iya Jiyo quncinta da rashin madafarta a muryarta.
Yanda yayanta suka mutu Daya bayan Daya ta fada masa tareda saukowa qasa ta zube gabansa sai alokacin hawayenta masu tsananin zafi suka sauko ta fada masa gaskiyar haihuwar Amnah tareda fashewa da Wani irin Kuka tana rokonsa akan Benazir marainiyar da batada kowa saisu a yanzu ce.
Barazanar da Ababa zai ringa yiwa Benazir da ita ta sanar masa tareda sake fashewa da Wani irin Kuka mara sauti da radadin zuciyar Datake cikin