Showing 27001 words to 30000 words out of 85703 words
ya zauna da yata dole ba a sakar min yarinya dole ne mun gaji da talaucinsa makaryacin banza yazo da mota ya Mana fafa da kudi ashe karya ne a saketa idan an gaji Zaki Zo kina Mana ihu a gida,Mum Ido ta zaro tace abin har ya Kai haka? Ya wuce haka ma ehe sabo da Haka Kar na Kara jin kin ce ma ke surukata ce,Mum ta mike tace Allah ya kyauta ubangiji ya ganar daku,ameen sai me Kuma cewar Mama,Mum tace babu fita tayi daga gidan Suka hadu da Shehu yace ahhh Kece a gidan ya akayi baki jira na dawo ba? Sannu da zuwa yaushe Kika dawo? Mum tace hmm jiya naji abubuwa marasa dadi har Nusaiba ta Kai karar Aslam Office din Yan hisba Wai ya saketa shine nazo sasanci Amma Maman Yarinyar nan ta bani mamaki taci min mutunci,Shehu ya dinga bawa Mum hakuri yace wlh abinda nake fuskanta Nima kenan,sabo da mamansu nayi kuskuren Hana yarana abinci,Mum tace ashsha bai kamata ba Shehu ko me zata Yi ka dinga ciyar da yaranka,yace Inshaallah ai na Fara gyarawa yanzu Kam Ina Basu abinci amma fa kullum sai dai na auno sabo da idan na zube kayan abinci siyarwa takeyi duk da bai kamata na fada Miki ba amma Abu ne Wanda muke fuskanta Ni da danki ya kamata kisan Nima ta gagareni wlh ban Isa da ita da Nusaiba ba sauran yarana dai na Isa da su amma Banda Mama da Nusaiba kuyi hakuri yaushe za aje Office din Yan Hisban? Mama tace kayi bangarenka Kawai basa ji ne karka damu mun San Kai mutumin kirki ne wlh amma gobe Inshaallah Dana zai saki Nusaiba kowa ya huta,Shehu yace ba damuwa bazan ga laifinku ba,a nan Suka Yi sallama da Mum shi Kuma ya Shiga gida ya budewa Mama wutar masifa amma ko a jikinta tace a saki yata a huta da ya saketa zai sake ganinmu ne,Shehu yace Matukar aka saki Nusaiba to kema kin daina Jin Dadi a gidan nan,dalla rufe min baki me zaka iya, yace ana sakin Nusaiba kema wlh sai naci mutuncinki,Mama tace wlh ba inda zaka Yi Dani ko sakina kayi Ina nan gidan yarana nane sai nayi zaman Yaya na.
Yau Nusaiba da bala'inta ta dora tana cewa Allah ya Isa idan baka sakeni ba,Azzalumi ka kawo ni gidan wahala gidan talauci macuci tana ta zage zage.
Washe gari ranar da za a koma Wajen Yan Hisba Nusaiba ta riga kowa zuwa har da saka katon Hijab,Abbanta ta gani yazo Shehu sai Mama itama tazo,Mum tazo tare da Aslam,ana zuwa shugaban hisba yayi magana yace Nusaiba Kin nemi saki Kuma kin Fadi dalilinki mijinki bai da lafiya baya iya biya Miki bukatunki bashi da lafiya Nusaiba tace kwarai kuwa,Yace kin shirya biyansa kudin da ya kashe kafin aurenki har sadaki? Ko kin shirya Yi Masa wani auren? Nusaiba tace na shirya biyansa abinda ya kashe,Shehu yace kinyi asara Nusaiba yaushe Kika Zama haka,Aslam yayi murmushi Kawai,Dan hisba yace Aslam me kace kai? Yace ba damuwa taje na saketa Saki daya,Takarda ya rubuta ta saki ya mikawa Nusaiba ta karba harda saka Hannu biyu tace na gode Allah ya saka da Alkhairi Allah ya biya bukata na gode na gode wayyo Allah dadi kashe ni, ta kalli Mama tace Mama Kinga takardarta ki tayani murna yau an sallameni freedom ya samu,Mama ta karbi takardar sakin tana cewa kawo na sa Mata Albarka 'yata,Kowa kallonsu yake da mamaki a wajen,Shehu yace mahaukatan banza.
Aslam ya kalleta Kawai ransa a bace bayan an gama Shehu yace akwai shagon da Aslam ya budewa Uwar Yarinyar nan Nusaiba sabo da Haka a maida Masa da shagonsa,Yan hisba suka ce wannan kyauta yayi sai idan da Kansa yace a biya shi,ai kuwa Aslam yace a biya ni,Mama ta bude baki tace dama taimakonka badan Allah kayi ba Dan iskan yaro mutumin banza matsiyaci,Aslam bai saurari Mama ba yace hukuma ta sheda na barwa Shehu Baban Nusaiba shagon gida Kuma dama shi na gyarawa ba ku ba,Shehu yace bani mukullin shago ya Zama nawa,Mama tace akan shagon banza kaje can danka ne a ciki ka karbi shago kayi arziki da shi,Shehu yace ae naji,Aslam yace Ina bukatar sadaki na,Nusaiba nan take tace kawo account a maka transfer, Ya kalli Shehu yace Abba bata accnt dinka Shehu ya karanta nan take Nusaiba ta tura kudin Sadakin dubu dari,Aslam yace Suma kudin na bar maka Abba,Shehu yace Saura lefenka Aslam yace ai sutura ce tazo ta kwashe kayanta na bar mata,Mama tace to mun rabu karka sake na ganka a gidanmu,Aslam yace dole nazo gaida Abba Watarana,Shehu yace kwarai kuwa zamu ci gaba da zumuncin mu
Mum tace to Alhmdllh Muje Aslam aka kashe magana kowa ya Kama gabansa,Suna Fitowa Nusaiba ta Kira Sufyan tace an sake ni fa,Sufyan yace Alhmdllh Mama tace kashe wayar sai kinyi Idda yazo ta kashe kuwa Nusaiba sai gida suna murna da shewa Kamar Wanda aka musu gafara
Suna zuwa unguwar su ta Fara zuwa gidan su Charity duk gidan ba kowa sai Charity a gida tana zaune tana Jin radio sai ga Nusaiba tayi sallama amsawa tayi
Nusaiba ta bude jaka tare da dakko takardar sakinta ta mikawa Siyama tace kin gani na gama da shi idan kina sonsa kije ayi dake ni nan da kike gani na gama da shafinsa, Charity ta karanta tace Yanzu ke a tunaninki farincinki kenan? Nusaiba tace yes Yana da kyau ya cika Namiji amma baida kudi bashi da magana,takardar ta karbe tare da maida ta jaka tace gobe Zan ebo kayan sawata sabo da haka idan kina ciki kije ayi dake ni bani bukata ta juya ta fice,Siyama tayi Shuru tana tausayin Aslam Kamar taje gidan ta duba shi sai kuma ta fasa Sabo da shi kadai ne yanzu bai da Mata ko taje ma baza ta shiga cikin gidansa ba.
Bangaren Aslam kuwa Mum ya maida masukinta ya koma gidansa ya kwanta saman kujera shi kadai a gidan Kamar maye shi Kam yaga wulakancin mace ya zauna Yana tunani shi kadai Kamar maraya abin tausayi tashi yayi Kawai ya tafi gidan su Sabeer Abokinsa sabo da ya rage kadaici ,Babar Sabeer tace Aslam mutumin naka Yana bangarensa Dake su Sabeer masu rufin asiri ne Baban Sabeer Doctor ne,Sabeer Yana aiki shima a bangaren ministry of Finance Yana da motarsa me kyau baiyi aure ba amma Yana da budurwarsa Na'ima gaf suke da aure,Aslam Yana zuwa ya bawa Sabeer labarin saki,Sabeer yace Alhmdllh Kai Kam ai ka samu hutu dama Siyama ka aure,Aslam yace kawarta ce fa ni bayan nan ma yanzu ban shirya aure ba sai na huta,Sabeer yace hutun me Kuma yanzu ka Saba da mace gwara ka Fara Shirin aure dan Watarana zaka ji Kawai dumin jikin mace kake bukata,Sabeer yace rabu dani Kai na gaji,Nabeela ce ta shigo dakin Sabeer tare da ajiye musu abinci da lemo,Nabeela ta Kaduna tsohuwar budurwar Affan mamanta yayar Maman Sabeer ce ubansu daya,Nabeela watanta biyar a gidan mijinta Yusuf yayan Affan ya saketa.
Tana fita yace ko na hadaka da Nabeela Yar uwar mu ce bazawara sakin wawa ce kwana nan tayi barin Yan biyu bayan mijinta ya saketa cikin ya zube da zaka aureta ma,Aslam yace hmm amma Sabeer ya dage Yana ta faman yabon halayen Nabeela Yana so lallai sai ya hada aure tsakanin Aslam da Yar uwarsu Nabeela,yace har Babarta suna nan gidan mu sun dawo nan da Zama gaba daya sabo da can Kaduna su kadai ne a gidan,Yarinyar nan ta Sha wahala a hannun tsohon mijinta,Sabeer bai San hakkin Affan ne ke bibiyar Nabeela ba,Aslam dai Yana Jin Sabeer.
Yau Raudat Fitowa tayi zata siyo abu Affan ya fito da 3qtr da riga Armless ya ganta Murmushi ta Masa yace Hajiya Aunty Ina kwana,yau nice Hajiya Kuma Aunty a'a Kaine Yayana,Affan yace baza ta sabu ba bindiga a ruwa dole kece Aunty kuma Hajiya,yace Zaki iya sawa a toshe window din dana hada mana ke macece bai dace ba Kuma ba muharramata ba,Raudat tace a barshi Kawai Zan saka labile yau yace hakan ma yayi yanda kike so,tace Ina zaka je ne Haka ko Appointment ne? Murmushinsa me zauta Yan Mata ya saki yace ai banyi Shirin fita ba kalleni fa a haka Zan fita shago Zan je na siyo kayan tea nawa sun kare,Raudat tace nima can zani yace aha yayi gaba abinsa yana tafiyar gayu,Raudat daga baya ta karasa tana Shiga ciki ta dinga jido manya manyan Madara na gongoni kayan shayi na kirki komai ta hada ta Mika ATM card dinta aka zare kudin ta mikawa Affan katuwar ledar kayan tace gashi ka huta siye,ya kalleta ya kalli kayan yace Allah sarki Ashe mutuniyar kirki ce ke ban sani ba ta gari ce ga kamun Kai ba ruwanki da kowa da wata ce da yanzu mun gaji da ganin samari iri iri,Raudat tayi Murmushi kawai,ya karbi ledar yace gaki da kunya Kuwa Allah ya Miki Albarka ya karbe Kaya ya Kara gaba abinsa.
Liman ne ya samu Affan yau bayan Sallar asuba yace yaya budurwar taka Kuwa na jika Shuru? Affan yace naje ta wulakantani bani da kudi Wai, Liman yace da zaka yarda da na baka manager a gidan Mai na dana gama ginawa kwana nan,Affan yace me zai hana na karba manager fa na gode ubangiji ya Kara girma,Kamar Wasa sai ga Liman a cikin gidajen mansa ya bawa Affan manager a guda daya,Wanda Affan me zamarwa a shago ya sanarwa suka Yi sallama ya taya Affan murna Affan ya koma Zama a office dinsa Dake cikin gidan mai ai tunda ya fara Kama kudi wanka ya ninka na baya amma Liman Yana ganin gaskiya Yana ganin aiki da ci gaba a harkar,farin ciki yasa liman ya siyawa Affan Mota dalleliya ta matasa,Affan ya Karo wulakanci,ba ruwansa da Raudat yanzu sun daina fada baya shiga safgarta itama Haka sannan window dinsu ma ta saka labile,Affan Kara rike aikinsa yayi Hannu bibiyu sun Zama kamar Da da uba tsakaninsa da liman sanadin zuwa masallaci
Bayan kwanaki Raudat kullum bata da aiki sai tunanin Affan da shi take kwana da shi take tashi tun tana jurewa har ta kasa ta window take zuwa ta dan bude labilenta tayi ta leken Affan tana kallonsa tana Jin dadi a ranta.
Taji Sanda ya shigo da motarsa da sauri ta bude labilen window dinta kadan ta leka cikin palon Affan akan idonta ya shigo sanye cikin shadda Yar gaske laptop ce a hannunsa sai ledar take away na abinci a Palo ya ajiye ya nufi bedroom ai Raudat da gudu ta fada bedroom dinta ta window din ciki ta sake lekawa tana kallonsa tace na Shiga Uku meke damuna haka mutum bai damu Dani ba amma na damu da shi haka fa nayi akan Hussain na Kare a wahala,jikin window din ta bari ganin Yana kokarin cire kayan jikinsa
Bayan wasu satikai Liman ya Kira Affan zuwa gidansa,Affan yaje aka Masa iso palon baki ya shiga Suka gaisa da Liman,Liman yace Affan na yaba da hankalinka da irin rike Amanarka tabbas na yaba akwai wata Alfarma da Zan nema a wajenka fatan zaka min, Affan yace Inshaallah bazai gagara ba,yace Ina da babban aboki Yana da yarinya budurwa ce amma nutsatsiya ce ta dace da kai idan ba damuwa Ina so na hadaku aure,Affan yaji ba dadi bai zaci haka ba shi Kam baya son auren wata mace ko wace amma idan ya duba abinda liman ya Masa bazai iya kin tayinsa ba haka baya so yace na amince Mallam ai Kamar mahaifine a wajena nasan baza ka min zaben tumun dare ba, Liman ya washe baki yace na gode da ka daukeni a matsayin uba mahaifi ubangiji yaji Kan iyayenku,Affan yace a Ina matar da Zan aura take? Liman yace a nan kano take Babanta ya Dade da rasuwa a hannun yayan Babanta take,Affan yace ka bani address sai na Fara zuwa zance,Liman ya fara karantawa Affan gidan su Siyama, gumi ne ya Fara ketowa Affan yace Mallam ya sunanta? Yace Siyama,Affan gumi yake gashi ya amsa bazai iya yiwa liman Musu ba har ga Allah shi sunan ma Siyama yayi Masa local a harkarsa ta gayu, jikinsa a sanyaye ya basar yace shike nan zanje abinda mukayi da ita zan dawo na sanar maka,Liman yace Alhmdllh ka taimaki marainiyar Allah tausayi suke bani Babanta abokina ne amini,Affan dai ya tafi gida jiki ba kwari.
Raudat yau tana compound ita da Landlady suna Hira Affan ya shigo da motarsa a fusace yayi parking ya fito cikin bacin rai ya shiga part dinsa yana huci,Raudat ta tsura Masa Ido har ya kule, Landlady tace yau Baban wanka meke damunsa haka Kinga yanda yake fushi,Ni abin mamaki ma a Ina yake samun kudi yanzu Kamar fa yanzu yana zuwa wajen aiki duk da ba abinda ya iya sai karya amma a Ina yake samo kudin Kar dai ko barawo ne? Raudat ta bata rai tace Allah ya tsare min shi da Zama barawo Kuma Yana zuwa aikinsa babban aiki ma ki daina fatar Masa masifa ehe ta mike ta Shige part dinta da sauri tana yiwa landlady masifa,Landlady ta bude baki tace me nake gani haka mutanen da kullum basu da aiki sai fada amma yanzu sun daina Raudat ma wani Kare shi takeyi ita da take zaginsa tana gulmarsa yau taki yarda a aibata Affan harda Jin haushina uhm to meke faruwa tsakaninsu oho.
Aisha bayan tayi idda tayi sabon bazawari Bashir,Bashir Yana da rufin asiri domin lecturer ne yana da Mata daya da yaransa biyu,Bashir Maganar aure tana kankama ya tura manya ba bata lokaci aka sa ranar aure da wuri Maman Aisha ta dage sai da aka daura auren Aisha da Bashir sabo da ta isheta a gidan sai da tayi nadamar zuga Aisha ta dawo gabanta sabo da rashin kunyar da Aisha ke mata,Bashir ya Kama gidansa me dan kyau na Amarya sati na zagayowa aka yiwa Amarya Aisha jere Yan Uwa da kawayenta suka rakata dakin mijinta cikin motoci uku da ango Bashir ya turo.
Ango ya shigo Suka ci Suka Sha tare da gabatar da Nafila sannan ya Fara soyewa da Aisha,ranar Aisha taji wahala mugun Hariji ne na gaske Ita Farooq ba haka yake Mata ba abinsu dai dai da dai dai,gashi Bashir baya Wasa da jikinta wajen jiyar da ita Dadi Sabanin Farooq da yake zama yayi Wasa da ita sosai Kuma yanda yaji Dadi haka yake Mata itama sai taji dadi ta gamsu ya iya sarrafata sosai sabanin Bashir da Kawai Kansa shi Yana Jin dadi shi ba ruwansa mace ko ta gamsu ko bata gamsu ba shi ba ruwansa,Ranar kwana yayi Yana gurzar Aisha har sai data dawo tana tureshi tana cewa zafi dan Allah ka bari sai da ya Mata rauni ya hakura.
Washe gari da safe ya Dora daga inda ya tsaya har sai da Aisha ta koma kuka kawai tana rokonsa ya kyaleta gashi da kekasashe sai jaraba
Bayan sati daya Aslam bai je gidan su Siyama ba itama bata duba shi ba,ji yayi bai kyauta ba yace yau da Yamma zaije ya gaida Siyama,Siyama kasa Zama tayi bata ji Aslam ba ko bai da lafiya bata sani ba,ana gama abinci tayi wanka tare da shiryawa cikin atamfa sabuwa karama riga da skert ta yafa mayafi tayi kyau matuka ta zuba shinkafa da miyar da ta dafa ta zuba salat a Daya robar ta shirya komai a ledarta ta fito ta tsaya ta siyi kifi soyayye manya me zafi na dubu daya ta saka a ledar ta shiga Napep sai gidan Aslam,shi Kuma yayi wanka sosai ya Sha kana Nan kaya ya zuba kyau abinka ga me kyau da aji ya bude kofa da Niyyar zuwa gidan su Siyama sai ya ganta tana Shirin biyan me Napep kudi,Me Napep ta tsayar tace to gashi ma na ganshi karka tafi tsaya ka maidani gida,Aslam ne yace me Napep jeka Zan maidata,Siyama tace bafa shiga gidanka zanyi ba yanzu baka da Mata bazan shiga gidan Gwauro ba,Murmushi Aslam yayi yace me Napep jeka Kawai don't mind her, Me Napep yayi gaba abinsa,Siyama ta tsaya a gaban Aslam ya kalleta yace kina Jin dadi Siyama irin wannan wanka haka,dariya tayi ba shiri tare da Mika Masa ledar abincin tace tafiya zanyi ni,yace Kinga nan wajen duk student ne ki saki jikinki ga waje can mu zauna to a waje,Kan wani tudun siminti me Fadi Suka zauna ya bude ledar ya dakko abincinsa a wajen ya fara ci ya saka kifinsa soyayye Yana ci yace kamar kin San yunwa nake ji,Siyama ta kalle shi tace karka yabi yanda na iya girki ni bana so ma yanzu, Wai dan ya yabeta taji bai yaba ba shi yasa ta Fara Masa hannunka me Sanda,Dariya Aslam ya fara sosai,tace ae Kar dai ka yabeni nace, fuskarta yake kallo yasa hannu a hancinta ya cire Mata wani dan zare baki da ya makale mata,sai da ya cinye abincin tas tana kallo sannan ya Shiga gidansa ya Sha ruwa ya fito ya sameta yace tashi muje yawo,Siyama ta mike Suka jera suna tafiya suna Shan iskar gari suna tafiya Kamar saurayi da budurwa,Siyama tace kawata dai ta matsa an saketa, Aslam yace tayiwa kanta ta rasa saurayi me tashe,Siyama ta kyalkyale da dariya har da durkusawa tana dukawa kasa tana dariya,Aslam yace get up sarkin dariya ya riko hannunta tare da janta sama ta mike tana kwace hannunta,sai Yamma likis Siyama tace zata tafi Napep ya tare Mata ta shiga shima ya Shiga tace ya naga ka shigo Kuma?
Yace gida Zan kaiki da kaina Suka tafi tare again Suna sauka a Napep Suka yi arba da Nusaiba da Mama sun dawo daga unguwa,Mama ta nuna Siyama da hannu tace ke