Showing 48001 words to 51000 words out of 127646 words

Chapter 17 - Furar Danko Book 2 Hausa Novel Complete

Unknown   

19 Dec 2024

260

Da sauri ta buɗe idanun nata a daburce, dan yanda ya furta kalmar sai taji kamar ya haɗa da jinin jikinta ne ya zuƙe har ma da numfashi, kafin ta samu damar cewa komai Usman yay sallama. Amsa masa yay yana mai dafe goshinsa da faɗin, “Gaskiya baka iya zuwa ba”.
Ƙaramar dariya Lulu tai tana kauda kai, shi kuma ya harareta da bashi izinin shigowa bayan ya miƙa mata mayafin da ke ajiye gefenta da faɗin, “ALLAH yasa ma ba haka kike zama min a gabansa ba yana kallemin kayana”. Yanda yay maganar cikin ɓata fuska ya sakata sake sakin murmushi, cike da neman tunzurashi ta ce, “Mi kuma ya rage bayan shine mai karɓar haih....”
       “Mtsoww! Shut up!”.
     Ya faɗa a hasale yana balla mata harara fuska a gimtse. Dai-dai nan Usman ɗin ya ƙarasa shigowa, sama-sama ya bashi hannu suka gaisa, kafin ya ɗan juya yama Lulu tambayoyi game da yanayin jikinta. Ta tabbatar masa da Alhmdllh bata jin komai. Shima hamdalar yay yana ɗan duban Smart da murmushi, “Oga zamu iya wucewa masauki ko anan zaka kwana ka taya Madam jego? Dan itama lokacin barcinta yayi”.
       “Kaga dana ɓarke ɗinkin sai ku tara min jama'arku na likitoci kenan”. Smart ya bashi amsa da ɗan barkwanci duk da da gaske maganar Lulu ta sosa masa zuciya amma ya danne.
Ƙaramar dariya Usman yay da faɗin, “Ai kai oga ne zamu ɗaga maka ƙafa kodan Son ɗina AA”.
Murmushi Smart ya sake yi kawai bai ce komai ba. Usman kuma ya matsa ga Lulu ya mata allura da duk sauran abinda ya dace sukai mata sallama, gaba Usman yay ya barsa. Ganin yanda Smart ɗin ya raka bayansa da kallo mai kama da harara yasa Lulu saurin faɗin, “Nifa wasa nake maka kada ka ƙullacin bawan ALLAH bayan ƙoƙarin sa a kammu. Kana dai ganin a yanda yay min allura ma cike da taka tsantsan”.
      Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa da launinsu har ya canja. Batare da yace mata komai ba a karo na biyu ya ƙarasa gareta ya rungumeta tsam-tsam a jikinsa ta yanda dai bai taɓa mata ciwo ba. Su dukansu babu wanda bai sauke ajiyar zuciya ba, yayinda Smart ya shiga laluben lips nata. Da sauri ta janye jikinta saboda jiyo takun tahowa, shima sai ya miƙe dan dai-dai nan Ammah tai sallama. Gaban gadon Babyn ya koma tare da kama hannayensa ya fara tofa masa addu'oi. Har saida ya kammala sannan ya ɗago yana kallon Ammah da ke taimakawa Lulu ta kwanta yanda zataji daɗi. Sun ƙara haɗa ido da Lulun ta kauda kai shima ya kauda da ɗan salon taɓe baki yana wani lumshe idanunsa.....


*_NIGERIA_*

     Sosai jikin Dada ya ruɗe a safiyar yau dan haka hankalin ƴaƴanta a tashe yake matuƙa. Cikin ƙanƙanin lokaci aka shirya mata barin ƙasar. Baba Garko na Abuja a lokacin Uncle Khamil ya kira shi a ruɗe yana sanar masa zai tafi Kano jikin Dada ya tashi sosai. Duk da ya ji damuwa a ransa sai ya danne cikin nuna halin ko'in kula ya ce, “ALLAH ya bata lafiya” ya kashe wayar abinsa. Abinda Baban yay ya sake tada hankalin yaran. Dan sun sake tabbatar da har yanzu ransa a ɓace yake akan mahaifiyar tasu. Haka suka shirya wasu a cikinsu suka wuce da ita gwiwa a sage. Wanda aka bari a gida kuma suka bita da addu'a kafin suma subi bayansu da ga baya. Matansu kam addu'a suke ALLAH yasa da ga can ta wuce ko zasu huta da samun sukunin zama da mazajensu cikin ƴanci kamar kowacce mace a gidan aurenta. Dan gaskiya surukar tasu ta musu kane-kane a cikin rayuwar aurarrakin nasu....

        (To mudai munce ALLAH ya baki lafiya Dadansy).

       __________★

    Duk da zuciyarta a dagule take da wannan tafiya ta mijinta da kishiyarta da tafi tsana fiye da kowa a rayuwarta ta wani fannin hakan ya taimaketa, dan ta samu damar aiwatar da mugayen nufinta akan wanda suke wa taƙamar da tinƙaho. Saboda tayi alƙawarin kofa komanta zai ƙare ita sai taga bayan Smart da uwarsa. A haka ma dan bata san ainahin abinda ya kaisu UK ɗin ba kenan. Hankalin aunty amarya ya tashi da ganin kai-kawon da Umma ke yi, dan haka kawai zuciyarta ke ayyana mata kai-kawon bana banza bane ba. Su dukansu sun jima suna zargin Umma akan shige-shigen gidajen malamai. Dan a wasu lokutan sukan kasa gane kan mijin nasu ta koma sai ita kaɗai ce madubin dubawarsa. Sai sun dage da addu'a abin yay sauƙi kafin ta sake masa sabon aike. Wannan dalilin yasa a yanzu ɗin ma Aunty Amarya ta shiga damuwa. Sai dai ta rasa dawa zatayi maganar dan Mama ita ba gane kanta ake ba wasu lokutan sai a hankali ce. Ga shi su Maryam basa nan. Ganin abin nata cigaba da alamomi masu yawa ta ɗaga waya tai kiran aunty Bilkisu akan tazo dan ALLAH idan ta samu lokaci. Da sauri Aunty Bilkisu ta tabbatar mata da gatanan zuwa.
          Da yamma ko sai gata, sai dai ta nuna kamar daga wani waje take ta biyo gaishesu. Sama-sama Mama da Umma suka amsa mata gaisuwarta, dan suna cike da takaici da kishin tafiyar Abba da Ammah. Aunty Bilkisu bata nuna ta damu ba ta shiga ɗakin aunty Amarya abinta. Tsakanin aunty Bilkisu da aunty Amarya suna abune kamar ƙawaye, duk da aunty Bilkisun ta girmeta kaɗan, bayan sun gaisa babu ɓata lokaci suka shiga tattauna abinda ya tara su. Sosai hankalin Aunty Bilkisu ya tashi da bayanin aunty Amarya, duk sai ta rikice. Cikin kwantar da hankali aunty amarya ta ce, “Bilkisu dan ALLAH karki ruɗa kanki, mu nutsu muyi tunanin abinda ya dace, dan kinga dai bawai tabbas garemu ba zargi ne”.
        “Aunty wannan ai ya wuce zargi tunda har kinji tana ambatar sunan Hydar ɗin da matarsa. Wlhy nikam al'amarin Umma ya fara bani tsoro a gidan nan. Ko kin san kwanan nan sai da taje ta kaima kishiyata gulmar Ammah da har ta kaimu da yin faɗa. Alhaji ne ya tausheni da kar nazo gida na faɗa kamar zaimin kuka. Kuma ya tabbatar min da ai ta daɗe tana kai musu gwabsona dana Ammah kawai dai yanzu ne ALLAH ya tona asirinta. Akan wannan rigimar yanzu haka uwargidana na gidansu ya mata saki ɗaya”.
            “Innalillahi. Itako Umman Hannatu mi take son zama ne? Wlhy al'amarin ta na bani mamaki”.
      “Dolene abinta yake bada mamaki ai Aunty, ki duba fa yanda ta tada hankalinta a gidan nan tunda taji Hydar na ƙasar waje. Ni wlhy zuciyata ma har ta fara zarginta akan matsalar da yayta samun nan a baya. Kawai dai dan Ammah tace kar nayi magana ne”.
          “Eh ai tabakin Yayar gara a barta, ita da kanta halinta zai tsangwameta kowa ya shaida. Amma yanzu idan akaji a bakin wani a cikinmu za'a ɗauka sharrin kishi ne kawai. Kin san kuma Yaya ita komai nata a nutse ne bata son gaggawa. Shiyyasa yanzu ma kikaga na nemoki dan kota dawo bana son na fara mata maganar, duk da nasan zata fahimce ni”.
       “Hakane Aunty, yanzu to yaya zamuyi?”.
      “Addu'a zamu dage da ita, mu kuma saka a cigaba dama Aliyu shima har sanda su Yaya zasu dawo miji nata shawaran”.
    Aunty Bilkisu ta gamsu da shawaran aunty Amaryan, dan haka suka cigaba da tattaunawa. Bata bar gidan ba sai bayan sallar magrib........✍️

_Network kaje dan kanka. Na barka da ƙarfen da ake maƙalaka ehe🥱🥱🚴_.



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣6️⃣



.......Kamar yanda Daddy ya faɗi zasu tattauna da Smart tun a waya ya cika alkawari, dan washe gari tunda safe ya baro Abba da Uncle Yousuf ya sami Smart a gidan su Usman dan nan ya kawoshi. Sun gaisa cikin mutunta juna kafin su fara tattaunawa. A nutse Daddy ya fara ma Smart bayanin mafarin komai tsakaninsa da Sulaiman har zuwa yau da suke tare. Matuƙar girgiza Smart ya shiga, tare da jinjina ƙarfin halin Daddy da sake ganin kimarsa. Ya jure ɗaci da damuwa saboda kawai karya rama sharri da alkairi, saboda kare mutunci da lafiyar ahalinsa. Cikin zubda hawaye Daddy ya katse Smart da faɗin, “Abu ɗaya ne ke cimun zuciya a yanzu Aliyu shine cutar da matarka da nayi, kwarai da gaske na zalunci rayuwar Mawaddat dan rashin ilimin addini babbar naƙasu a rayuwar ɗan adam. Gara ace mutum bai san komai a limin boko ba dan wannan iya kar alfaharinka da shi shine duniya. Inajin kunyarta ta yanda a duk sanda na tunata nakanji hawaye na zubarmin tunda ba haka naima sauran ƴan uwanta ba. Wlhy alokacin idanuna ne suka rufe da iya tunanin kuɓutar da ita da ga sharrin Sulaiman ne kawai shiyyasa. Iya ƙoƙari Yousuf kuma yayi na ganin ta samu ilimin har malami ya nema mata a can Germany amma tsoron karda a haɗa baki da Malamin a cuta mata yasa na hana hakan. Ashe na manta UBANGIJI shine mai ikon tsarewa da killace bawa da ga sharrin masu makirci da ƙulle-ƙulle ba wai wayo ba. Domin nayi gudun gara na faɗa gidan zago. Dan ALLAH ka tayani bata haƙuri da neman gafararta, ka tayani gina mata sabuwar rayuwa, ka tayani horas da ita sababbin ɗabi'u, ka tayani ɗorata a hanyar tsira Aliyu kafin ɗan sauran lokacin da ya rage min ya ƙure mana ni da ita. Dan nasan da wahala na tsallake da ga tarkon Sulaiman saboda shu'umi ne na gaske. A yanzu haka ya ƙullaci mahaifinka akan maganar kotun nan, amma Alhamdullah babu abinda ya isa masa dan duk inda ya saka ƙafa na saka ƴan sandan farin kaya biye da shi, bama shi ba hatta ƙannenka dake gida dana ma'auri al'amarinsu na ƙarƙashin kulawar hukuma a duk sanda zasu bar gida. Kayi haƙuri kaima Aliyu na sakaka a rigimar da baku san mafarinta ba, shiyyasa raina fansa akan ganin wani abu bai cutar da ku ba a dalilina. Amma dan ALLAH ku yafe min duk laifina ne, da ace nayi nazari kafin na biyema Sulaiman tun farko maybe da duk bamu kai a irin wannan matakin ba.....”
          “Daddy jarabawace kawai, bawa kuma bai isa tsallake ƙaddararsa ba. Ba kamana laifin komai ba sai alkairi a rayuwa. Babu abinda zan iya cemaka sai godiya da cigaba da maka addu'a har ƙarshen numfashina. Ba laifinka bane Mutumin nan hatsabibin ne na gaske. Na fahimci hakan tun a haɗuwata da shi ta farko. Dan haka na zauna na karancesa yanda ya kamata, sai dai rashin sanin abinda ke a tsakaninku yasa ban taɓa wani yunƙuri ba. Amma tabbas na jima da lura da duk inda nake ana biye da ni, hakama ƙannena, na shiga tashin hankali saboda a tunanina Sulaiman ne, sai daga baya na fahimci ƴan sanda ne, sai dai babu irin bibiyar da ban musu ba sunƙi gayamin wanda ya sakasu, sai nai tunanin ma ko Uncle Yousuf ne ko Coach a lokacin, shiyyasa na zaɓi musu shiru a ganina wataran ai zan sani. Kamar yanda na faɗa maka ina son ka bar wannan case ɗin a hannuna yanzu, sannan ina son na bada shawara....”
       Cike da kulawa Daddy ya ce, “Ina jinka Aliyu, ka faɗi komi ke'a ranka kai tsaye tsakaninmu babu wani ɓoye-ɓoye”.
     Kai Smart ya jinjina tare da furzar da iska mai nauyi. “Wato Daddy irin su Sulaiman da hatsabibancinsu yaƙin sunƙuru yake buƙata a farkon fara wasa. Kamar yanda ka ɗauki masa salon shekarun da suka gabata na nuna baka san mi yake ciki ba wannan salon zamu cigaba a yanzu har zuwa wani mataki. Domin idan har akace za'ai masa fito-na-fito a shirye yake da wannan tun ba yanzu ba. Jirace yake da kai kace kule yace cass. Sannan mahaifinsa da kai hallacin shanye komai daminsa zai iya samun bugawar zuciya wlhy in har yaji kasuwancin da yake yi da kuma ketama autarsu mutunci da yayi. Ko kuma shi da kansa ya shirya hanyar halakasu idan yaga zaka cimma burin tona masa asiri. Kaga anyi gudun gara kenan an faɗa gidan zagon dai. Dan haka mu ajiye batun fito-na-fito ɗin nan mu lallaɓa Baba Garko ya sakar masa ɗansa, ka cigaba da nuna masa kana shakkar tasa, sauran yaƙin ka bar mana zamu ƙarasashi ni da Mawaddat da Uncle Yousuf in sha ALLAHU”.
      Idanu kawai Daddy ya zubama Smart, yama rasa abin faɗa akan wannan yaro. Lallai farar haihuwa tayi, dan shikam dole ya kira wannan yaro da farar haihuwa ga iyayensa. Smart ne da yaga kallon da Daddyn ke masa yay ƙasa da kansa yana murmushi kawai....


__________★

   Yau kam Ammah da kanta ta wanke ɗan jikanta ta gyarashi ɗaras ɗas. Yayinda Mamy ta gyara Mawaddat ita kuma Ummita ta shirya abinci. Lulu da ke jin jikinta wani iri tunda garin ALLAH ya waye cikin damuwa take sanarma Ammah ta mata addu'a gabanta sai faɗuwa yake. Jawo hannunta Ammah tai ta zaunar kusa da ita cikin damuwa da kulawa ta fara mata addu'oi, a hankali Lulu ta dinga samun nutsuwa har ta ɗan sha tea ta kuma shayar da AA abincinsa. Sun kammala kenan Ummita na gyara mata gashinta su Smart suka iso niƙi-niƙi da kayan da ya siyo bisa jagorancin Usman. Da mamaki Lulu ke kallonsu su da kayan, Usman ya nuna Smart cikin ɗaga hannu yana ficewa acewarsa bari yay kiran Dr Lameer.
         Lulu da ke jin faɗuwar gabanta na dawowa tun shigowar Smart ɗin ɗakin cikin dauriya ta ce, “Good morning” a takaice. Bai amsa mata ba sai da ya ɗauki AA tare da kaiwa zaune cikin kujerar dake a gaban gadon ya ɗan ma yaron kiss a goshi da kumatunsa sannan ya dubeta idanu ƙasa-ƙasa. Kamar wanda baya son motsa lips ɗinsa ya furta, “Haka ake gaishe da miji? Kamata yay kizo da gudu ki rungumeni da bani ƙyaƙyƙyawar sumba ki ce good morning rabin raina” yay maganar cikin kwaikwayon muryarta. Harara ta zuba masa da saurin faɗin, “ALLAH ya kiyasheni. Miye wani rabin rai babu ko daɗin ji.....”
        “Ki rantse ni ba rabin ranki bane”.
    “Kana buƙatar ganin likita kam”.
Murmushi ya saki da ɗan lumshe idanunsa yana gyara AA da ƙyau. “To muje a hakan, idan tai wari maji ai. Ina fatan kun tashi lafiya ke da baban Ammah?”.
      Cikin ɗan marairaice fuska ta ce, “Wane lafiya bayan ya hanamu barci, ka masa faɗa gaskiya ni bana son damuwa. ALLAH nima sai da nai kuka duk ya ruɗamu ga Ammah tayi tafiya ta gaji ya sata tanata faman jijjigarsa”.
             Gaba ɗaya neman harmutsa masa lissafi take da salon nata. Ƙaramin gyaran murya yay saboda jin yawu na neman sarƙeshi. Hakan yasa Lulu zuba masa ido, sai yay saurin janye nasa da ke neman canja launi cike da basarwa ya ɗan lakace kumatun AA da faɗin, “My Grandpa miyasa ka hanamin Mata barci? To da ga yau karna sake ji kaji Sadaukina. Kuma ka bama Maah-maah haƙuri” Sai kuma ya ɗago ya dubi Lulu data zuba musu ido, a yanayin ɗan ɗage gira ya ce, “Koda yake ni ya kamata ma na bada haƙurin nan a madadinsa” ya ƙare maganar yana tasowa. Ƙoƙarin sauka tai a gadon tana faɗin, “Ni dai ban gayyaceku ba”.
      Cikin ɗan murmushi ya ce, “Oh oh har ma takai gudunmu akeyi. Haƙuri da kawai zamu baki”.
   “Na haƙura basai kunzo ba”.
“Please mana Baby luv ko ɗuminki ki bari muji mana”.
            Dama ta fahimci wayon nasa kenan, dan haka ta maƙe kafaɗa kamar wata ƴar baby da faɗin, “Naƙi ɗin. Kai koma kunya bakaji a gaban ɗanka sai kayi taɓara. Ka rage halin nan wlhy rashin jin magana zalla”.
       Komawa yay ya zauna yana dariya da faɗin, “Kema ai rashin jin ne ya kaiki ga samo AA Mawashi. Haka kawai kin lalatama Ammah yaro, sai kawai ta ganki da yaro a hannu kuma dai tasan a inda kika samo.....”
           “What!!”
      Ta faɗa da sauri cikin daburcewa kamar Ammah na gabanta. Aiko ya shiga yin dariya a hankali. “Ni dai ai kowa yasan ni babu ruwana salihin ALLAH. Ina zaman zamana kikace sai anyi yaƙin ƙasa da ƙasa. Tsabar zalama baki fito a filin dagar ba sai da ganimar yaƙi wannan yarinya sai a barki kawai amma dai gaskiy....”
        Fillon data ɗauka zata jefa masa ya hanashi ƙarasawa, cikin ɗaga hannaye sama da sauri alamar surrender ya ce, “Yi hakuri nayi shiru, ke kam akwai kawaici nine zalamammen ga shi ma AA ni yabiyo tabbacin haka”.
         Hararsa tai da ajiye filon ta koma ta zauna. Sai kuma cikin damuwa da marairaicewa ta ce, “Da gaske dan ALLAH su Ammah suna ganin bani da kunya ko? Wata goma da kwanaki dayin aure na haifi yaro, wlhy nima abin na damuna, sai nake ganin abin yayi kusa da yawa kamar wata mayyar miji”.
      Daƙyar Smart ya iya danne dariyarsa. Dan ya fahimci tsakaninta da ALLAH take tambayar. Cikin kaɗa kai ya ce, “Kai kai baza'a suce ba Madam. Sai dai ma a kiraki da jaruma mai matuƙar hazaƙar ɗaukar darasi a wajen malaminta. Ammah kam ai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login