Showing 15001 words to 18000 words out of 85703 words
ta daina daga Masa hankali ma ba ta ita yake ba yanzu ta kudinsa yake Yi,Ya kalli Siyama da damuwa yace baza ki gane ba Siyama amma Dan kasuwa shi Ina karanta Masa zai Gane,Siyama tace na fahimta ma wlh ubangiji Allah ya mayar maka da mafi Alkhairi Allah yasa ka samu Wanda Suka fi Wanda kayi asara Allah Kuma ya Kare gaba wlh da ace Ina da kudi da na taimaka nima,kallonta yayi yace karki damu na gode
A ranar ya sallami me gadi yace Isa baka min komai ba ga salary dinka na wata biyu ka tafi gida Zan nemeka,Isa yace Sir fatan ba wani laifi nayi ba dan Allah karka kore ni yace ba laifin komai idan na samu yanda nake so Zan kiraka a waya,Isa ba a son ransa ba ya tafi,ya Kira Daya me aikin itama Bara'atu ya sallameta yace nan gaba zai kirata itama tana takaici ta tafi.
Washe gari Siyama ya samu tana girki ya Bata dubu sittin cash yace gashi na wannan watan da watan gaba kije gida domin nan da sati ma'aikatan banki zasu iya zuwa su kore mu daga gidan Nan,Charity tace bazan karbi ko kwandala ba Sir na bar maka ka rike Kuma bazan bar gidan Nan ba sai ranar da Yan bank Suka zo Zan biku naga gidan da kace zaka Kama haya idan naga gidan sai na koma gida Zan dinga zuwa lokaci lokaci Ina dubaku kayi hakuri da kawata kaddara ce da Jarabawar rayuwa ka Zama me tawakali kasa Allah a ranka Inshaallah shi zai taimakeka,Murmushi yayi cikin dacin zuciya yace ba damuwa,Mamansa ya Kira a waya itama da kudinsa take gadara duk da cewa a wajen Yayarta take zaune a turai,Zuciyar Mum dinsa ta kusa bugawa da taji irin bala'in daya tunkaro danta musamman da ya fada Mata halin Nusaiba abinda take Masa,itama Mum hakuri take bashi akan halin Mata tace sai yayi hakuri dole,tana so ta taho Nigeria yace Kar tazo idan tazo ma wahala zata Sha gwara tayi zamanta Kawai ta tayashi da Addua,Mum har kuka tayi danta ya samu karayar arziki taje tana bawa Yar uwarta labari.
Tun daga Sanda Nusaiba ta tabbatar Aslam ya talauce kudinta na accnt da shi take kwasa ta fita yawon shakatawarta ya sallami driver dinsa ma duk da cewar ma'aikatan bank din Basu zo ba tukun a taxi take fita tunda bata iya mota ba,Siyama ce ke Masa girki,yau ma tun safe bai karya ba ya fita akan matsalar data fada masa.
Sai Yamma baici komai ba ya dawo ya iske Siyama tana Shirya Dining sallama yayi ta amsa tare da furta Sannu da zuwa,Nusaiba fa? Ya tambaya tace bacci takeyi Kai ya jinjina ko a jikinta ita, wanka yayi ya canja kaya wani yard hadadde ya fito da takardu zai sake fita Siyama tace dan Allah ka tsaya kaci abinci tukun,wa ya bani lokacin cin abinci ya furta,tace ka dai Yi hakuri ka dauki komai a nutse,Dining din ya karasa ya zauna Yana Kiran Abokinsa Sabeer Wanda tunda matsalar ta faru tare suke shige da ficensu,Jullof rice ta zuba Masa taji Hadi sai dai ba nama tace Naman fridge din ya Kare jiya Nusaiba ta kwashe ta soyesu duka suna dakinta a soye,yace kyaleta ya fara cin abincin yaji ba nama amma yayi mugun dadi yace Wai ke da Nusaiba waye ya girmi wani ne? Dariya Charity tayi tace Santi ne ko me? Yace na Dade Ina so na tambaya sai na manta yau dai na tuna,Na girmeta Mana ai Nusaiba bama sa'a ta bace Kawai dai school ne ya hadamu kasan makaranta ba lallai ace shekarunku Daya ba ni na girmeta da wurin shekaru uku Yayarta ce ni Charity Allah yayota da son girma Yan watanni ta bawa Nusaiba amma sai tayi ta cewa shekaru ta bawa Nusaiba,Nusaiba ce ta fito ita ba alamar Wasa a fuskarta tace to munafuka na hakura da aikinki ki tattara kayanki ki tafi gidan ubanki,sai wani shishigewa mijina kike Yi karuwa,Charity tace Ina zani ba inda Zan tafi Zama daram,gidanki ne Naga nina kawoki ko,to bazan tafi ba cewar Siyama har ya gama cin abinci suna fada ya mike ya fice,Yana barin gidan Nusaiba ta Kira wani mutum tace ya fita kazo ka dauki motar,Wanda ta Kira bai Dade ba yazo ya shiga katuwar motar Aslam me tsada ya fita da motar,Hijab ta saka tabi Wanda ya dauki motar,wurin siyar da motoci Suka karasa aka Yi cikin mota Wanda ya siya yace ki dawo gobe ki karbi kudi tace to ta tsaya a gefen titi zata shiga mota sai ga wani matashi a dankareriyar mota da alama Yana da kudi yace ranki ya dade barka da Yamma,Nusaiba ta kalleshi ta ja tsaki,yace Dan Allah idan baza ki damu ba ki shigo na rage Miki Hanya,Bata kulashi ba sai da ya fito daga motar wani baki ne Dan mummuna da shi yaci gayu Yana kamshi yace dan Allah ki shiga na rage Miki Hanya sai muyi magana,motar ta bude tare da shigewa Gaban motar ta zauna ya shiga shima yace ko na kaiki wurin cin abinci zamu fi sakewa a nan,tace to ya ja mota zuwa wani hadadden Joint Suka zauna yasa aka kawo Mata lafiyayyen abinci shima haka suna ci suna labari,yace tunda na ganki naji Ina sonki Nusaiba,Dan Allah ki so ni ki aureni,Nusaiba tace Ina da aure Amma karka damu auren ya kusa mutuwa,Matashin me Suna Sufyan yace Alhmdllh Allah yasa ya sakeki da wuri muyi aurenmu,Nusaiba tayi Murmushi tana kora lemo har Suka gama hirarsu wurin magriba ya kawota har bakin gate ta fita tana Masa bye bye ta Shige gidanta,tana Shiga Aslam Yana sama Yana kallonta ta saman yace daga Ina kike Ina motata da Kika fita da ita? Kallonsa tayi Kawai ta dauke Kai,da sauri ya sakko cike da bala'i bata taba sanin ya iya Fushi ba sai yau sai da ta tsorata cikin tsawa yace Ina motata,Tace karka dameni mari ya kwada Mata Karo na farko kenan,Siyama ta fito taga abinda ke faruwa yace Ina motata,Nusaiba ta firgita dafe da kumatu ta fada cikin Palo da gudu
Wata wire doguwa Siyama ta Mika masa tace ungo ka zaneta sai ta fito maka da mota karka yarda tunda bata Jin magana,karba yayi ya bita ya zaneta tas yasa key ya kulleta a wani daki yace sai ta fito Masa da mota sannan zai Bude ta,Nusaiba ta fashe da kuka ba shiri ta Kira Mamanta,tana dagawa tace kizo Mama Aslam zai kashe ni wlh ya min dukan tsiya sannan ya kulleni a daki sai na fito Masa da mota,Mama tace karki damu gani nan zuwa gidan duk zafin talauci ne ya dame shi
Aisha zaune take a dakinta da aka gyara Mata cikin gidansu na rufin asiri babansu ya sata a gaba da fada yace yanzu ke abinda Kika Yi kin kyauta haihuwa bata Allah bace, ba fa lallai ki samu miji kamar Farooq ba amma tunda haka kika zaba ga gidan nan kizo kiyi ta zama Allah ya bada sa'a wata haihuwar ma ba gwara babu ba da ita wasu yaran ma in Banda su addabi alumma me suke yi yanzu watakil Baki San Wanda Zaki Haifa ba Allah ya dubaki ya hanaki amma baki gode ba Kawai ke dai ki Haihu ai shike nan ya mike ya fice.
Aisha tana gida Farooq yaje biko yafi sau Nawa Taki yarda har ya gaji ya hakura,Umma ce ke fada na gaji da kwanciyar nan taki Aisha tunda Kika zo bakya hasala komai a gidan nan sai kwanciya baiwarki ce ni da Zan zauna kullum sai dai na dafa na baki kici ko Sanda kina gidan mijinki Haka kike yi,Aisha ta mike zaune cike da Takaici domin kullum aikin gidan nan kusan ita ke Yi amma mamanta ta hanata sakewa ta Saba da gidanta sai abinda taga dama gaba Daya a takure take jinta,tashi tayi tace gaskiya ni na gaji kullum aiki kullum aiki,idan baki ba Kuwa wallahi babu ke ba cin abinci a gidan nan,Aisha ta zauna Kuwa taki tashi ita kuma Ummanta tana Gama abincin ta hanata ranar yini tayi suna fada da Ummanta kowa na Jin haushin kowa,Aisha sai gidan Yan Uwa taje taci abinci ta dawo.
Washe gari ma Aisha ta daura gaba da Ummanta ba Wanda yace wa wani ko kazil suna ta gaba da juna,Umma bata Mata magana itama Aisha haka,Takaici yasa Umma ta Kai karar Aisha wurin Babanta tace Wai ka Haifi yaro a cikinka ya dinga gaba da kai Alhaji ka duba Aisha Wai dani zata Yi gaba,Alhaji yace ba ruwana karki sake kawo min Maganar Aisha ke Kika je Kika zugata ta fito daga gidan mijinta sai ku zauna tare gaki gata nan ai,Umma ta fito tana hawaye tace dama nasan baza ka Mata fada ba tunda ba kaunata kake ba Watarana Naga Alama Aisha dukana zata Fara Yi a gidan Nan,Aisha tana ji ko magana haka tayi mirsisi da ita ta Danna headphone a kunnenta tana Jin Waka tana bi da bakinta baza ma taji fadan ba bare ma ta sakko,kwafa Umma ta ja ta koma ta Fara wanke wankenta Aisha baza tayi ba.
Affan tubewa yayi ya Shiga wanka ya fito daure da guntun Towel,Raudat tana bedroom itama ta window tana hango shi Yana shiryawa Yana ta faman shafe shafe da feshe feshen jikinsa da turaruka Yana ta kalailaita har yafi mace,tunda yazo taje sumarsa yafi minti talatin Yana Abu Daya akan Suma,Raudat baki ta tabe ta saka doguwar rigar baccinta me Dan kauri ta kwanta tare da shigewa bargo duk bata da sukuni sabo da Affan zai kalleta komai sai ta faki idonsa take yi,Yana kallonta duk abinda takeyi kayan baccin ma a toilet ta shirya,Dan gajeren wando ya saka sannan ya zauna a bakin bed Yana Shan ruwa,windown ta ya bude glass yace iska Wai zai Sha,Raudat ta mike ta zuge,ya sake tashi ya bude,ta fito daga bargo ta zuge kafin ta koma ya Mika hannu ta cikin window ya jawo rigarta ta manne a jikin bango rankwashinta yayi ta saki Kara yace karki dawo nan na fada Miki idan ba haka ba Zan dawo cikin bedroom dinki,Raudat da taurin Kai tace wlh baka Isa ka hanani sukuni ba ta maida Hannu zata kulle window ya taka windown ya dane ya shigo cikin bedroom dinta ta window daga shi sai gajeren wando,ihu ta saki kwarto Jama'a kwarto,yace yau sai munyi musayan bed ki kwana a nawa yau a naki Zan kwana tace Allah kiyaye ka shafa min kazantarka a gadona,takawa yayi da Niyyar Daukanta tayi sauri ta taka window tare da dirgawa cikin bedroom dinsa tana ihu,Windown ya kulle yaje ya fada saman gadonta ya kwanta,tace Allah ya Isa mugu azzalumi taci gaba da tsaiwa tana kallon dakinsa ya Sha furniture komai me tsada da kyau ko Ina kamshi yake a ciki Kal Kal Tsaki ta ja ta shiga kitchen dinsa kamar na Amarya komai akwai Raudat tace lallai ya shiryawa karya mutumin nan ta duba sosai tana Bude flask taga soyayyar kaza ta hau kaza da ci taci da yawa sai da ta kusa cinyewa sannan ta duba fridge taga wani katon juice an tsiyayi rabi a ciki ta dauka taci gaba da Shan abinta ya leka ta window Yana kallonta bata sani ba kwayar maye ya saka Mata a ciki yasan kwadayinta sai ya kaita ta Sha,Nan da nan Raudat ta Zama wata Yar kwaya ta kasa bacci taji wani karfi ai sai ta hau gyaran gidan ko Ina sai ta share ta goge ko ba dirty Bata Yi bacci ba Yana dakinta Yana sheka bacci akan gadonta ita Kuwa tana ta gyara Masa gida lungu da Sako har kasan bed sai data janye ta share ta goge ta gyara komai ta fada toilet ta wanke ta goge ko Ina ta dawo aiki bai isheta ba ta fito da kayan fridge ta wanke komai ta goge ta maida kayan neat ta dawo ta rasa me zata Yi ma ta bude kofa tsakar dare ta fita ta Fara sharan uban compound da parking space kowa na bacci tana ta fama kafin gari ya waye ta share compound din me dauke da Interlock ya dawo tsaf,flowers din dake compound har su ta share kasansu kafin gari ya waye taji jiki bata sani ba sai data gama ta fada dakinsa inda ta fito lokacin Sallar asuba yayi lokacin kwayar ta Fara sakinta ta window ta sake haurawa zuwa dakinta ta fada Saman bed bata san da mutum ba ta manta jikinta ya mutu Affan Yana bacci yaji jiki me laushi ya fado Kansa
Tashi yayi da sauri yaga itace tana shigewa jikinsa da sauri ya dirga kasa daga bed din har zai kwanta a kasa ya tuna shi fa guy ne baya kazanta Tsaki ya ja yabi ta window ya koma dakinsa yace aikin banza warin balaga takeyi ma Yana karkade jikinsa harda shinshina inda ta fado Masa a jiki yace kaji ko warinta ya manne min a jiki irin wannan warin sai na balaga yanzu ma ta Fara balaga na rainata ma banza ta gyara min daki kwadayayya ta cinye min kazata ya furta tare da fadawa saman bed dinsa ya kwanta Kiran Sallah yaji an kwala yace ta cuceni ban karasa baccina ba ya tashi ya daura Alwala ya wuce masallaci yana doro da carbi a hannunsa Kalar jallabiyarsa kullum ko masallaci zai je carbinsa ma toomatch yake da carbi da kayansa carbinsa sunfi kala hamsim ko wanne Kaya da Kalar carbinsa ana taku dai dai ya shiga masallacin unguwar, Liman ya sanshi Yana shigowa zaka ji kamshinsa Yana bawa liman dariya sai dai Yana birge mutane duk gayunsa Sallah a jam'i kullum ba fashi ko wacce Sallah har sun Saba da liman da duk wani me zuwa masallacin.
Sai da aka idar da Sallah Affan ya daga hannu sama Yana Addua Allah ka azurtani,Allah ka bani kudi....kudi ya Allah na halak...Liman yace samari barka da asuba Affan yace Morning liman how are you? Dariya liman yayi yace Alhmdllh, Affan ya mike tsaye yace lafiya dai liman muyi Maganar a tsaye sabo da rigata zata yamutse ka ganta ta Sha guga bana so ta yamutse na tafi hanya a haka,liman ya zaro Ido yace asuba ce fa yaro da sauran duhu wa zai ganka,Sabo da jin dadin kaina ai ni Zan kalli kaina cewar Affan,Liman ya jinjina kai Yace baka da aure ne? Affan yace wuuu Ni aure rufa min asiri da yanzu Ina nan hankali a tashe Ni da cikakken bacci munyi hannun riga,Liman Murmushi yayi yace kaga Kuma da zaka Yi auren sai kafi haka nutsuwa,Affan yace to nifa gaskiya bana son aure yanzu mace ta dameni da kudin cefane kaina ma da kyar nake rikewa,Liman yayi dariya yace baka da budurwa saurayi kamarka kyakyawa da Kai haka kowa ya ganka yaga Namiji irin Kalar da Mata ke yayi,Affan ya shafa sajensa yace ba ruwana haka Kawai soyayya yanzu sai da kudi inje in tari budurwa bani da abin bata ta ci min mutunci,Liman me kudi ne na gaske yace kaje ka kula ko wace Indai da aure kake sonta Ni Kuma ko nawa zaka Bata Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har muga abinda Allah zaiyi, Affan yace to yaji samun kudi yace dama Ina da budurwa Ina sonta fada mukayi akan kudin anko tana so na za ayi biki na kasa siya Mata anko kunya tasa da kaina na fece,Liman yace tayi aure ko bata Yi ba? Bata Yi aure ba jirana takeyi Kawai Liman yace ka koma ka Bata hakuri ku daidaita Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har a tsaida Maganar aure ya kamata ace kana da aure bai dace mutum me addini irinka ba ka zauna haka Kuma muna limamai mu zuba muku Ido bayan Allah ya hore Mana yanda zamu tallafeku, Affan yayi godiya ya fice Yana murna a ransa wurin samun kudi ya samu shi Kam Yana cewa Allah na gode ma ka amsa Addua ta sai ta fada Kan liman.
Kwanan Nusaiba biyu a daki a kulle Aslam ya kulleta yace sai ta fito Masa da motarsa abinci ma Dan kadan yake Dan zubawa ya Mika mata,tana ta kuka ta dinga Kiran Mama a waya,ba shiri Mama ta sauka a kofar gidan Charity tana bakin kofar da aka kulle Nusaiba tace ki fito Masa da motarsa a zauna lafiya,Nusaiba tace sai naci uwarki shegiya munafuka,Aslam Yana gidan yaji ana bubbuga gate yaje ya bude yaga mama ce ta shigo tana karewa gidan kallo tace Ina kudinka? Ina motocinka makaryacin banza dama karya kaje kake Mana ka jefa yata a masifar talauci,Aslam yace kije ki fadawa yarki ta fito min da motata,Mama ta kalle shi tace butulu wato babu mutunci ba girmamawa Aslam bai kulata ba suka shiga ciki yasa key ya Bude dakin Daya kulle Nusaiba Yana tsaye ya tare Hanya Mama ta shiga tana shiga ya maida kofa ya datse ya kulle su tare a dakin yace ku fito min da motata na fada muku,Mama ta zaro ido tace dama haka yake baida mutunci,Nusaiba tana hawaye tace wlh Mama zai kashe mu Yana da bindiga,Mama tace kwantar da hankalinki yanzu Ina motar? tace na siyar da ita ko kudin ma ban karba ba ya kulle ni,a jikin kofar Mama ta tsaya tace dan Allah surukina ka Bude mu sai muje a karbo maka motarka,Aslam ya kalli Charity dake sanye da Riga da skert na Atamfa wasu kodaddu yace wlh mutanen nan sun maidani wani banza,tunaninsu Banda hankali, charity tace yo ai Basu san da hankalinka bane basu san Kai cikakken Namiji bane sai yanzu,Aslam yace dan Allah? Charity tace Allah,yanzu ni cikakken Namiji ne? Ae sosai yanzu na tabbatar Amma da ka zauna Kamar solobuyo,Murmushi Aslam yayi yace Ni kaina sai najini wani na sake girma yanzu, Charity tace ah ai sai yanzu ni