Showing 63001 words to 66000 words out of 74955 words
Chapter 22 - Inda Rai Book 1 Complete Hausa Novel
cewa.
“Hmmmm”.
Still da damuwa afuskarta tace.
“Dan Allah Taj na roƙeka kayi min magana in samu salama”.
Sai alokacin ya ɗan cije lips ɗin sa murya can ƙasan maƙoshi yace.
“Me kika ji”.
Tana jujjuya kai tayi saurin cewa.
“Taj muryanka ta faɗa min baka cikin nutsuwa da kwanciyar hankali muryanka na tattare da damuwa meke faruwa? Jikina ya jiyo min alamun kana cikin damuwa. Me yasamu Laylah”.
Sai alokacin yaji wani irin zafi da zugi azuciyarsa tunaninsa ya tafi kan Laylah dagaske ne kenan?,ciki ne da ita, to idan ya bari aka kashe shi waye zai kula da rayuwar Laylah, Ya Ummeeyshi zataji, waye zai meyewa Ishmah gurbinsa?”.
Asanyaye ya furzar da iska mai zafi jin Ishmah na kiransa a hankali yace.
“Ba abinda ya samu Laylah Ma'eesha”.
Itama cikin sanyi tace.
“Toh yanzu meye ne matsalar”.
Ahankali ya sake runtse idanunsa tare da faɗin.
“Kiyi min Addu'a Ma'eshaa”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“In sha Allah zanyi, to amman addu'ar me zan maka?”.
Tsintar kansa yayi da cewa.
“Kiyi min Addu'a Allah ya bani ikon cinye Jarrabawar dake kutso kai cikin rayuwata”.
Cikin gamsuwa tace.
“In sha Allahu zan yi maka addu'a yanzu ma ina kan sallaya bari nayi maka addu'a”.
Kai ya gyada tare da katse kiran.
Da kallo tabi wayar jin ya katse yasa ta sake tabbarwa yana cikin matsala.
Bisa kan sallaya tayi sujjada tare da cewa.
“Ya Allah ka kare wannan bawan naka, ka tsare wannan bawan naka daga sharrin masu sharri, ka ɗaukaka darajarsa ka kare mutuncinsa ka hanasa ta ɓewa ka yalwata duniyarsa da lahirar da farin ciki ka bashi ikon cinye Jarrabawarsa”.
Haka dai tayi ta mishi addu'oi...
Taj kuwa dai-dai lokacin ya shiga ya samu Meymey na zaune kan 3sitter Laylah na gefenta tana bata tea wani irin kallo ta bishi dashi.
Ahankali ya girgiza kansa kana ya saki Murmushi wanda yafi kuka ciwo Murmushin da yake nuna zallan Jarumtakarsa wanda yake nuna rashin nasarar maƙiyansa a kansa Murmushin dake nuni da alamar Fahimtar abinda ke ranta.
A hankali ya wuceta ya nufi bedroom ɗinsa yana shiga ya kwanta saboda yanda yake jin tsananin ciwon kai da yanda yake sarawa kwanciya yayi ya rasa mai zai tuna a duniya arayuwar ya rasa abinda zai tuna ranan haka ya yini aɗaki, ko jami'in Sallah agida yake yi tunda ya shiga ɗakin bai fito ba sai washe gari da safe ya fito.
Yana fitowa ya tsaya atsakiyar falon kana ya ɗan ɗaga sautin muryan sa da bai fita yace.
“Laylah!, Laylah!!, Laylah!!!”.
Cikin yanayin tsoro da firgita ta fito da sauri ta tsaya gefensa baki ɗaya ilahirin jikinta na karkarwa matsawa kusa da ita yayi tayi saurin ja da baya Muryarsa asanyaye yace.
“Laylah ki tsaya ba abinda zan miki”.
Kai ta shiga jujjuya masa amma ba tace komai ba.
Yana sauƙe ajiyar zuciya yace.
“Yau ba kije school bane?”.
Kai ta gyaɗa cikin tarin tsoro tace.
“Malam yace in daina zuwa school”.
Cikin matsanancin tsoro da firgita ta kai karshen maganar.
Da mamaki yace.
“Yah Abana da kansa ya faɗi haka?”.
Kai ta gyada masa.
“To saboda me?”.
Ya tambaya yana kallonta murya na rawa tace.
“Yace wai kar inje a gane ina da ciki in zubar mishi da darajar sunansa da gidansa”.
lip ɗin sa na ƙasa ya cija da ƙarfi tare da juyawa ya fita.
Yana fita yayi kiciɓis da motar Amal tana shiga...
Yana fita ya wuce asibiti da nufin ko zai iya aiki koda yaje yaji bazai iya aikiba ji yake to mai zai yi daga can ya wuce gidansu Ummey kai tsaye falonta ya wuce yana shiga ya samu falon shiru sai Aunty Maryam da
Rashida,Rashida na ganinsa tayi saurin cewa.
“Taj".
Cikin sanyi ya amsa mata kana ya zauna gefenta itama Aunty Maryam zama tayi gefensa ta zamana sun saka shi a tsakiya.
Ummey kuwa jin an kira sunansa ne yasa ta fito daga bedroom bisa duk kan alamu walaha tayi hannunta riƙe da Carbi zama tayi aƙasa agabansa tace.
“Afif”.
Idanunsa da suka jikkata da dimuwa da tsantsar tashin hankali ya ɗago ya kalleta kana har zuwa lokacin suna nan Ja-ja-jur ahankali tace
“Afif na roƙeka ka yakice wannan ɗabi'a taka ka raba bakinka da wannan nauyin, ka cire wannan zurfin cikin, ka kare kanka Tajudden al'amarin nan fa Babba ne kada ka ɗauke shi da wasa lamarine da zai ruguza duk kan wani farin cikinmu”.
Ahankali ya juya ya kalli Rashida da tun kiran sunansa bata sake cewa komai ba sai kuka.
Aunty Maryam kam zamewa tayi ta kifa kanta jikin kushin ta zubda hawaye.
Ahankali ya zame ya zauna gefen Ummey har gwiwoyinsu na gugan juna ahankali ya ɗaga tafukan hannayensa ya daura kan haɓarta ya shiga share mata hawaye.
Cikin sanyi tace.
“Ba abinda zaka min ka share min hawayena wadda ya wuce ka buɗi baki kayi magana ka fadi abinda yake zahiri ka fadi abinda yake gaskiya, sannan ka fadi abinda yake tsakaninka da Ubangiji ka kuma fadi abinda ka sani akan cikin Laylah”.
Runtse idanunsa yayi yana jin tausayinta aƙasan ransa Ummey kam cikin tarin tausayin sa da kuma jin kai ta cigaba da cewa.
“Ni ban sani ba Yah Abananka bai sani ba daga kai sai Allah ne kuka sani, dole sai ka buɗi baki kayi mgna ne zamu sani ka samu ka kuɓuta da kan ka Tajuddeen”...
Sake runtse idanunsa yayi jin yanda ƙahon zuciyarsa ke harbawa cikin sanyayyan murya yace.
“Kiyi haƙuri Ummey bazan iya ba ban san me zanceba”.
Cikin sauri da matsanancin tausayinsa Rashida ta ɗago kai tare da cewa.
“Afif zurfin cikin ka zai ja mana bala'i kayi magana dole ka fito kayi magana kayi In-kari”.
Ahankali ya subkuyar da kansa ƙasa Ummey kam tafin hannunta tasa ta tallafo fuskarsa kana ta riƙe haɓarsa dai-dai gemunsa tace.
“Ka kalli Idona ka faɗa min me gaskiyar abinda Meymey ta faɗa”.
Cikin yanayin dashi kansa bai sani baya kalleta araunane yace.
“Ummey nima ban sani ba”.
Idanunta na tsatstsafo da ruwan hawaye tace.
“Kamarya baka sani ba?,ka faɗa min gaskiyar abinda Meymey ta faɗa kai kayiwa Laylah ciki?”.
Kansa ya sunkuyar tare da cewa.
“Ummey i don't know bansan abinda zan ceba”.
Yanda yayi maganar ne zai nuna daga ainihin ƙoƙon zuciyarsa yake fita”....
Daga Page 15 zan gama free pages in dai Kinga littafin INDA RAI a wani group ɗin ba group ɗina na littafin ba to na satane kika karanta.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[1/16, 7:57 AM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*INDA RAI*
*BOOK ONE PAGE 14*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*Littafin INDA RAI na kud’ine wannan free pages ne mukeyi kuma suna gab da k’arewa, littafin INDA RAI 1k ne kacal biya ki karanta cikin aminci, zaki iya tura kud’inki ta wannan account d’in 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, zaki tura shaidar biyanki ta wannan numbern- 09097853276. Mutane k’asar Niger kuma 1000fc ne jaka d’aya kenan rak zaku tura kudin karanta littafin +22790899076 ita zaku yiwa magana.*
A dai-dai lokacin kuma Addawa tashigo, zama tayi a bayansa kana ta janyo kansa ta manna da guiwowinta, ahankali cikin sanyi da tarin tausayinsa tace.
“Kayi gadon zurfin cikin nan, amma kuma a dai wannan karon idan kayi zurfin cikin zai matuk’ar cutar da kai sannan zai cutar damu Afif, ka fito kayi magana ka faɗi abinda ka sani kuma yake shine gaskiya.”
Idanunsa da suka sauya launi yayinda jijiyoyin dake cikinsu suka yi jajaye ya ɗago ya kalleta, lips d’insa ya d’an cije kana ahankali yace.
“Ba abinda na sani da zan iya cewa”.
Da yanayin damuwa Aunty Maryam ta kallesa kana cikin sark’ak’iya tace.
“Kamar ya ba abinda ka sani Tajj? wani irin maganane wannan? wacce iriyar magana kake zaka ce mana ba abinda ka sani?”
Ta ƙare maganar cike da jin tsoron anya kuwa Taj bai shiga tarkon shaiɗan ba.
Dai-dai lokacin Zakiyya ta fito hannunta riƙe da waya tana hawaye wanda bisa alamu da Aunty Halima take waya.
Ita kuwa Aunty Halima shesh-sheƙan kuka take Ummey ta mika wa wayar.
Ummey na amsa tace.
“Toh Halima ya zamuyi addu'a kawai zamuyi masa amma lallai muna cikin ƙalubale, muna gab da fuskantar wani kalubale mafi muni a rayuwarmu, muyi ta addu'a Allah ya kawo mana da sauƙi, ni da Abbanku jiya kwana mukayi ba muyi bacci ba, sannan yau da safe naje na samu Dr. Abbas na duba shi BP d’insa ya hau.”
Jin hakan yasa Taj sunkuyar da kansa ƙasa tare da d’an yunƙurawa ya miƙe ahankali.
Kallonsa Ummey tayi tare da faɗin.
“Ina zakaje?”.
Ƙwayar idanunsa ya risinar ƙasa kana atausashe cikin had’iye tarin damuwarsa yace.
“Zanje duba Yah Abana”.
Ya ida maganar yana mai jin ƙaunar iyayen nasa acikin ransa.
Yana shiga ɗakin kuwa ya samu kusan baki daya yayunsa Mazan suna nan sai kuma ya ɗan tsaya jin Yah Hafiz na magana cikin sanyi da taushin lafizi da biyayya yana cewa Mahaifin su.
“Abbah kafin ayi komai a nutsu abi abin ban Ahankali, Abba kaine mafi sanin halayen mu gaba ɗayanmu mu ƴaƴanka. Allah ne ya tarbiyyantar damu amma kaine ka daura mu kan hanya Abba ka sani cewa Taj baya ɗaya daga cikin irin mutanen daya kamata ace wannan zargin ya hau kansu, kuma ka tuna cewa Taj mutum ne ajizi dan girman Allah da Manzonsa koda an sameshi da ajizanci a cikin maganar nan ayi mishi uzuri a sassauta mishi”.
Cikin sauri Yah Yusuf ya karbi maganar da cewa.
“Sosai ma Abba dan Allah asan abinda za'a yi akan maganar nan, ni inaga Maganar nan anyi masa bahagon fahimta ne yarinyar nan Meymey ita kanta batasan mai take faɗa ba”.
Ahankali Yah Abana ya ɗago gajiyayyun idanunsa dake nuni da damuwa ya kalli Tajj sai kuma ya sunkuyar da kansa.
Tajj kuwa lokaci ɗaya yaji hankalinsa yayi masifar tashi fiye da wanda yake ciki zuwa yanzu ya fahimci mahaifinsa kamar baison ganinsa ne jiki amace ya isa tsakiyarsu kana ya zauna a gaban Yah Abana tare da faɗin.
“Yah Abana Barka da safiya”.
Batare daya amsa gaisuwar nasa ba yace.
“Menene gaskiyar abinda Meymey ta faɗa?”
Ahankali ya motsa Lips ɗin sa zuciyarsa na wani irin mummunan bugawa yace.
“Ban saniba Yah Abana”.
Kai Yah Abana ya kawar batare daya sake bi ta kansa ba.
Murya na rawa ya ɗan zuba masa Idanu ganin yanda lokaci ɗaya ya ya faɗa, asanyaye kuma yace.
“Yah Abana ya jiki?”.
Ƙin amsawa yayi sai ma rufe idanunsa da yayi.
Ganin haka yasa ahankali Taj ya zauna kana ya sunkuyar da kansa ƙasa tare da sa hannunsa da nufin kamo ƙafar mahaifin nasa dan yi masa tausa.
Saidai hakan baikai ga samuwa ba yayi sauri janye hannunsa sakamakon Yah Abana da ya dakatar dashi ta hanyar janye ƙafarsa.
Kafaɗarsa Yah Abdurrahman ya dafa tare da faɗin.
“Afif kai namiji ne fa ya kamata ace kana da ƙarfin zuciyar da zaka iya yaƙi da komai.
Ya kamata ace zurfin cikin ka ya tsaya iya kan hakuri bakan abinda zai cutar da kai ba kana ya cutar damu”.
Sai kuma duk sukayi shiru suna kallon Aryaan dake cewa.
“Akan komai dai ɗan Adam zai iya zurfin ciki mun shaida Afif nada zurfin ciki amma dai akan wannan maganar in dai yana da gaskiya yasan ƙazafi akayi masa dole ya fito ya wanke kansa”.
Ya ƙare maganar da iya yaƙinin gaskiya yasan dole in dai Afif yana da gaskiya acikin maganar dole ya fito ya wanke kansa.
Taj kam shiru yayi batare daya tanka kowa ba...
Dai-dai lokacin kuma Meymey ta shigo hannunta riƙe da Laylah da kuma sauran Matan Yah Abana duka su huɗun suna shigowa Hajiya Babba tace.
“Ni yanzu ma an tabbatar da cewa shin akwai cikin?,ko yaya?”.
Cikin sauƙe nannauyan ajiyar zuciya Yah Hafiz yace.
“Batun ciki kam tabbas akwai shi domin likitoci sun gwada an gani cewa akwai ciki harna wata 2”.
Cikin sauri Ummu Aryaan tace.
“Aje dai asake gwada wa shine kawai abinda yafi dacewa”.
Cikin sanyi Meymey dake zaune a gefen Mom Amal tace.
“Wani gwaji kuma ya rage Umma? ai ba gwajin daya rage, likitoci nefa sukayi gamayya a kan gwajinta kuma suka tabbatar da cewa tana da ciki.”
Kai Ummu Aryaan d’in ta girgiza tare da cewa.
“Ai shima Taj ɗin likita ne yaje ya gwada da kansa a tabbatar mana”.
Cikin sauri Meymey tace.
“Toh Umma in dai da kansa zai gwada ai bazai taɓa fadar gaskiya ba, tunda yasan abinda yake tafiya, nifa nasan cewa shi ya aikata duk wannan abun kuma shima ya sani.”
Cikin taɓe baki Aryaan ya karbi maganar ta hanyar cewa.
“Toh dama ya za'a yi wanda ake tuhuma ya zama shine mai yin gwaji? kamar fa Shari'a ce ace an bawa mai laifi alƙalanci, kawai Idan ba'a yarda bane sai asake tafiya wani waje aje a gwada”.
Cikin sauri Yah Yusuf yace.
“Toh shikenan asake ayi wani gwaji a tabbatar”.
Asanyaye Yah Abdurrahman yace.
“Toh shikenan bari na haɗa ku da abokina Dr Sonail Khan ɗan Indi'a ne amma anan yake aiki ”.
Amsawa sukayi saɓanin Tajj da har zuwa lokacin kansa ke k’asa, bayan ciwon da yake ji acikin zuciyarsa ya gaza iya cewa komai, dan har yanzu ganin abun yake kamar acikin mafarki.
Meymey, Laylah, Yah Abdurrahman, da kuma Khabeer tare suka tafi asibitin.
Bayan awa uku da tafiyarsu suka sake dawowa dai-dai lokacin kuma anyi sallar la'asar bayan sun dawo sun zauna Kabeer da takardun gwajin ke hannunsa ya miƙawa Yah Abana tare da cewa.
“Gashi fa tabbas akwai ciki har na tsawon watanni biyu”.
Azuciye cikin b’acin rai me tsanani Yah Abana ya wurgawa Tajj takardun, cikin k’unan zuciya ya kuma cewa.
“Menene gaskiyar waɗan'nan takardun?Tajuddeen me gaskiyar wannan abin? Me dalilin faruwan haka? Waye Uban cikin nan?”.
Ya jero masa duka tsauraran tambayoyin ajere Akuma lokaci ɗaya.
Shiru ya kumayi kamar yanda ya saba saboda bazai iya cewa komai ba.
Saidai jin ya sake jero mai tambayoyin a hargitse ne ya sashi buɗe baki hankali yace.
“Kayi haƙuri ya Abana”.
Kusan duk a tare suke kallonsa cike da fara karaya.
Ita kuwa Meymey kai ta girgiza alamun.
“Toh kun ji dai”.
Zazzafan Iska Yah Abana ya furzar daga bakinsa kana akausashe yace.
“Tunda baza ka iya magana ba ka fita bana son ganinka!”
Ahankali ya yunƙura kana lips ɗinsa na rawa cikin wani irin yanayi me wahalar fassaruwa yace.
“Yah Abana kayi haƙuri ka gafarceni”.
Idanu Yah Abana ya rumtse tare da nuna masa k’ofa rai b’ace yace.
“Ka fita sai lokacin da kasamu hujjoji abakin ka kazo ka faɗa min”.
Jikinsa ne gaba d’aya ya d’auki rawa cike da tsananin ruɗani ya miƙe ya nufi hanyar fita.
Yana fita kuwa Ummey tabi bayansa da sauri, tare da riƙo hannunsa murya araunace tace.
“Ina zaka je Afif?”
Kansa dake masifar ciwo ya d’an girgiza kana cikin mawuyacin halin da yake ciki murya can ƙasan maƙoshi yace.
“Zan tafi gidan Addawa”.
Numfashi ta fesar cikin tsananin tausayin d’an nata tace.
“Toh ai itama Addawan tana nan bari in mata magana sai ku tafi tare, kaci abinci ma kuwa?”.
Kansa ya girgiza cikin lumshe idanunsa ahankali yace.
“Bana jin yunwa".
Addawa kuwa jiyo maganar su ne yasa ta fito, tare da bin bayanshi suka shiga mota suka tafi...
Ummey kuwa direct parlorn ta ta koma sai kuma ta kalli Rashida dake cewa.
“Ummey yayi magana”.
Kai ta girgiza tana kokarin maida hawayen dake kokarin zubo mata tace.
“Um-um baiyi magana ba Rashida, sai haƙurin da yake badawa dake tayarmin da hankali, Abban ku kuma naga bai fuskanci lamarin nan da fuskar daya kamata a ɗauke shiba yanzu cewa ma yayi baya son ganinsa”.
Da sauri Aunty Maryam ta girgiza kanta tana maimaita kalmar “Allahumma Ajirni Fii musibati wa akhlifliy khairan Minha!”
Ummey kuwa araunace ta cigaba da cewa.
“Yace ya fita ya bashi waje In har ba zai yi magana ba, yayi maganar nan kamar ya manta waye ne Taj kamar ya manta menene halinsa mutumin da tun yana karami baya iya In-kari”.
Atsorace Aunty Maryam ke kallonta cikin tarin damuwa kuma tace.
“Toh yanzu Ummey ya zamuyi?”.
Cikin sanyi Ummey tace.
“Yanzu sai dai ku tashi kuje gidan Alaramma Sulaiman tunda ni kona tambayi Abbanku bazai barni in fita ba, kuje kuyi masa bayanin ga abinda yake faruwa inada yakinin shi kaɗai ne zai iya fahimtar da Abbanku wani abu, dan na fahimci Uncle Jibril bazai taba bincike akan duk maganar da Meymey take faɗa ba”.
Kai Aunty Maryam suka gyaɗa daga nan suka fita suka tafi kai tsaye gidan Alaramma Sulaiman suka tafi wanda shine Aramman Mahaifinsu mai ja musa baƙi suna tafsir bayan sunje gidan suka masa bayanin iya abinda suka sani.
Da kansa ya rakosu har bakin mota yana mai jaddada musu cewa in sha Allahu da daddare zai zo su gana da Yah Abana.
Da daddare Alaramma Sulaiman yazo bayan sun zauna da Yah Abana bayanin da Yah Abana ya masa da yanda Taj yaƙi yin magana sai jikinsa yayi sanyi hankalinsa ya tashi Yah Abana kuwa ya ɗaura da cewa.
“Kwanan nan fa da Afif yai tafiya Nigeria yarinyar ya ɗauka kwana goma fa sukayi da ita kafin suka dawo, na gaya maka cewa acikin lamuran Taj akwai alamun ayar tambaya?”.
Idanunsa ya runtse yana jin wani irin ɗaci acikin azuciyarsa kana ya cigaba da cewa.
“Sannan koda nasan tabbas Taj yana da zurfin ciki acikin al'amarin nan kamata yayi ya fito ya wanke kansa asalima Taj sai shiru yake duk abinda na tambayesa sai yace bai sani ba ko yace wai inyi hakuri me haka yake nufi kenan? Taj ya gama ɓata min sunan zuri'a ya gama tozartani ya gama cimin zarafi kana ya ƙasƙantar min da zuri'a”.
Cikin sauri sheik Sulaiman yace.
“Kada kace haka ka bari sai an tabbatar da komai kayi magana akai ”.
Kansa ya girgiza yana mai jin daci azuciyarsa yace.
“Wani tabbaci ne ya rage?na rasa ta ina zanbi in samu tabbacin da zan iya gamsuwa dashi”.
Haka dai sukayi tattaunawar suka gama bayan Alaramma Sulaiman ya sake tunarsa dashi amma duk da haka basu gano bakin zaren ba...
Wasa gaske haka aka ɗauki tsawon kwanaki biyar ana ta gumurzu Taj ya kasa wanke kansa kana Meymey babu abinda take sai ƙara jaddada cewa shi yayiwa Laylah ciki.
Ahankali ya shiga cikin gidan yana mai sauke zazzafan Ajiyar zuciya yau kwanansa biyu bai zo gidan ba saboda koda yazo mahaifinsa daga gaisuwarsa da yake amsawa babu wata magana da take sake haɗa su.
Ahankali ya ƙarasa shiga Falon Yah Abana zaune ya