Showing 9001 words to 12000 words out of 127646 words
dan haka babu musu ta yarda akai mata doctor na cigaba da tsokanarta.
Minti talatin dai-dai dayin allurar nan wani irin ciwon mara na azaba ya tasoma Lulu. A take jikinta ya fara vibration, tai wani irin dunƙulewa waje guda tana kiran “Wayyo ALLAH na Dada marata”. Yanda ta saki siririyar ƙararar sai da zuciyar Dada ta harba, hankali tashe tai amfani da wayar landline dake a ɗakin tai kiran doctor Olivia. Tamkar dama a kusa take babu jimawa sai gata ta faɗo, zuwa sannan jini ya ɓalena Lulu abin babu daɗin gani....
Iya wahala da azaba Lulu ta Shashi, inda da ƙyar aka samu jinin ya tsaya, akai mata allurar barci tare da gyarata, barcin wahala ne ya ɗauketa sai wata irin tagwayen ajiyar zuciya take saukewa a cikin barcin. Dada da duk ta shiga damuwa ta shiga tambayar doctor yanda ake ciki, Doctor ta tabbatar mata da aiki yayi ƙyau, dan yanzu haka dai ciki ya fita sai kuma ɗan jiyyar jiki da Lulun zatai na kwana biyu. Wata irin ajiyar zuciya mai nauyin gaske Dada ta sauke, a take tai kiran Alh. Sulaiman, a lokacin yana tare da su Hon. Misau suna tattauna batun Daddy. Kamar yaƙi ɗauka sai kuma dai ya ɗaga yana kaiwa kunne. A ɗan daƙile ya ce, “Dada nafa sanar miki inada uziri, mi kuma ya faru yanzun?”.
A ɗan ɗokance da ture maganarsa ta farko Dada ta ce, “Ai an kammala aiki yanzu haka ciki yabi gottern turawa kuma”. Ajiyar zuciya Alh. Sulaiman yayi da faɗin, “To maddala, na san zasu sallameku yau ku koma gida, zuwa anjima idan na samu nutsuwa zan kiraki”. Daga haka ya yanke wayar batare da ya jira tace wani abu ba. Hakan ya bama Dada haushi dan bata gama maganarta ba, amma sai batace komai ba bayan jan tsoki. Kamar yanda ya faɗa zuwa dare da Lulu ta sake farkawa aka sallamesu. Duk da Lulu najin jikinta cikin rashin ƙarfi kwata-kwata ga jiri na ɗinarta bata kawo komai a ranta ba. An basu magunguna suka hau cab zuwa gida. Sun samu Ummita ta gama gyara ko'ina sai tashin fresheners masu ƙamshi da gidan keyi, cikin ƙarfin hali Lulu ta ce ma Dada tana son tai wanka first, amma ta taimaka mata. Dada da kanta ta cuccuɗa Lulu tare da taimaka mata suka fito, kaya ma da taimakonta ta saka, tana gama sawa tasha tea ɗin da mai aikinta Ummita ta haɗa mata bisa umarnin Dada. Sosai ta sha shayin har ma abin yaso bama Dada mamaki, ita dai cikin sauke numfashi ta koma ta kwanta dan barci takeji har yanzun.
*_BAYAN KWANA UKU_*
Yau kawani uku kenan da zubar da cikin jikin Lulu da batasan da shi ba ba kuma tasan an zubar ba. Ta ɗan ƙarasa jiyyarta ta kwanaki biyu yayinda Dada ke kula da ita a duk motsinta. Yanda ta miƙe da wuri zai baka tabbacin zuwan Dada yay mata daɗi, dan akoda yaushe tana nane da ita. Duk da tana jin kewar ƴan gidansu musamman Daddy, Uncle Yousuf, Da Ammah sai take ƙoƙarin dakewa da sakama ranta haushinsu akan basa sonta. Ga kuma Dada a kaikaice tana sake cusa mata laifinsu hadda sharri. A duk sanda kuma Dada ta ɗakko zancen Smart sai Lulu taja tsaki da yamutsa fuska cikin shagwaɓa tacema Dada bata son ji, ita a daina mata koda zancensa. Hakan nama Dada daɗi da sake zaburar da ita cusa ma Lulu ƙiyayyar Smart a zuciya har ma da su Uncle Yousuf. Tun ma abin baya tasiri a ran Lulu har ya fara a randa take cika kwanaki biyar da samun lafiya a bazata sai ga Alh. Sulaiman da Tajuddeen. Lokacin tana kwance a falo tana kallo. A zahiri ta warke ragal. Sai dai tana jin wani irin kasala da son shan fruits, dan rigima ma yau sai cewa tai a mata kunun gyaɗa. Da Dada tace ina za'a samo wata gyaɗa anan sai ta sanya musu kuka na gaske. Dole Dada tai kiran wani saurayi ɗan ƙawarta da suma suke nan Canada ɗin amma asalinsu ƴan Nigeria ne ya bazama nemawa Lulu gyaɗa. Sai ko gashi ya samo, Ummita ta amsa ta haɗa mata kunun data buƙata sannan aka samu lafiya. Wannan kunu shine a gabanta har zuwa yanzu lokaci-lokaci takan zuba tasha abinta har sai taji yakai mata sannan ta ajiye. Sororo tai da ganin Uncle ɗin nata da Tajuddeen, dan ita dai ganin nasu yazo mata a bazata. Yanayinta babu yabo babu fallasa ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Sai kuma ta ɗan dubi Tajuddeen a yatsune tare da balla masa hararar kallon ƙurillar da taga yana mata. Sanye take da doguwar riga kalar ja da tabi jikinta ta lafe, sai rigar sanyi data ajiye gefenta kasancewar gidan akwai hitter dake ɗumama ko'ina. Rigar ta fisga ta sanya tare da komawa kwancenta kamar yanda take da. Sai dai ta danna wani ɗan maɓalli dake gefen kujerar ya bada ƙara sai ga Ummita da sauri ta fito da ga wani ɗaki tana faɗin, “Aunty kina buƙatar wani abu n...” ta kasa ƙarasawa saboda ganin baƙi. Batare da Lulu ta kalleta ba ta ce, “Ki sanarma Dada anyi baƙi”. Ummita data zube tana gaida su Tajuddeen ta amsa da to tana miƙewa ta nufi ɗakin da Dada da Lulun ke kwana.
Ta wutsiyar ido Alh. Sulaiman ke kallon Lulu da nazartar ta, ba yau ya fara fahimtar girman kai da izzar yarinyar ba irin ta uwarta da ma shegen ubanta ce. Dan duk da yake amsa sunan yayan mahaifiyarta bata wani sakewa da shi, hasalima a duk sanda suka haɗu takan dinga acting like tana jin haushinsa. Hakan yasa yake zargin ko mahaigunta ya sanar mata wani abu a kansa ne. Wata ƴar ƙaramar ƙwafa yayi ciki-ciki a ransa yana faɗin (Zan dawo dake cikin hankalinki ai yarinyabke da ubanki dama duk mai daure miki ƙugu). Tajuddeen kam kai tsaye ya kafe Lulu da kallo, itako duk da tana jin idanunsa a kanta tai biris da shi tamkar bama tasan ALLAH yay zamansa a falon ba da ga shi har ubansan. Laifin Tajuddeen ne ya shafi mahaifinsa Alh. Sulaiman a wajen Lulu, dan bama shi ba, duk wasu ƴan gidan su Tajuddeen Lulu ta tsanesu a dalilin Tajuddeen ɗin ba kamar yanda shi Alh. Sulaiman ke tunanin Daddy ya faɗama Lulun sirrinsa bane.
Cikin nuna mamaki Dada dake fitowa ta ce, “A'a wai dama da gaske ne kuna tafen ashe dai?”.
Murmushi Alh. Sulaiman yayi da amsa ma mahaifiyar tasa da “Wlhy kuwa Dada ai na tabbatar miki babu abinda zai hanamu zuwa. Idan muka gaisheki sai mu wuce mu duba Baba kuma duk da shi Tajuddeen zai dawo nan Canada ɗinne akwai aikin da zaiyi”. Dada bata samu damar bama ɗan nata amsa ba saboda miƙewar da jikanta yay Tajuddeen yaje ya rungumeta. Lulu da duk ke saurarensu gabanta ya faɗi jin wai Tajuddeen yazo aiki ne nan Canada. To lallai dolene kam tabar ƙasar nan kenan a wannan gaɓar. Dan bataga haɗin kifi da kaska ba tsakaninta da Tajuddeen bazasu taɓa kasancewa a inuwa guda ba. Tsam ta miƙe cike da izzar nan tata sai dai rashin ƙarfin jiki na ciwo duk ya cinyeta a tsaye ta ɗauki flaks ɗin kunun gyaɗarta ta bar falon. Su duka da kallo suka bita kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa. Dada ta katse shirun da faɗin, “Bara yarinyar nan ta shirya muku abinci ko. Sannunku da hanya”.
Bakin Tajuddeen a washe yana sauke nannauyar ajiyar zuciya da ga dawowa hayyacin bin kallon Lulu da yay da ido ya kalli kakar tasu. Ido ya kashe mata tare da mata nuni da ɗakin da Lulu ta shiga da baki. Dada tai ƙaramar dariya da faɗin, “To Alhaji zumuɗinka kadai bi komai a hankali, dan bamu san wane kalar barbaɗe shegen yaron nan yay mata ba, maybe bata gama dawowa cikin hankalinta ba ta kuma butsare mana a karo na biyu kadai san halin taurin kai irin na Mawaddat da shegen fitina”.
“Karki damu Grandma, komai zai tafi dai-dai kamar yanda aka tsarashi. Indai ni ne a wannan gaɓar babu garaje. Bamma san tasan komai har sai an ɗaura auren”.
Ƙaramar dariya Dada tayi, yayinda Alh. Sulaiman ya kura musa ido kawai, sai dai baice dasu komai ba.......✍️
_🤔To an taɓa aure akan aurene? Yau naga lukutar masifa Dada da Alh. Tsule fa babu man kai zasu iya ɗaurawa...🚴🚴🚴_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣
........Lulu bata sake fitowa falon ba tana a ɗaki, sai in lokacin sallah yayi ta tashi tayi, dan tunda ta dawo asibitin nan kuma sai hankalinta ya dawo jikinta sosai. Da lokacin sallah yayi kamar wadda ake zabura sai Smart yazo mata a rai, miƙewa take cikin jan ƙaramin tsaki da son kauda al'amarin sa tai sallarta. Alhamdullah game da shan kayan shaye-shayen ta ma tunda suka dawo asibitin tamkar wadda aka tsawatar mawa bata sake sha'awar shan wani abu ba dan sun gagareta. Hasalima data tuna sai zuciyarta tahau tashi kamar wadda ta tuno wani abinci. Wannan dalilin ne ya zare mata duk wani tunanin ɗaukar wani abu tasha ya bugar da ita. Sosai wannan zuwa na su Tajuddeen da jin zaiyi zaman aiki anan yasata shiga dogon tunani, bata sha'awar tunkarar Nigeria sam, dan harga ALLAH wani sashe na zuciyarta na tsoron haɗuwa da Uncle Yousuf, sannan kuma bazata iya cigaba da zama a ƙarƙashin inuwa ɗaya da Tajuddeen ba. Dolene tasan mafita na barin ƙasar zuwa wata ƙasa daban ta karasa dogon hutun data ɗauro ɗammarar yi har sai sanda taso ta waiwayi gida Nigeria sannan. Kasancewar anan ba wani an damu da dare ko rana bane dan akoda yaushe ba fasa sabgoginsu suke ba sai in sanyin gari ya hana hakan yasa Lulu tunanin ɗan fita yau tasha iska. Miƙewa tai duk da yanayi rashin ƙarfin jikin da take ji ta sake sabon shiri cikin wando da riga da jibgegiyar rigar sanyi mai hula. Turare taɗan ƙarama jikinta ta ɗauki ƙaramin ledan chocolate ɗinta ta saka a aljihun rigar bayan ta ɗaure igiyar takalmanta ta fito. Tajuddeen kawai ta samu zaune a falo yana daƙilar waya. Kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta. Shiko da sai da taɗan gittashi ƙamshinta ya dakar masa hanci ya sashi farga da ita da sauri ya ɗago. Ganinta da shirin fita ya sashi miƙewa da sauri yana faɗin, “Ƴammatan ina zuwa haka ba neman abokin rakkiya?”.
“Ba buƙata”.
Ta faɗa a daƙile tana ficewarta, kafin ya iso ƙofar ta maida ta rufe da sanya security ta baya tana hararar ƙofar da jan tsaki tai wucewarta. Sororo Tajuddeen ya tsaya bayan ya gama mummurɗa handle ɗin ƙofar ya tabbatar da ta kulle ta baya. Lips ɗinsa ya ciza da yanayin rashin jin daɗi ya koma ya zauna a inda ya taso. Itako Lulu cikin tura hannayenta dake sanye da Safa suma a aljihun rigarta ta fara tafiya bisa lafiyayyen titin street ɗin nasu a hankali dusar ƙanƙara na ɗan sauka mata a jiki ɗis-ɗis kaɗan-kaɗan. Duk da akwai sanyi sosai yanayin ya mata daɗi, dan rabonta da irin wannan fitar haka tun bayan gama jiyyar jikinta da Smart ya murza, tana kuma ɗan fara samun walwalar ta kwana biyu sabon yanayin ciwon nan ya sake kwantar da ita shima. Tayi nisa sosai da gidan ta samu wani shagon shan coffee ta shiga, coffee ɗin tasa aka kawo mata, sai dai tana kaisa bakinta taji zuciyarta ya fara tashi, a take ƴan cikinta suka shiga hautsinawa. Babu shiri ta baro gurin cikin tashin hankali bayan ta biyasu, duk yanda taso riƙe aman ya gagara dole ta koma cikin restroom nasu ta dinga sheƙasa har ɗan kunun gyaɗar da tasha a gida sai da ta zazzagar. Cikin galabaita ta samu ta wanke fuskarta ta fito dajan ƙafa. Can gefe ta samu ta sake zama tana maida numfashi ɗaɗɗaya zuciyarta a cunkushe da tunanin wai mike damunta haka ne?. Ita dai tunda take bata taɓa fuskantar kalar ciwo haka ba da amai. (Ni dai nace Hummm). Ta jima a shagon coffee ɗin kafin ta miƙe cikin ƙarfin hali ta sake nufo hanyar dawowa gida dan wani irin sanyi mai shiga jiki da ƙashi take jin na ratsata duk da yanda ta rufe duk jikinta da kariya harda su Safar hannu da facemask amma bata tsira ba. Da ƙyar ta iya kawo kanta gida, ta cire security ɗin data sakama ƙofar saboda Tajuddeen ta shigo cikin tangaɗi. Babu kowa a falon da alama Tajuddeen ya shige, gudun karma wani yazo ya sake damunta ya sata nufar bedroom ɗinta dan yau tayima Dada yaji akan bazata sake kwana a ɗakinta ba. Dan dama da nata zuwan Dadar ya sata komawa inda ta sauka kasancewar bata da lafiya. Gaba ɗaya hankalin Dada da Alh. Sulaiman da suka haɗe kansu a bedroom ɗin Lulun da tunanin bazata shigo nan ba koda ta dawo yanzu baya kan ƙofar, tattaunawa suke game da zancen cikin da suka saka aka zubar mata batare da tasan ma da cikin ba. Wani irin bugawa ƙirjin Lulu yay da ƙarfin gaske. Ta tsaya cak tamkar wadda aka dasa matsayin gunkin tarihi ba mutum mai numfashi ba tana cigaba da saurarensu. Kanta ne ya fara juyawa sannu-sannu ta fara ganin hajijiya babu zato sai jin faɗuwar abu sukai ƙasa yifff. A tare suka zaburo tare da kallon ƙofar cikin waro idanu.....
Bayan kamar awanni biyu ta dawo a hayyacinta, zuwa lokacin hatta da Tajuddeen na a ɗakin zaune a gefenta cikin damuwa dan har fuskarsa ta gagara ɓoyewa. Ɗaya bayan ɗaya ta gama binsu da kallo tamkar mai son tantancesu kafin ta maida idanun nata ta lumshe kawai batare data nuna alamar ta tashin ba. Hirar kakar tata da kawun nata ne suka shiga dawo mata dalla-dalla, ita Mawaddat ce keda ciki, ciki na haihuwar ɗan mutum, amma suka saka aka zubar da shi. To minene dalilinsu nayin hakan. Duk da a karan kanta bazatace son cikin take ko akasinsa ba, amma tanaji a ranta kamar ya kamata ace kafin su aikata zubar da shi a bari ta sani da kuma jin ta bakinta ai. Hannunta dake ajiye a saman cikin nata ta motsa a hankali, tare da sake matsar da shi ƙasa sosai ta shafa cikin. Wannan ne ya fargar da su Dada cewar ta farka. Gaba ɗayansu sukai kanta da sannu musamman Tajuddeen da Dada. Dan Alh. Sulaiman dai idanu kawai ya zuba mata batare da yace komai ba. Cikin damuwa Tajuddeen ke jera mata tambayar mike damunta? Ko zata tashi suje asibiti ne? Yanzu ina ke mata ciwo?. Idanun nata ta ɗan sake buɗewa ta kallesa, sai kuma ta maida abinta ta lumshe. Sake jera mata sannu da roƙon ta bari ya kaita asibitin yayi. Amma sai ta girgiza masa kanta kawai. Zai sake magana Alh. Sulaiman ya katseshi da faɗin, “Tajuddeen relax mana”. Shiru yay badan yaso ba, hakan yasa ɗakin komawa shiru. Lulu da gaba ɗaya take jin wani irin yanayi mai kama da jin zafi da ɗaci a zuciya ta sake buɗe idanunta da sukai ja akan Dada. Muryarta irin ta mara lafiya a dake ta ce, “Dada nice na samu ciki aka zubar?”. Ba Dada ba hatta Alh. Sulaiman sai da furucin nata ya razanashi. Kusan a tare suka kalli Tajuddeen da ya furta “Ciki kuma Mawaddat?!”. Maimakon amsa Tajuddeen ɗin Dada take kallo alamar jiran amsa daga gareta. Dada data ɗan daburce cikin inda-inda ta ce, “E... E... Eh hakanne Sweet heart. Mun...m...munji tausayinki ne da ganin halin da kike a ciki na wahalar ciwo. Sannan minene amfanin haihuwa da wancan sankaran shashashan yaron da ko kansa bai iya riƙewa ba sai baƙin talauci, ke akaran kanki ma baki isa haihuwar ba ai shekarunki nawa ma duka. Na biyu inaji a jikina bada yardarki aka samu cikin nan ba, sai dai in asiri yay miki tare da fyaɗe. Dan ke da bakinki kin tabbatar min baki taɓa bashi kan ki ba. Ki faɗa mana gaskiya, fyaɗe yayi miki ko?”.
Kai Lulu ta kauda tana mai lumshe idanunta batare data bama Dada amsa ba, dan wani irin zafinsu takeji kamar ta shaƙo ɗaya a cikinsu ta maƙure kawai, a mamakinsu sai ganin hawaye sukai na zirara ta gefen idonta yana sauka saman filon da take kai har a cikin kunnenta. Gaba ɗayansu babu wanda bai kasance a yanayin zama turus ba, musamman Tajuddeen da ke jin jikinsa na tsuma. So yake kawai yaji Lulu tace fyaɗe Smart yay mata, shiko ya ɗauki alwashin koda uwarsa yake yawo sai ya yagalgala masa rayuwa. Amma abin mamaki sai gashi iya lallaɓa Dada taima Lulu dan tace wani abu game da samuwar ciki taƙi tace komai. Da tagama zasu dameta sai taja bargo har saman kanta ta rufe kawai da faɗin “Not your business! Please live me alone”.
Wannan abin da tai ya ƙara sakasu a wasi-wasi, amma sai Alh. Sulaiman yace su manta da batunta tunda dai an ɗauki mataki, yanzu kawai abinda zasu maida hankali shine binciko inda Smart yake ya saketa a ɗaura aurenta da Tajuddeen. Sun gamsu da hakan, sai dai daga ƙarshe Dada ta bada shawaran in har fa anƙi ganin Smart dole ne su nufi Nigeria su makashi a kotu ta bama Lulu takardar saki kawai ko su nemoshi su dole ga amsa kiran kotu yazo ya bada ai. Nan ɗin ma sun gamsu, dan haka suka tsaya