Showing 9001 words to 12000 words out of 85703 words

Chapter 4 - Auren Mu Book 1 Hausa Novel Complete

25 Jan 2025

602

dubu dari uku Kuma ko ficika bai bata ba,idan tayi yaji ta tafi ta barwa wa yaranta ga yarta har sati guda shuru,Mama ta kwana takeyi tana kuka tana kaiwa Allah kukanta.

Charity idonsu duk ya kumbura sabo da kuka basu ga kowa ba Kuma an hanasu fita,Oga zai iya sati biyu a gida ba tare da ya leko ko compound ba Haka yake shi,Sun wanke kayansu ya bushe sun maida shi jikiksu bayan sunyi wanka,Palo Suka dawo Suka zauna babu Wacce tayiwa Yar uwarta magana sunyi jugum jugum a Palo,Tv tana yi Amma ko kallonta basu Yi,kamshi suka ji ya mamaye palon,wani me uban kyau Suka gani yana sakkowa daga steps sanye yake cikin wani silk doguwar Riga Kuma armless gefe da gefe an tsagata Silver color takalminsa ma haka sumarsa ta Sha gyara na musamman fadar kyawunsa bata baki ne komai nasa na daban ne,sheki Kawai yake da walwali,kwarjininsa ya kamasu Suka kasa magana har ya samu kujera ya zauna irin Zama na isassu na masu Hannu da shuni kana gani kasan Hutu ya ratsa shi.

Gyaran murya yayi kadan lokacin Charity tace Ina yini cike da Ladabi Nusaiba Kuwa ta kafe shi da Ido tana kallonsa sai da Charity ta dan bigi hannunta sannan tace Ina kwana au na manta Ina yini? A takaice ya amsa ya kalli Nusaiba yace ke kina kama da Baban Mum da gani jikarsa ce ko?,da sauri Nusaiba tace ae,ya kalli Charity yace ke da alama Yar Hajjo ce ta gangare ko? Charity tace ae,yace sorry Allah yaji kanta,Charity tace Ameen harda kuka dan a barsu su tafi tace ka tuna min da babana Yana can shi daya gwara na koma, Oga yace har Kun gaji baza ku tafi yanzu ba ya Dace ku huta sosai ya furta tare da mikewa ya fice suna ji ya shiga mota, Nusaiba suka sake fashewa da kuka,tunda ya fita bai dawo ba sai tsakar dare sunyi bacci lokacin harda siyo musu kayan makulashe da safe suna tashi suka gani a bakin kofar su Leda guda, Charity tace wlh da wannan kayan dadin gwara muna gidan Iyayenmu,Nusaiba ta kalleta tace hmm ai ni abin ya isheni gashi Muna fadar gaskiya za a kamamu sai gidan kaso masu kudi zasu Yi tunanin ma da abinda ya kawo mu,ai Kar mu sake mu fada Kuma Kinga Yana kamamu sai Iyayenmu sunji abinda muke yi,Nusaiba tace badluck, har suka gaji suka fito suna zaga gidan ko Ina sai da suka gani sun Sha kallo amma Sam abin baya birge su burunsu su koma gida,Palo suka koma sai gashi a zaune Yana kallon film sannan Yana latsa wayarsa.

Zama suka Yi can nesa da shi yace hope Kuna Jin dadin birni ya furta Yana kallon Nusaiba, Charity tace sosai ma Alhmdllh amma gida muke so mu tafi yau Iyayenmu zasu Mana fada,Ogan yace ai Indai kunce a nan kuke ba matsala kadaici ya min yawa kuyi zamanku kwa dan ebe min kewa ko ba komai na dinga Jin motsin mutane, Nusaiba ce ta kalli Charity suka hada Ido idanuwansu ya ciko da kwalla zasu Yi kuka ya tashi ya haura sama shi dama ya gaji da Shuru shi kadai a gida ga Yan uwa sunzo yaji motsin mutane ko da na yan satikai ne, Yana fita Charity tace kamar fa wannan mutumin kwakwalwarsa a takashinsa take ta kowa a kansa aka Masa brain amma Banda shi tasa a takashi aka Masa ita baya tunanin Iyayen nu chab

Aisha ce ta shiga motarta tana tukawa a layin har makwafta suka tsiri zuwa suna gaida su Sabo da aga ta siyi mota ko Ina da key a hannunta tana karkadawa,Sunday Yana gida Aisha anci gayu ta fito tace Maggi fa ya Kare sannan ba kayan miya ko yaji Banda shi bare nayi Mana shinkafa da wake,Farooq yace Wai ku Mata me yasa baku da hankali ne sau Nawa Ina fada miki idan Abu ya kusa karewa ki sanar min amma kinki ji sai komai ya Kare kat Zaki zo ki fada min to yanzu kin San wata yayi nisa ba kudi sai mu yini haka ya furta Yana Jan tsaki,Aisha tace Farooq kafa isheni tsakani da Allah na gaji Kai ba haihuwa kake ba how many years? 5yrs da auren mu maimakon ka lallaba ni sabo da nice ke hakuri Ina taimaka maka wajen Zama da Kai ba haihuwa Alfarma fa nake maka,for how long Zan dinga jira ba haihuwa ta juya ta saka Hijab ta fice ba ko neman izini haka tasa kudinta tayi cefane ta dafa abincinta ita kadai taci na Rana ta boye na dare Yana kallonta,tashi yayi ya fice zuwa gidan Abokinsa a can yaci ya koshi,tsakanin Aisha da Farooq an rasa waye me gaskiya tsakaninsu idan wannan yayi rashin mutunci gobe wannan ne zaiyi kullum basa shiri abinda ya damu Farooq irin gorin haihuwar da Aisha take Masa kullum,kwana biyu Babar Aisha tazo gidan suna dakin Aisha Babarta tace ke dai anyi shashasha mene amfanin aurenki da Farooq mutumin da baya haihuwa kunje asibiti yafi a irga ance a shine ai ya kamata kisa ya sakeki,ribar aure ai haihuwa ce tun wuri kisan me kike ciki,Babar Aisha haka ta gama zuga yarta daga ranar Aisha ta daina girki Farooq Yana Mata magana sai masifa tace juya Wanda baya haihuwa ka sakeni tun baya damuwa har abin ya dameshi ya sanar da Babarsa tace yayi hakuri Kawai kowa haka yake hakuri,da a baya suna yin Dan fadansu su shirya haka Yar karyar su dai sukeyi yanzu duk Aisha ta canja ba mutunci Kawai a sake ta taje ta samu me haihuwa.

Affan ne ya fito yasha wata shadda fara yayi mugun kyau Yana kamshi Raudat itama ta fito cikin farin lace zata tafi wajen aiki Kawai taga Affan da fararen kaya Ido suka hada tace Allah ya kiyaye na saka Kaya kala daya da Kai God for bid ta juya cikin fushi ta canja wata blue atamfa ta fito Yana tsaye da mamaki Tsaki yaja ya juya zai fita tace masu appointment kullum Ina da appointment kullum meeting ba uwar komai a kasa ba Sisi,kallon baki Isa ba ya Mata yace Banda lokacinki ya Bude karamar kofar gate ya fice,ita Kuma ta bude gate ta fita da motarta yace arga akwarabas da na Shiga wannan motar gwara na tafi a kafa,Tsaki ta ja tare da Shiga motarta tazo ta gabansa Malam bani hanya gurgu kawai masu mota suke da kafa ta daga glass din motarta sama tayi gaba.

Yau kwanan su Charity goma Sha biyu da bacewa Mama ta rame ta lalace ga bakin cikin Shehu ga bacin rai yarta ta bace Addua kullum suke ba dare ba rana,Bangaren Charity Kuwa Matar kanin Babanta wacce take Kira da Anty cewa tayi ban yarda ba Dauda yarka karuwanci ta tafi Siyama duniya Kawai ta shiga,nima Ina zargin haka cewar Dauda, Su Nusaiba kuwa sunfi sati daya basu ga ko alamar Oga ba sunci kukan har sun gaji,me aikin ma da suke gani yau ta tafi ganin gida sai nan da kwana biyu zata dawo sai ranar Suka ga Oga ya fito daga dakinsa ya musu murmushinsa me kayatarwa yace Hey,suka kalle shi Kawai yace me aiki yau ta tafi kuyi hakuri sai jibi sai ku tafi idan Kun tafi babu me gyara min gida ni Kuma bana son kazanta Dan Allah ku gyara gidan nan ya juya tare da komawa sama,ba yanda Suka iya Haka suka hau gyara ko Ina na gidan

Bayansu ciwo suna gyara garden Nusaiba ta rike bayanta tana Nishi tace gwara tallan kosai na sau dubu da irin wannan aikin, Charity tace hmm ai nayi missing tallan Alala ashe haka talla yake da sauki kana zaune za a Zo a siya,tun ba ma an soya ba kafin ka tafi tallan sai kaci ka koshi cewar Nusaiba itama
Ai sai ma Ina zubawa mutane Ina daga zaune abina da yajina a gefe,daina tuna min cewar Charity suka ci gaba da uban aikin gidan




Ku dinga sharhi please novel zai Fara wuta nan gaba





AsmaBaffa
[4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️

21-25


Official

By
AsmaBaffa




Page naki ne
MRS CHIEF







Biki Saura kwana uku Charity taga ba a sata a harkar itama bata Shiga ba uzurinta take yi,ana gobe daurin aure Nusaiba tazo gidan su Charity tace kinki zuwa ana ta shagali ba ke,Charity tace kice ana ta soya kwankwason rago,wa yake ta wani rago ana fada Miki kwankwason bijimin sa,dariya tayi ta shirya tare da yiwa Aunty sallama suka tafi,leshin da Nusaiba ta sa aka dinkama Charity ta Bata tace gashi shi Zaki sa da safe ni na Kai Miki dinki me tsada aka Miki, Charity ta ajiye Kaya a gefe Nusaiba tace an fa goge su ki Adana Kaya masu tsada ne fa sai ana kula,Charity tace hmm kawai,Nusaiba tace Ni tsoro ma nake ji Kar ki fini kyau ranar bikin yanda kike farar nan kyakyawa Ni Kuwa wankan tarwada da ma nice ke Charity,Siyama tayi dariya Nusaiba ta sake cewa ji dimple dinki sis gaskiya ki godewa Allah ya Miki baiwa,Siyama tace kema ai kyakyawa ce Nusaiba hancinki ai yafi nawa tsayi,Ni ba Fara ba Yaushe ma na Kama kafarki,sai gashi a hakan me kudin ke yace Yana so ba farar ba ko ta nan ai Kya godewa Allah ni da kin sani ma dinkin Riga da wando Kika min ban iya sa Riga da skert ko da zani ba kin sani,Baki Isa ba bikina guda ki sa Riga da wando bazai yuwu ba shegen duwawunki su ja hankalin mijina,Siyama tace da Zan ja hankalinsa ai da tuni ya gani ki daina kishi dani wlh sister bazan taba cutarki ba,Nan ta kalli Lefe akwati kusan ashirin aka kawowa Nusaiba.

A gidan charity ta kwana duk wani aiki da ita akeyi tana gaba gaba ranar daurin aure 11am za a daura su Charity an Sha kyau tafi amaryar kyau duk da cewa Amarya me makeup tazo ta Mata nan take Nusaiba ta bata rai ganin Charity tayi kyau cikin Riga da skert din less kawayensu duk sunci kwalliya sun Zo Basu sa anko ba Basu da kudin siya,Ango da best friend dinsa Sabeer sun gayyaci abokai Nan da nan masallacin kusa da gidan ya cika da mutane ko Ina Yan gayu ne da manyan masu kudi lokaci na Yi aka daura auren Aslam Mu'az da Amarya Nusaiba Usman,kowa yayi mamakin Wai Aslam ne zai auro mace Yar talakawa haka Basu shigo gidan ba Suka wuce reception kowa a can yaci ya sha daga nan abokai suka wuce gidan da suke angwanci.

Nusaiba haka aka yini ana hada hada sai 5pm duk Suka yi wanka aka Fara Shirin Kai Amarya,Shehu yasa yarsa a daki ya dinga Mata Nasiha yace ki zauna lafiya da mijinki Nusaiba Allah ya Miki zabi,ki rike mijinki da Yan Uwansa babu batun Maganar son kudi a cikin aure idan ka auri mace ko mace tayi aureka baka fata ku rabu sannan zaka tsaya ka jure samunsa da rashinsa ki Zama mace me tunani ke ba yarinya bace kin girma kin wuce shekara ashirin ki San me kike, Mahaifiyarki Aminatu kin San mu Yan asalin Rogo ne dake nan Kano,sanda na ganta Ina sonta Ina da kudi lokacin kasuwanci Yana gara min na aureta Bayan na aureta na hadu da karayar arziki daga lokacin Mamanku ta dinga wulakantani tana ci min mutunci sabo da bani da kwandala,bayan wasu shekaru Allah yasa kudina ya dawo daga nan Kuma kauna ta dawo ta dinga nuna min so Sabo da kudina shi yasa Kika ga na fita safgarta gaba Daya ba karamin wulakantani tayi ba lokacin da Banda shi to karki haka Nusaiba ki zauna lafiya a nan dai yayi ta Mata fada ita Kuwa Mama ance ga Amarya ko Zaki Mata fada,Mama tace mu yaranmu ai tun suna gabanmu mun Gama musu fada da can basu ji nasiha ba sai yanzu da ake Shirin kaita dakinta, menene basu sani ba na zaman duniya ku tafi Kawai a kaita zata Yi zamanta daram,Yan Uwan Shehu da Yan Uwan Mama Suka fita da Amarya sai kawaye motoci ne lafiyayyu sunfi talatin aka dauki Amarya zuwa gidan mijinta.

Duk Wanda yaga gidan sai ya kasa rufe baki,Amarya Kuwa tun a mota ta Fara cewa kunga tun gidan da Muka sani ne tun Ina budurwa bai canja komai na gidan ba Amarya guda ai ya kamata ace an canja komai na gidan tana magana kasa kasa an zaci kuka ma take Yi,ko Ina kamshi ke tashi na gidan ga Amarya ta Sha gyara bayan Yan Kai Amarya sun gama ganin gida suna ta Santi Suka fito Suka tafi gaba Daya har Charity bata zauna ba,Ango ne ya shigo bayan Sallar Isha ya Sha wanka cikin shadda Yar gaske sky Yana tafiya cikin takamarsa da ya Saba Kyau Kam ba a magana Kamar shi yayi kansa,bedroom dinsa ya wuce direct ya iske Amarya abar kaunarsa a zaune saman makeken gadonsa,a gefen gadon ya zauna ya Kare Mata kallo cike da Murmushi,Hannu yasa tare da Bude mayafin data rufe fuska da shi fuskarsa ya Dora a saitin wuyanta Yana shakar kamshinta a hankali ya furta a I love you Nusaiba tace me too,wuyanta ya fara kissing Kamar Wasa Yana binta da sumbata Yana shafata jikinta sai rawa yake yana yi har ya fara cire Mata sutura a hankali Yana tsotsar bakinta Yana so suyi Sallah suci kayan makulashe amma ya kasa a cikin gaggawa yake bai iya hakura,Nusaiba tana ganin kamar Wasa taga da gaske yake,a hankali tace ji nake sai munje kasar waje zamu Fara amarcin,wacce irin kasar waje ya tambaya Yana shafata,tace ban gane wacce ba kasar waje dai ai ji nake acan zamu Yi Honeymoon?, A'a gidan zuma zamuyi ba Honeymoon ba cewar Aslam ya furta da Wasa Yana ci gaba da abinda yake,Boobs dinta ya cafka basu da wani girma ma Yan kuyas a hannunsa haka ya dinga murzasu,Nusaiba kasa komai tayi kamar gunki haka yayi kidansa da rawarsa har ya samu ya shigeta yau ta yabawa aya zakinta Harijine sosai bai kawowa da wuri tayi kukanta ta hakura sai da ya samu gamsuwa sannan ya lallabata suka ci abin dadin bayan sunyi wanka tare da tsarkake jikinsu Yana ta yabonta tana Jin Dadi.

Bayan kwana biyu Nusaiba taga Shuru bai da Niyyar kaita kasar waje tana zaune a Palo ta Sha gayu ya fito yace wow you look good tayi Murmushi ya zauna a gefenta tace har yanzu banji ka Fara cewa mu Fara Shirin Visa ba,Aslam yace ta me fa? Honeymoon Mana ya kamata ace Muna kasar waje yanzu,Ganin ta dameshi da zancen kasar waje baiyi niyya ba Amma sabo da a zauna lafiya yace ba komai zamuje Saudiya ya Kika gani? Kallonsa tayi tace Saudiya? Makkah kake nufi? Ibada zamu je Yi kenan? Ni ban shirya zuwa Makkah ba turai zaka kaini irin su Paris,Germerny etc kana wani Maganar Saudiya shike Nan kullum Muna masallaci bazan je ba ta mike tsaye tace ka rike kudinka bazan je ba Indai Makkah ce ni na taba ganin me kudi Dan tsumulmula ma irinka,Baki Aslam ya Bude cike da mamaki duk kudin da ya kashe Mata da danginsa dan tsumulmula ne shi gaba Daya sai abin ya daure Masa kai sabo da ya samu Yar tarbiyya me nutsuwa ya nemi Yar talakawa irin Nusaiba Ashe gwara Yan masu arzikin ma.

Tsayawa yayi Kawai Yana Shan mamaki just 3days da aure har an Fara fada,sharewa yayi ya hakura ya rabu da ita suna soyayyarsu har Suka cika sati biyu da aure Nusaiba ta shirya cikin tsadadaddjen material blue and purple ta Sha kyau ta fito sanye da takalmi me tsini da jaka ta yafa Dan siririn mayafi,Aslam bai fiye fita ba Yana gida ta same shi a bedroom dinsa Yana Shirin fita tace Baby kudin gyaran jiki zaka bani daga nan Zan biya a min make up,okay ya furta ya irga dubu ashirin ya bata,galala ta karbi kudin tace dubu ashirin kacal gyaran jiki fa nace da kwalliya,dubu biyar ya Kara Mata tace Bari dai nayi manage duk da Haka basu Isa ba,Kawai kallonta yake da mamaki,tace yawwa na manta yau Mama zata Zo da kannena anjima da Yamma,yace Allah ya kawosu lafiya Ina gida ai lokacin Zan Dan je Office na dawo Alright,ta zabi key cikin motocinsa ta Kira driver Suka fita ba inda taje wani gyaran jiki bank taje ta saka kudin a accnt dinta ta dawo gida.

Tana dawowa ta sa me aiki ta shirya lafiyayyen abinci dama bata girki Bata aikin komai,Mama ce tazo gidan tare da Ihsan da Ameer Nusaiba ta rude tana musu Sannu da zuwa ta mike ta shiga kitchen ta cika musu gabansu da kayan Dadi sunci sun Sha Mama tace wannan irin kyau haka Nusaiba kin ganki Kuwa Alhmdllh 'yata tayi goshi,Mama ta mike tana rawa da Waka Kai 'yata tayi goshi....Yata tayi goshi...ah..ahhh....Nusaiba tana tayata suna ta faman shewa,Mama tace ya accnt iceko ya fara Nauyi? Nusaiba ta nuna Mata Alert suka tuntsire da dariya,Ameer da Ihsan Baki suka tabe,Ameer yace wlh da nine shi sakinki zanyi daga kaiki ko yaushe karbar kudi,auren miji me kudi hauka ne,Ihsan ma tace duk tallan kosan da kike Yi kin manta kenan Mama nan kwanan nan kike siyar da gasara kullum kuka Abba baya bada kudin abinci amma har Kun manta...Mama ce ta masge Ihsan tace rufe min baki mahaukata idan mun tara kudin ai da ku za a ci
Aslam ne ya shigo ya zauna tare da gaida Mama,Mama anga me kudi harda cewa surukina ka dawo barka da dawowa suna ta hira ya haura sama sai ga Nusaiba tace anjima Mama zasu tafi Kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login