Showing 27001 words to 30000 words out of 74955 words

Chapter 10 - Inda Rai Book 1 Complete Hausa Novel

By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[1/8, 5:26 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*INDA RAI*

*BOOK ONE PAGE 7*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Littafin INDA RAI na kiɗine yanzu free pages ne mukeyi ki biya ki karanta cikin aminci da salama. 1k ne kacal 0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number zaki turo min shaidar biyanki 09097853276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne zaku biya jaka ɗaya ne kacal zaku tura +22790899076 Ta wurin Mommy*

Yau tallana na nakune Mutanen Ƙasar Niger. More especially, ƴan Niamey ko masu dangi anan ko ƙawa ko abokin, da in na tura muku kaya can zaki samu mai amsa Miki shi yasa Miki shi a motar garinku, inma kuma ace duk ma baki da mai amsa Miki, Driver da zai taho da kayanki daga Sokoton Nigeria, zuwa Niamey Niger zai sa Miki shi a motar state da kike. Akwai kuma Garabasa ta musamman wacce takuce, step ɗin kayana akwai manya set akwai kuma ƙanana, domin banafa barin Customer tazo da kuɗinta su koma, ga farashin su biyo kiji. Manyan set ɗin daga haka arba'in, jaka hamsin, jaka settin, jaka saba'in, jaka tamanin, sune manya a yanzu saboda kuɗinki sun yi sama sunfi naira, Amman in naira ta kuma hawa ta fi nakun zai zama manyan set ɗin daga jaka 50, 60, 70, 80, 90, 100, ƙananan set ɗin kuma yanzu daga jaka talatin ne, haka ashirin da biyar, jaka ashirin, jaka sha biyar, jaka goma, sai kaja takwas banayin haɗin ƙasa da jaka takwas, sai kwanon Ƙasaitacciyar mace shi jaka biyar ne. A yanzufa kenan, in kuma Naira tayi kunnen doki da kuɗinki to ƙanan set ɗin Daga jaka 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k sai kwanon Ƙasaitacciyar mace 7k idan kin sayi kayana ni free Delivery ne Adamawa to Sokoto ke kuma sai kiji da sauran.

Fara samun tangarda, sai kuma tayi shiru tana sauraron tausasan kalamansa.
“Duk mijin da kikaga, ya nemi aurenki daga bisani ya janye, toh dama can Allah bai hukunta zamowarsa mijinkiba, ke muminace, kuma saliha, tsarkakekkeya dan haka, ki kwantar da hankalinki, inada kekkyawan yaƙinin Ubangijin talikai da kika tsare mutuncin kakin domin sa, baki saɓamasa, yayi Miki tanadi da miji mumini, salihi mai sonki, tamkar ransa, mai ji da gamsuwa cewa in babu ke cikin rayuwarsa bazata yi armashi ba, yana nan tafe gareki zai kuma iso a duk lokacin da Ubangiji ya ƙaddarta faruwar hakan, so please kada kiyi kuka ki zubda min raunatattun hawayen akan Dr Nafi'u, ki adanasu domin Taj ɗinki baya son zubarsu, kiji ko Ishmah Boɗdin Dadeey”.
Sassayan numfashi mai cike da korar damuwar dake ranta ta fesar kana a hankali tace.
“Taj yau kwana uku fa, kenan Dr Nafi'u baya kirana sai in ni na kiranshi, yace min muje muyi gwajin Genotype naje munyi kuma yaƙi ya gaya min Result ɗin, sannan yazo ya daina kirana, ya zanyi in banyi kuka ba kuma ni dai nasan bani da matsalar komai. Dadeey nama kanta abin ya bata tsoro ɗazu sai cemin tayi Allah yasa tana da rabon ganin na sakeyin aure”.
A hankali ya ɗan kalli far-fajiyar gidan nasu lokacin da Abu Hashim yayi parking.
Cikin sanyi ya rumtse idanunsa da ƙarfi domin ji yake zuciyarsa na hankaɗo abinda ke cikinta tsawon shekaru yana tahowa kan harshensa.
Saboda jin abinda Ishmah ke faɗi.
“Taj 7 yaers fa kenan yanzu har za'a shiga na 8 Taj banyi aureba, Abba na kanshi abin na damunsa Taj”.
Ta ƙira sunansa cikin raunatacciyar murya da alamun zubda hawayen wanda hakan ya sashi ƙara jingina da car seat ɗin tare da cewa.
“Na'am Ishmah, menene? Gaya min?”.
Murya a sanyaye tace.
“Taj ina son inyi sure ko dan farin ciki Dadeey da Abba na, inason inyi aure ko dan samun nitsuwar zuƙatansu”.
A tausashe yace.
“Zakiyi aure Ishmah zakiyi auren da zasuji daɗinsa, kinji ki daina kuka, yanzu muje kirakani in sallami Yah Abana da Ummey ko, zan wuce Airport ƙarfe goma zantashi”.
Tana mai share hawayenta tace.
“Toh”. Ba tare da ya katse kiranba yasa wayar a aljihun ƙirjin jallabiyarsa kana ya fito.

Zaune ya samu Ummeynshi da Yah Abana a pravet Parlour inshi kasan cewar yau Ummeeyshi ce da girki.

Tea Ummey ta haɗa mishi tare da miƙa mishi.
Amsar mug ɗin yayi tare da ɗan ƙara matsota kusa da Malam, ɗin kana ya ɗan gyara zamansa ya tankwashe sawunsa, yana mai fuskantar su, murya cike da girmamawa yace.
“Yah Abana”.
Murmushin Ummey tayi tare da zuba musu ido, Allah ya sani Taj shine farin cikinta mijinta kuma shine duniyar ta, bata jin zata iya rayuwa ba ɗayansu a rayuwarta ta kuma samu farin ciki, ita kanta tasan biyayyar Taj da Alkunyarsa da haƙurinsa ne ke ƙara zuzuta soyayyarsa a zuciyar mahaifin nasa da har yake gaza iya ɓoyewa.
Lumshe idanunta tayi ganin shima malam ya ɗan gyara zamansa tare da ɗan ronƙofowa ya matso da kansa kusa da fuskar Taj ɗin kana yace.
“Na'am Abbana ya akayi?”

Murmushin Ishmah tayi tana mai jinjina son dake tsakanin uba da ɗansa, sai kuma ta kuma sakin murmushi mai sauti jin Muryar Ummeeyshi na cewa.
“Malam irin wannan kasa da murya da keɓe kunne, duk nice ake ɓoye abin da ake son tattaunawar”.
Lunshe ido Taj yayi tare da ɗan manna kanshi da guiwowinta kana yace.
“Ummeey na me zamu ɓoye Miki, kecefa muhalit sha'eyd na ko wacce mgnar da zamuyi”.
Sai kuma ya kalli Malam ɗin dake shafa kansa.
Hannunsa na dama ya ɗaura kan hannun mahaifin nasa yana mai asawa da Amin jin addu'o'in da yake jero masa.
Dai-dai lokacin kuma zaratan ƴaƴansa suka shigo Parlour a jere domin zuwa yi mishi sallamar zasu tafi wuraren aikinsa.

Kusan a jere suka shigo, cike da son zaratan yaran nasa wanda tuni wasu irin Yah Hafiz Yah Sulaiman, Yah Yusuf, Yah Abduraham, duk sun zauna a gabanshi irin zaman nan na neman albarkar iyaye,
Cikin kulawa Ummeey ta kalli Yah Aryan da Kabir dake tsaye tace.
“Bismillah Aryan Autan Kabir ku zauna mana”.
Wani irin kisataccen kallo Aryan ya jefa wa Taj tare da kwaɓe fuska kana yace.
“Uhmmm ai ga auta kam ana sa mishi al'barka na musamman”.
Ya ƙarashe mgnar yana ɗan tauna lip inshi na ƙasa saboda azabtar suya da zuciyarsa keyi.
Kabir kuwa sunkuyowa yayi ya zauna jin Malam ya jawo hannunsa ya jawosa zaune, ganin haka ne yasa Aryan ɗin ma zama.
Ummeey kuwa kasake tayi tana, nazartar kalaman Aryan tana haɗesu da irin kallon da yake bin Taj dashi tana ƙara haɗesu a mizani ɗaya da kalaman Mom Amal a lokuta da dama.
Shi kuwa Taj hannu ya rinƙa bawa yayun nasa tare da gaidasu.
Cike da so suke amsawa, daga ƙarshe ya miƙawa Aryan hannun kauda kansa yayi tare da amsa gaisuwar ba tare da ya bashi hannun ba.
“Uhmmm”. Ummeeyshi ta saki wani ɓoyeyyen numfashi ganin yadda Kabir ma ke bin Taj ɗin da bahagon kallo.
Sai kuma tayi murmushi ganin Yah Hafiz ya ɗaura hannunsa bisa kan Taj ɗin tare da cewa.
“Baban Malam naji yaranka Imran da Arfa sunce yau zaka tashi zuwa Mexico City, sunanta murnar zasuga Uncle Afif.”
Murmushin yayi tare da sunkuyar da kansa.
Aryan kuma tsuke fuska yayi shi ya tsani yadda aketa maimaitawa cewa Taj ne ya ɗauki nauyin karatun ɗansa.
Ai ga Yusuf ma Taj ɗin ne ya ɗauki nauyin karatun ɗansa Malam ƙarami yana karatu a kan ball sam ba'a zuzutashi kamar nasu, kuma shi ba roƙa yayi ba shima yana da arziƙin da zai iya karantar da ɗansa”.
Yah Sulaiman ne ya ɗan kalli Taj ɗin tare da cewa.
“Jiya Inti ke cemin Abbu Uncle Afif ya zamon jiya da yamma.” sai kuma ya ɗan kalli yan uwan nasa da mahaifinsu kana yaci gaba da cewa.
“Waifa cemin take Abbu duk Uncle Afif ya fiku sonmu, in dai yazo gari to sai ya ziyarcemu yazo kuma yace min zan koma makaranta”.
Sai kuma yayi Murmushin jin Yusuf na cewa.
“Haka tace min kwanaki wai ai Abbunta kam ma bai taɓa zuwa gida taɓa.
Muma sai haihuwanta ne muka je”.
Cike da jin daɗi Sulaiman yace.
“Toh dan Allah Malam inje ince me,”.
Dariya sukayi baki ɗayansu banda Aryan da Kabir Abduraham kuwa cikin sanyi yace.
“Yara da daɗi”.
Da sauri Taj yace.
“In sha Allah kaima zaka haihu Yah Abduraham”.
Murmushin yayi tare da cewa.
“Allah yasa haka”.
Sai kuma malam yayi gyaran murya tare da fuskantarsu da kyau kana tay fara jero musu addu'o'i ɗaya bayan ɗaya.
Suna amsawa da Amin Amin.

Da sauri Taj ya ɗan kalli Malam ɗin sabida ganin har 8 ta kusa cika.
Cikin sanyi yace.
“Yauwa Yah Abana batun asibitin nan ne na Qatar da nace maka an tallata min, shine nake so, a tayani da addu'a idan sayansa alkhairi ne Allah ya tabbatar idan kuma ba alkhairi Allah ya musanya min da abin da yafi alkhairi”.
Kusan a tare Malam ɗin da yayunsa duk sukayi ta mishi fatan al'khairi.
Harda Aryan da Kabir wanda ganin idon Malam na kansu ne yasasu yin fatan alkhairi.

Daga nan duk suka fita.
Shi kuwa Taj a hankali ya ƙara matsowa tsakiyan iyayen nasa, a tare suka ɗaura hannunsu a kanshi suka haɗa bakin.
“Allha ya kaika lfy, ya dawo da kai lfy, ya al'barkaci rayuwarka ya azurtaka da yara na gari masu yi maka biyayya fiye da yadda kakeyi mana, ya azurta yaranka da irin haƙurinka da kawacinka”.
Yana mai lumshe ido yake amsawa da.
“Amin Amin”.
Sai kuma ya kalli Ummeynshi jin tana cewa.
“Sai dai bana fatan yaranka su ɗauki zurfin cikinka domin zasuyi ta cutuwa.
Da kuma ɗayan halin bana so su ɗauka”.
Sunkuyar da kanshi yayi ƙasa, malam kuwa cikin kula yace.
“Ni nafi tsoron ɗaya halin nashi nema, don zurfin cikinsa bai bani tsoro kamar ɗayan”.
Ya fahimci cewa faɗa da nasiha sukeyi mishi cikin son nuna suna ƙin wannan halin nashi da shi bai san ya zaiyi ya canza kansa ba. Yadda in an ƙureshi a abu yayi riƙo sakewa nayin wuya”
Ita kuwa Ishmah cikin sanyi ta fesar da numfashi, tana nazartar wannan halin da suke faɗin.
Sosai sukayi mishi nasiha kana ya fita suka tafi.

“Baba Malam”. Shine sunan da Ishmah ta kira shi dashi lokacin da ya ƙara wayar a kunne.
“Na'am Maman Abba”.
Ya faɗa, tare da kallon Abu Hashim yace.
“Ka hanzarta fa”.
Sai kuma ya ɗan gyara zamansa tare da cewa.
“Muje Airport ko?”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Afwan ai na iso har na shirya na taho Hospital inmu, Khalid ma ya wuce school yau da sassafe yazo wai yazo duba Dadeey da jiki shine ya samemu a haka har ya kai maka rahoto”.

“Ok to ba matsala sai na sauƙa a Mexico zan kiraki”.
Daga nan sukayi sallama

Takwas da rabi dai ta samesu a cikin.
Addis Ababa bole intranational Airport.

Yana isa escorts in shi, na biye dashi a baya, na gefen damanshi ne ya amshi briefcase inshi daga hannun Abu Hashim, daga nan shi ya juya ya koma gida.

Side ɗin da ake tantance lfyar pilots and Hostess ɗin su ne ya wuce.

Shigarsa da kamar 26 minutes ya fito, riƙe da wasu files bisa dukkan alamun rahoton lfyar Hostess ɗin da zai tashi da sune, kasan cersa pilot kuma likita shiyasa yake samun wannan damar.

Wani ɗakin ya shiga mai masifar kyau da tsaruwa wanda yake da girma da faɗi ga haske kai kace da rana ne,
Ƴan matan Hostess ɗin sune a jere kusan su goma biyar a gefen dama biyar a gefen hagu.
Sai kuma wani mutum a gefe bisa alama shima pilot ne.
Hostess ɗin suna tsayene tamkar waɗanda aka dasa, a jere suke gwanin ban sha'awa.
Kusan tsawonsu duk dai-dai ne haka ƴar ƙibarsu.
8 daga cikinsu fararene ƙal irin farin Ethiopia's Gerls sai kuma biyu daga ciki Chocolate collor ne mai ɗan duhu.
8 daga cikin sanye suke da Uniform insu Nevy blue, mai masifar kyau, riga da sket ne, sai hulunan da suka kafa a kawunansu,
Sai biyu daga cikinsu kuma suma riga da sket ne sai dai kalar nasu farine kuma ya ɗanfi na sauran ɗan faɗi da tsawo, kana su akwai mayafi, ƙasan sket ɗin da mayafin an mishi ado da zare Nevy blue.
Yayinda duk sawunsu ke sanye da cover shoe mai masifar tsini da tudu.
Bisa alamu biyun nan masu mayafi su musulmai ne.

Sai wani irin fitinenne ƙamshi suke bazawa, tamkar anyi barin turare.

A hankali yake taku mai cike da kamala haiba gamida kwarji.
Jin wayarsa na Vibration ne ya ɗan sashi zaro wayar da niyar katsewa ganin.
Sunan dake yawo a fuskar wayarne ya sashi amsawa, tare da manna wayar a kunnensa ya maƙale ta da kafaɗarsa.

Sai kuma ya tsuke fuska yayi kici-kici da ita, domin ya tsanin irin masifeffen kallon nan da Agnes Samuel keyi mishi waccan itace ta biyu a layin hagunsa.

“Hummm”. Yace can ƙasan maƙoshinsa jin Ishmah na cewa.
“Dama na kira inji ko kun tashi ne?”.
Sai kuma tayi shiru jin ya ɗanyi gyaran murya cikin dakekkiyar murya mai cike da isa yace.
“Na lura wasu daga cikinku, ba aikin bane a gabanku, kallo nane yake kawosu”.
Da sauri duk sukayi ƙasa da kai.
Ishmah kuwa Murmushi tayi fahimtarta yana nufin da Hostess ɗinsu ne, shiyasa ta gyara zamanta tare da maƙale wayar.

Shi kuwa Taj a hankali yake taku har ya iso tsakiyarsu.
Pilot ɗin nan kuwa Murmushi mai ɗan sauti yayi, sai kuma yayi saurin sunkuyar da kansa ganin kallon da Taj ɗin ya jefa masa.
“Ganan Result's in gwajin da akayi muku, dan sanin ingamcin lafiyarku, Abin takaici, ba a sami meku da cutar da Allah kan ɗorawa bawa ba, sai fitinar tsiya da aka samu a cikin wasunku, wanda suka ɗaurawa kansu.
Ni kuwa bazan iya tafiya da mace mai irin wannan matsalar ba,
Bisa wannan dalilin ne Agnes Samuel bazanyi tafiyar nan da keba, ki koma gida ki gayawa iyayenki abinda kike so su miki sure.
Sai ke kuma Jannifer kema bazamu tashi da ke ba.
Ki huta sabido ba aikin bane a gabanku”.
Wani irin kallon ƙasa-ƙasa mai cike da tsananin flenings da son kusanci da tsarkakken fatar Taj ɗin da shine muradinsu, sukayi ƙasa da kai.
Domin sun san mgnar sa, ɗaya ce in ya faɗa ba fashi more especially irin yau yadda ya tsuke fuska da watsa musu kallon tsanan da yasa suka gaza haɗa ido dashi.

Sanin basuma isa suyi musu ko inkari dashi bane yasa sukayi cib kamar gumakai sai tsananin takaicin soko sunansu da yayi daga tafiyar.
Dai-dai lokacin kuma wasu ƴan mata biyu masu shiga irin na musulman cikinsu suka shigo.
Suna shiga yayiwa Agnes da Jennifer nuni da hanyar fita.

Cikin tsananin son da Agnes keyi mishi da zafin sha'awarsa dake nuƙurƙusan zuƙatansu suka haɗa baki wurin cewa.
“Thanks”. Gashi dai sokesu yayi Amman dole suyi mishi godiya,
Kauda kanshi yayi kamar bai jisuba, hakanne ya basu damar zuba mishi ido haɗi da mgnar zuci.
“Shi Taj namiji ne irin wanda duk macen da tasan maza da ban-da ban zatayi buri da fatan mallakarsa, domin ƙwayar idanunsa kaɗai na iya bayyana suffarsa ta zaraceccen namiji mai cikar sura uba uba gashi dogo, kana gashi bashi da wawan jikin da zai iya tauye Taj ɗin, kana ga shafeffen cikin dake bayyana guru-gurun murɗuwa ta cikin tattausar jallabiyarsa dake manne da cikinsa wanda murɗewar cikin da lafewarsa ne zai ƙara bayyana isar Taj ɗinsa.

Wani yawun sha'awa Jennifer ta haɗiye muƙut lokacin da idanunta suka sauƙa kan lips inshi masu kama da kunnen fure.
Sai kuma sukayi saurin ficewa tare da jan ƙofar.

Tsaki mai sauti yaja tare da fara zirya yana mai faɗin.
“Duk wacce tasan kallona ne ya kawota, ta faɗa tun wuri domin ko munje Mexico naga ƴarinya na min kallon maita acan zan watsar da ita, in wuce Turkey.
An ɗaukeku aikine domin kula da Passingers ɗinmu da sauran ayyukan da wajibinku ne, dan haka ku kiyayeni, kun fahimta.”
Yess sir suka haɗa baki wurin faɗa.

Da hannunsa yayi musu alamun su tafi su fara aikinsu.
Cike da nitsuwa suka nufi hanyar fita, suna irin takunsu na tada fitina.

Pilot Sassy kuwa ɗaya hanyar yabi ya fita.
Shima Taj a hankali yabi bayan Sassy.

Ishmah kuwa murmushi tayi cike da shaƙuwarsu tace.
“Taj meyasa ka soke tafiya dasu?”.
Sassayan numfashi ya fesar tare da yin mgn murya can ƙasan maƙoshinsa yace.
“Yara gaba ɗaya jarabar son maza ya hanasu nitsuwa, sannan ina shiga suna bina da kallo tamkar kura yaga ɗanyen nama”.
Da sauri tace.
“To shine sai ka korasu”.
Tamkar cikin raɗa yace.
“Ishmah tsoro suke bani”.
Sassayan dariya mai sautin da yasashi murmushin jin daɗi tayi kana tace.
“Toh tsoron me kuma, me zasuyi maka kana uban gidansu, ta ƙare maganar tana ƴar dariya mai sassayan sauti, sai kuma tayi cib jin yana cewa.
“Tsoro nake kada su danneni suyi min fyaɗe”.
Ya Salam da sauri ta katse kiran.
Tana mai rufe idanutan da tafukan hannunta duka biyu saboda kunyarshi daya rufeta kalamar shin tazo mata a bazata don tsawon shekaru da suke tare bai taɓa yi mata ma kamancin kalmar ba.

Shi kuwa Taj ido ya lumshe tare da zira wayar a aljihunsa kana ya shiga cikin jirgin.

Karfe goma dai-dai jirginsu ya tashi daga Ethiopia zuwa Mexico City.


Bayan kwana uku. Abpu ne tsaye gaban Ummi cikin tsananin ɓacin rai yake faɗa.
“Ya za'ayi ki bar Adaya ta fita, bayan kina sane da cewa akwai igiyoyin aure a kanta, ya zaki min haka ina tubka kina warwara Hafsa, kina sanefa dan wannan yawace-yawacen da rawar da takeyi yasa na ƙudurta aniyar aurar da ita domin gudun lalacewarta”.
Cikin sanyi da tarin takaici Ummi tace.
“Apbun Adaya ka sani cewa, Adaya ta rainamu saboda son da muka nuna mata da tausayin maraicinta, yasa bata jin tsoron mu, ba yadda banyi da itaba kada ta fita Amman ina taƙi, sai cemin tayi ai dole ta fita, tunda wurin rihazal ɗin gasarar rawar da zasu tafi India nanda wata uku, zataje kuma itace jagorar tawagar Ethiopia, wlh har hawaye nayi Amman Adaya tayi nisa bata jin kira”.
Cike da takaici Abpu ya wuce Parlour sa yana mai zubda hawayen takaici.

Nigeria
A hankali Dr Nafi'u ya tashi zaune tare dasa hannunshi duka biyu ya rumtse kansa a fili yace.
“Im so sorry Aysha ina sonki, bana son cutar dake, in kuma na aureki dole zan raɓa miki cutar HIV dake tare dani, kuma ji nake bazan iya juran

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login