Showing 3001 words to 6000 words out of 85703 words

Chapter 2 - Auren Mu Book 1 Hausa Novel Complete

25 Jan 2025

597

so a lalata masa ita Shuru yayi yace kina da gaskiya,Mama tace kinyi dai dai ya zaci irin yaran nan ne yan talla lalatattu amma laifin mahaifinku ne da ya dauki nauyinku ai da haka bata faru ba

Itama Nusaiba Koko ta zuba tasha Amma ubansu a gabansu yake Shan shayi me kauri Kuma uwarsu zai sa ta dafa shayin ya siyo Madara da komai ya hada abinsa da kauri ya Sha a gabansu suna kallo yaran kanana Nusaiba ce Kawai Babba,Babar Shehu ce tazo daga kauye da Leda katuwa ta mikawa Mama tace gashi kanzo ne da nake shanyawa na taho muku da shi kwa rage zafi,ta Mika Mata Sabulun wanki da Omo da yawa sai masara kwano uku da gero kwano biyu,ga wake kwano daya,barkono har da kuli tace nasan halin Shehu ga wannan kwa rage zafi ba yawa,Mama tana ta godiya,su Nusaiba sai Murna sukeyi Watarana sai su kwana Basu ci komai ba lokacin Nusaiba ta ebi Kanzon ta musu dafadukansa suka ci Suka koshi shi kuwa Shehu dama a waje yake cin lafiyayyen abinci yaransa da matarsa ko oho.








AsmaBaffa
[4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️


6-10


Official

By
AsmaBaffa




page naku ne






Zuwa dare dukkan matan a daki daya suke kwana da iyayensu sabo da rarashin zuciya irin ta Shehu, dukkan yaran basu bacci ba sabo da Babu abincin da zasu ci Shehu suna saman gado shi da Mama su Kuma su Nusaiba suna kasa a kwance saman tabarma, mazan Kuwa suna kitchen a gefe daya suke kwana gefe daya Kuma kwanika da tukwanen abinci, washe gari da rana babu abinda su Nusaiba zasu dafa har ta lallaba kannenta suka tafi Islamiyya wacce dama ita kadai suke zuwa gwara ma kannen Yan primary suna zuwa ta gomnati ita kuwa rabonta da makarantar boko tun mda ta Gama primary,Bayan sun dawo babu abincin da zata ci Ameer Wanda ke binta yace wlh Aunty Nusaiba yunwa muke ji Babu komai da dare,Mama tana jinsu suna zancen ta kalli yaran nata cike da tausayawa tace bani da komai a gidan Nan sai masara sai dari da hamsim,kanwarsu me bin Ameer wato Ihsan tace mu Kai Nika Mana Aunty sai ki Mana tuwo ko ba Dadi sai muci haka tunda mama wake da geron sana'arta take gyarawa

Mama tace wannan shawarar tayi ta zaro dari da hamsim tare da mikawa Yasmin ta karba ta siyo waken Miya na hamsim,manjan hamsin sai Maggi dama da daddawa sai wani ragowar tattasai guda uku suka Yi miyar kuka tuwon masara,Suna cin tuwon Mama tana furta Allah ya baki miji me kudi Nusaiba wanda zai kaini paris,Nusaiba tace gwara da kika ce Paris irin su Dubai inda tourist ke cika gari,me za ayi da London Mama baki ta tabe tace tsoron ai London bata Yi ba kasar leburori ce Kuma ko kin samu me kudi karki sake ki taimakawa Shehu ya Gama zaluntar mu,dama wa zai bawa Abba ko sisi cewar ameer suna ta labarinsu,Ihsan tace Ina ruwan Abba Kuma ma ai uba ubane ko me yayi ai taimako Zakayi sai Allah ya buda miki,Nusaiba tace hmm tunda muka taso cikin kuntatawar Abba muke,to ba sai muyi hakuri ba cewar Ihsan,duk abinda ya faru akwai dalili shi yasa idan Kika ji Mata ko Yaya suna abu wasu dole akwai dalili, Siyama ce ta shigo tare da kwada sallama,Nusaiba tace shegiya Charity ce,Ziyama wacce aka fi sani da Charity tafawa sukayi da Nasaiba, Nusaiba ta Fara tsokanarta Charity,itama Siyama tace begin at home, Charity we dey begin at home,Dariya sukayi,Siyama ta kalli Nusaiba tare da furta Wai kayan nan basa isarku ne kullum Hijab da su Atamfa,Nusaiba tace kalleki wa zai kalleki yace Yar musulma ce Kuma bahaushiya kin wani saka Riga da wando ga pcap Kuma wasu tsofaffin da ace ma sababbi ne da sauki,Charity ta kalli kanta tare da furta baza ki gane bs Nusaiba,ya yau me kuka dafa? Mu fa gidanmu yau ko gafzar ma Babu ga jarin Ummi ya karye,Nusaba ta kalli babbar kawarta Charity tace muma yau zero sai kokon safe,Miko min kokon na samu na rage,Mama ce ta zubowa Charity koko ta banka tana cika cikinta tace shike nan sai tsula fitsari Sallama tayiwa Nusaiba tace gidan kanwar Ummi Zan biya duk da bata taimako dole na Kai Mata ziyara ko banza na cika tumbi na...

Nusaiba tace ah tsayani mu tafi yau ko bata Nan sai mun leka makwafta mun cika cikinmu,tafawa sukayi Charity tace Kuma gashi 1:30 ko waye yanzu sun sauke abinci suka fita Wanda kawai cewa suka Yi Mama zasu je karbo bashin da suke bi...

Suna fita a kafa suka dinga tafiya har zuwa GRA dake cikin Kano,Ba kowa a layin sai manyan motoci dake shige da fice a unguwar suka shiga gidan kanwar maman su Charity suna zuwa me gadi yace sun tafi Umrah,Nusaiba ta kalli Charity suka ce bad luck, Charity tace Kinga mu shiga gidan ko uban waye a haka har mu samu abincin ci inda za a sauke mu da abinci...

Fitowa sukayi suka samu wani katafaren gida hadadden gida na gaske Suka kwankwasa,Me gadi ya leko yace Kai Yan uwan Alhaji ne daga Kauye? da Sauri Charity tace ae,megadi ya Bude musu kofa suka shiga ciki,motocine hadaddu gasu nan anyi parking nasu iri iri,suna ta kallo suna faman zare Ido har suka hadu da wata me aiki tace bayin Allah lafiya? Nusaiba tace wajen masu gidan Muka Zo kice Yan uwansu ne daga Kauye,Me aiki tace to tare da Shiga ciki ta Kira Wayar bedroom din Ogan nata tace Sir kayi baki Yan uwanka ne daga Kauye,Tsaki yaja tare da furta maybe yan uwan Mum ne nasan itace me alaka dasu,yanzu Mum ta koma Turkey nayi nayi ta dawo taki and now tana jajibo min yan kauyensu,anyway ki kawo su palona a Basu abinci da komai bazan iya ganinsu yau ba sai gobe sannan ki fadawa gageman Kar ya Bude musu kofa su fita sabo da zasu iya bacewa a city su jawo min matsala kamar yanda last year wasu Dangin Mum na kauye suka jawo min,Kar a barsu su fita sannan na gaji ki fadawa megadi Kar ya sake barin kowa ya shigo daga yanzu,cikin Sauri me aiki ta amsa da an gama Sir ta fice.

Yanda Oga yace haka me aiki ta isar da sako sannan ta dawo ta shuryawa su Charity abinci ya sha nama ko Ina ga lemuka da ruwa me sanyi,Nusaiba da Charity sai Murna sukeyi, Charity tace gaskiya masu gidan nan sun iya karrama baki ji girki dan Allah muci mu koshi mu ware gida,Loma Daya Charity tayi ta kalli Nusaiba tace gyara min pcap dita ta kalli gabas girkin ya hadu, Nusaiba ma tana ci tace wayyoo dadi lallai da ace Hamisu zai dinga bani irin wannan to Zan iya aurensa, Charity ta kyalkyale da dariya tace ni Kinga akan girkin nan Ban ki na bawa Basiru kirjina sau goma ya taba ba Suka kyalkyale da dariya gaba Daya sun cika gidan da hayaniya kamar gidansu, sai da suka koshi harda hutawa suna Shan ac karshe Suka fito zasu tafi Megadi ya Hana yace Oga yace ba shiga ba fita

Tunda Farooq yayi Sallar asuba bacci yaka kasancewar Yau Sunday ba aiki har 11am Aisha ta shigo bedroom Duke da tire ta zuba gayu kyau Kam ta zuba shi,shayi ne da yamballs sai bread ta Fara tashin Farooq Honey... Honey wake up ya kamata ka karya,Farooq ya farka cike da mamaki domin yasan halin Aisha bata Masa soyayya sai da dalili dukkansu babu na zaba a cikinsu,Aisha tace tashi ka karya Baby ba sai kaje Dining kayi wahala ba,Mamaki ya Kama Farooq sai ya tuna da wani abu yace Kinga ma Ina so na fada Miki kudin jiya da dubu dari Uku Wanda na bayar bashi nace da abokin nawa na fasa karba ma ya barsu sabo da irin mutuncin da muke bai kamata na karba ba Yana magana ya dauki Bread zai Fara ci kenan Aisha cikin bala'i da masifa tafisge Bread din tare da dauke tire din tace dalla bani ance Kai kadai ya kamata ka karya a saman gado ni wato na mutu bana so na karya ne a Kan gadon tsaki ta ja ta fice tana cewa wani ya bar Masa kudin wato ni bazan ci kwandala ba lusari,baki bude ta bar Farooq Yana mamaki duk da yasan halin Aisha....

Bayan satikai Farooq yayi parking Yar motarsa gidansa na me rufin asiri,Aisha ya iske a Palo tana kallo sanye cikin Riga da wando masu kyau yace fito muje kiga abin mamaki,Aisha ta kalli Farooq yasha shadda tace karka bata min lokaci fa muje na gani,tana Fitowa taga wata sabuwar mota me kyau ba laifi,key ya Mika Mata yace surprise taki ce,Ai Aisha haukacewa tayi tana ihu da tsalle ta rungumeshi tana zuba godiya,Yace maza Zo muyi hoto so nake muyi maganin makiya a layin nan,dama bashi na karbo ta na wata biyu idan muka bawa makiya mamaki a layin nan sai na maida musu abarsu mota ce me tsada ta milliyan biyu shi yasa na karbo Miki aronta zuwa Yan watanni ya Kika ce dole makiya su Sha mamaki,Takaici ya Kama Aisha sai data Gama muryarta ashe ta aro ce kudi ya bayar ya karbo aronta na wata biyu,ranta ya baci haka ta tsaya Suka din pics a jikin motar aro suka dinga posting a WhatsApp da Facebook etc, mutanensu masu bibiyarsu ana ta congrats sun faso gari

Affan kayansa ya fito da su Yana wanki a jikin pampom katon Compound dinsu kaya akw uku amma tunda safe yake faman aikin wanke su sabo da du fito kal Kal,har Raudat taje aiki ta dawo Affan Yana wanke kayan Nan,har itama ta fito da nata tazo inda yake ta fara wanke nata bata San ta hado bra ba a ciki Affan ne ya tambayeta yace duk wannan karyar da kike da 36 kike sawa? Dama ba komai a kirjin? Kina nufin a haka Kika Yi Kasuwa harda samun Sugar Daddy har ya iya siya Miki mota,Tsaki Raudat ta ja tace idan bashi kake so a baka kayi magana har bashi muna bawa talakawa irin ku,me kake so a ciki ka taba sai a baka bashi,Affa yaji kunya Sabo da bai taba kula mace ba ko da wasa yace ba ruwana Ni ba Dan Iska bane






Kiyu hakuri yau bana Jin Dadi







AsmaBaffa
[4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️

16-20


Official

By
AsmaBaffa



Page naki ne
NAJIDA ALIYU BICCA








Bayan sun gama wanka suka yi Nusaiba kwanciya tayi sabo da gajiya Charity ce ta fito Palo ta iske Oga Aslam ya fito sanye cikin Jallabiya Yana hutawa gaida shi tayi Yana zamansa na takama ya kalleta kadan yace kin iya girki?zabura Charity tayi ta nuna kanta tace girki Ni? Ah kasan Kuwa yanda na iya girki? bari kaji Oga sanda Ina cikin mahaifar babata ka gane lokacin da Ina cikin Mahaifa da na samu damar Fitowa Zan shigo wannan duniyar lokacin Babata tana tuka tuwo na taho Zan fado duniya Saura kadan na fada cikin tukunyar tuwo Allah ya kiyaye ta tare ni ban fada ba kaga Kuwa wanne kalar abinci ne bazan iya ba,Allah ya min basira farko ma fa da tuni Yar kwallon kafa ce Ni,lokacin da Kanu yayi tashen cin ball ba shi ya kamata yaci wannan ball din ba lokacin Atalanta cup nice ya kamata,ana wani zancen Ronaldo wani Messi dan ba a Sanni bane na iya ball amma makiya sun hana naci gaba,Ina da makiya da yawa shi yasa,Aslam Yana ta dariya a ransa,yace to me Kika iya dafawa a ciki? Na iya Alala,tuwo,danwake ga sarkin Dadi shinkafa da Miya duk na iya,Yace hmm duk ni bana cinsu me yasa kike sa kananan Kaya kina Yar musulma bahaushiya?

Sabo da na nuna musu Ni ba sa'ar Mata bace mace ce ni me kamar maza kwari ne Babu,Ni Yar jam'iyar what man can do Woman can do better ce,to Kuma kina da saurayi? Charity tsaiwarta ta gyara ta Fara zuba Murmushi tace haba Ina da shi har da Ridwan a cikinsu yaudararsu Kawai nakeyi Ina cin kudinsu,Rannan Ridwan din ma yazo daga karbar kudin ankonsa shike nan ya rungumeni zo kaga kiss hmm kamar maye ni kuwa na ci masa mutunci nace babarsa me tsatsar hakora,Aslam dai Jin labari Kawai yake ratata tun a nan yace Charity bata kirki bace, Nusaiba ce ta fito ta dakawa Charity tsawa tace Charity kiji tsoron Allah Ridwan din baki taba sauraronsa ba yaushe ma a masifarki Zaki Bari ya Miki kiss Naga rannan Abdulhadi daga yace ki rungume shi Kika fasa Masa Kai da dutse, Enough kuje kuyi girki cewar Aslam,komai na Kitchen din kasa amfani sukayi da shi sai siyo musu abinci yayi,washe Gari suka dinga kuka tafiya zasu Yi yace to ba damuwa yasa Driver yace ya kaisu Tasha Kuma ya tabbatar sun Shiga mota,ya mikawa driver kudin motarsu sannan ya Basu dubu ashirin ashirin kowacce,da sauri Nusaiba suka Shiga motar,suna tafiya aka zo saitin layinsu Nusaiba tace nan zamu sauka,a sauke mu a nan,driver yace ai oga yace dolene a saku a motar Taraba Kar a samu matsala su Charity suna ji suna gani aka wuce layinsu har zuwa tasha aka sasu a mota tare da biyan kudin,sai da suka tabbatar driver ya tafi suka fito daga mota suka ce sunyi mantuwa ko tsayawa karbar kudin motar Basu Yi ba Suka Shiga Napep zuwa wani gidan amarya kawarsu ce Suka bata ajiyar kudinsu sannan Suka tafi layinsu

Kafin su karasa gida lungun da ba mutane suka tsaya Suka sallami me Napep suka shafawa jikinsu toka har gashinsu hular Charity ta cire ta wullata cikin wani gida itama Nusaiba ta jefa dankwalinta gashi sun samo toka wajen masu girki a tasha sun shafe jikinsu tare da shafa bakin gawayi a hannayensu da kafafun su cikin katuwar bolar dake layinsu suka Shiga tare da tsugunawa a ciki kamar birarrika,kowa ya wuce ana cewa Allah sarki ga wasu can mahaukata kalli Yan Mata dasu Allah ya Basu lafiya,ana ta musu addua har Yamma likis sai ga Ameer kanin Nusaiba zai wuce suka ki magana har ya wuce sai da ya wuce Charity a hankali ta daga hannu Ameer gamu nan karya muke,Nusaiba ce ta bige Mata baki suka Yi Shuru,har Yan unguwa suka gaji aka nemo Yan sanda da me unguwar layin aka je inda su Charity suke dukun dukun suna soshe soshen karya,me unguwa yace a fara bincike ko a Nan akwai Wanda ya sansu,Shehu yazo wajen Yaga yarsa Nusaiba da kawarta Siyama,Shehu yace Wannan ai Yata ce data bace da kawarta Yar gidan Dauda,mutane aka dauki Salati

Shehu yace Wanda Suka sace su ko me ya faru oho Nusaiba da Charity sunki magana ba uhmm Babu Uhmmm Uhmm Dan Kar ma a musu fada a gida,Yan Sanda Suka ce sai dai Wanda Suka sace su ne Suka musu tsafin da baza suyi magana da wuri ba,Shehu yace tunda Sun fito Alhmdllh kaga aikin Addua ko sun sace su amma Addua tayi tasiri sun kasa yanka su ko tsafi da su Addua kenan ai ba karamin kudi na kashe ba Sadaka masallatai Masallatai cewar Shehu yaja Hannun Nusaiba suka tafi gida Charity ta faki idon Shehu ta radawa Nusaiba Kar muyi magana sai gobe,Mama harda ihu sabo da murnar ganin yarta karshe ta fashe da kukan farinciki tana oh ashe Zan sake ganinki Nusaibata,Shehu yace basa magana yanzu amma kafin mutane su Fara shigowa suyi wanka Bari naje na Kira Dauda ya fita cikin Sauri,Su Ihsan Suka dinga ihu suna fada a unguwar anga su Nusaiba a bola aka tsince su.

Mama ruwan wanka ta hadawa ko wacce Suka shiga kowacce ta wanke toka da bakin gawayin da Suka shafawa kansu sai gasu fes ba alamar wahala a jikinsu duk sunyi wani kiba ma fatarsu ta murje amma sunki magana juyin duniya sunki magana a Haka Shehu ya siyo musu shinkafa da wake da Miya Wai sun Sha wahala hannun Yan mafiya bari a basu me dadi,suna Fara ci Anty tazo tare da Dauda Suka zauna a tsakar gida Nusaiba da Charity suna ciki suna cin abinci,ganin ba kowa kasa kasa Charity tace ba dadi abincin na Saba dana gidan Oga,Nusaiba tace ji kazar da aka sa Mana jiya a cikin shinkafa,Charity tace habawa ai sai lemon shekaran jiya ga sanyi ga dadi yanzu shike nan mun dawo cin gafza Kuma ga wanka da ruwan botiki can a shower Muka saba,ta kalli gidan su Nusaiba tace Kai Kan uba kalli gidanku dama haka yake duk dirty painti ma ba a Gane wanne kala ne,dariya sukayi yanda baza aji ba Nusaiba tace Nima sai yanzu na kula gashi mun dawo kwanciyar Kai da kafa gobe da sassafe sai tallan kosai,Charity tace idan Muna so mu huta da talla gobe zuwa jibi Kar mu sake muyi magana hauka muke cewar Nusaiba Suka sake Yin Shuru abinsu.

Juyin duniya sunki magana haka bayan sunci abinci Dauda da Aunty Suka tafi gida da Charity,washe gari ma basuyi magana ba a Rana ta uku Charity sai ta Fara magana tace Aunty daga nan bata sake magana ba,Aunty tace Dauda yarka ta Fara magana Alhmdllh wlh yanzu tace Aunty ta Kira sunana,Dauda yazo kusa da Charity yace Siyama me Kika ce kinyi magana dazu Nima Kira sunana ba sai kince Baba ba ko Dauda Kika Kira ba matsala ai duk cikin lalura ne, Charity a ranta tace dama haka nake so wlh sai na more sunanka tace Dauda,Dauda ya kyalkyale da dariya Alhmdllh Nima ta Fadi sunana asiri ya fara sakinta, Charity ta sake cewa Dauda Iliyasu,Dauda ya sake shekewa da dariya yace haka ake kirana da a makaranta, Charity Kuwa a ranta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login