Showing 45001 words to 48000 words out of 135778 words

Chapter 16 - Exiled Prince Book Three Complete Hausa Novel

Meerah   

24 Oct 2025

314

ya na sakin wani dan karamin kuka ya ce " Najoua , da gaske ke ce ? ba abun da ya same ki ? ba su cutar da ke ba ko ? "

ya kai karshen ya na raba jikin shi da nata , ya talabo face din ta da hannayan shi biyu

Dum ya ji gaban shi ya fadi lokacin da idanun shi su ka sauka saman shatin hannun mutum a face din ta , da allamun marin ta a ka yi ba guda ba dan wajen ya yi jazir

cikin bacin rai Hakim ya juya ya kai wa Miram wani mugun bugu a fuska ya na fadin " wa ya ba ka izinin taba min ita ? "

da sauri Sojoji su ka taho su ka ririke Hakim dan da ga gani zai iya kashe Miram

Cikin nitsuwa Malik ya ce mishi " Hakim , ka fara tambayar ta wanda ya yi mata hakan tukunna "

cak Hakim ya tsaya ba shi kadai ba duk mutanan fadar sai da hankalin su ya koma kan Najoua

Umarni Malik ya ba wa sojojin nan a kan su saki Hakim

ba musu su ka sake shi su ka dan ja da baya kadan

su na sakin shi ya juya ya kali Najoua ya ce mata " baby , ki kontar da hankalin ki ba abun da zai yi miki , ki fada min waye ya dake ki "

ba ta ba shi amsar tambayar shi ba ta sa hannun ta dama ta yi sama da hannu abayar ta na hagu ta na kuka ta ce " ni ba duka na ya yi ba abun da ya fi duka ya yi min "

a rude Hakim je ce mata " please baby tell me , ki fada min na yi miki alkawari ba zan kyale shi ba "

girgiza mishi kai ta yi murya kassa kassa yadda shi kadai zai ji ta ce mishi " He tried to rape me " ta kai karshen ta na kara sautin kukan ta

Dan zaro idanu Ya yi ya na maimaita abun da ta fada cikin zuciyar shi , ya na shirin magana ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Miss Najoua , za ki iya gwada mana wanda ya yi miki hakan ? " ya fada kamar ya ji abun da ta fada

a hankali ta dago kai ta kali Malik sannan ta gyada mishi kai a hankali ta kali saitin Maza ta na bin su da kallo daya bayan daya

cikin rudu Hakim ya ce mata " ga wanda ki ke magana a kai nan why ki ke kallon wani wajen daban ? " ya fada ya na nuna mata Miram

girgiza mishi kai ta yi ta na cewa " no ba shi ba ne , wancen ne " ta fada ta na nuna shi da yatsa

a tare duk su ka kali saitin da ta nuna , nan su ka ga ashe Mohammed ta ke nunawa

su na a haka su ka jiyo Muryar Miram ya ka cewa " Ran ka shi dade har da shi , tare mu ka kashe Malik , shi ya kawo shawarar kashe shi "

da sauri Mohammed ya katse shi da cewa " kai Miram ka san abun da za ka fada , ranka shi dade wlh karya ya ke min , babu ruwa na cikin abun da ya aikata "

ya na gama rufe bakin shi Najoua ta ce " ranka shi dade karya ya ke , wlh har da shi , tare su ka yi wannan aikin sun sha kawo min ziyara a tare " ta fada da karfi kamar za ta yi kuka

mikewa tsaye Mohammed ya yi ya na girgiza kai ya na fadin " wlh ranka shi dade karya su ke min , dalilin mi zai sa na kashe Mal ...... "

bai kai karshen maganar shi ba Malik ya katse shi da cewa " saboda ba kai a ka nada a matsayin Malik ba duk da kai ka auri babbar y'a ga Mai martaba Malik Abdoul latif bin Saud ba "

Dum Mohammed ya ji gaban shi ya fadi har wani zaro idanu ya ke ya na kallon Malik

a hankali Malik ya mike tsaye , da sauri mutanan wajen su ka yi kokarin tashi , sai dai ya daga musu hannu a kan su zauna , ba musu kowane ya koma ya zauna ya na kallon Malik

a hankali ya yi taku biyu sannan ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ya ce wa Mohammed " kamar yadda na fadawa shi Miram , duk wani abu da ke faruwa cikin masarautar nan ina sane da shi , ko da kuwa gwayar zarra ce , kawai dai ina shiru ne na ga gudun ruwan ku , ko ka zata ba ni da masaniya a kan abun da ku ka shirya , na san kai ka kawo shawarar kashe Malik , da farko Miram bai yarda ba amma ka matsa mishi , tun kafin na dawo masarautar nan ku ka shirya wannan , tare auren Gimbiya RIANNA da Miram yadda da kun kashe Malik a nadda Miram matsayin Malik tun da ba na nan yadda za ku yi yadda ku ka so cikin masarautar nan , amma shirin ku ya ruguje bayan dawowa ta , duk da hakan sai da ku ka saka a kashe Malik , da ga baya ya zagayo ya kashe ni , amma General ya yi nassarar kamo Sniper din da ku ka saka aikin , bayan an kai Hakim prison , sai da ka je wajen shi ka yi mishi kashedi a kan kar ya fada min gaskiya a kan cilas ta mishi a ka yi ya kashe Malik , amma bai saurare ka ba ya fada min , bayan na yi maganar a fada , shi ne ka tsorata , ka je wajen Miram , ka ba shi shawarar ku kashe Hakim tun kafin ya bayana gaskiya , a ranar da Miram ya yi kokarin kashe shi a cell , a tare ku ke , sai dai kai , ka tsaya a bakin kofa ba ka shiga cell din ba , ta yadda ko an tashi kamawa , Miram ne za a kamawa ko ba haka a ka yi ba ? " ya kai karshen ya na dagawa Mohammed gera guda

wasu wahalalun yawu Mohammed ya hadiye , ramin da ya gina ya rumzo mishi , ta ina zai fita yanzu ?

GASKIYA MALIK KA CIKA DAN SA IDO

🤣🤣

NI BAN MA SAN WANNAN LABARIN SAI DA YA FADA , GASKIYA NA SARA WA BASIRAR KA

😂😂

ya na a haka kawai ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Mohammed Magid , Miram bin Salman , an kama ku da laifin kisan marigayi Malik , ko ku na da abun fada kafin na yanke muku hukunci ? "



da sauri MALIKAT AL'UMU ta ce " Ranka shi dade me kuma za su ce ? A yanke musu hukunci dai'dai abun da su ka aikata , dama dokar musulumci ta ce wanda ya kashe a kashe shi , hukuncin kisa ne kawai ya dace da su , dalilin su É—iya na guda uku sun rasa mahaifin su , ni da yar uwa ta mun rasa mijin mu , wace damar magana za a ba su kawai a kashe su kamar yadda su ka kashe shi " ta kai karshen ta na sakin kuka

a hankali MALIKAT INAS ta sa hannu ta janyo ta jikin ta ta rungume dama Sofar su a kusa ta ke , Ita kan ta ba ta taba tunanin mijin yar uwarta zai raba ta da nata mijin , idan ta ce ta yi magana ta san Manisha ba za ta ji dadi , shi ya sa kawai ta yi shiru amma har cikin zuciyar ta ta na bayan maganar MALIKAT AL'UMU

Shi dai Malik shiru ya yi ya na sauraron abun da su ke fada , kawai ya tsare Mohammed da idanu babu ko kiftawa , shi dama ya na sane da kishin da Mohammed ke yi wa mahaifin shi , dan tun ya na yaro Mohammed ya sha tsangwamar shi , ya na dukan shi , har ya zagi Malik gaban idan shi , amma bai taba nunawa ba

A hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya bude baki ya ce " duk wanda ke son yin magana , na ba shi dama , ya yi maganar shi "

a hankali Miram ya dago kai ya ce " ranka shi dade , ko cell za a saka mu kar a hada ni da shi "

" kar ka damu kowane za a saka shi cikin ta shi cell din " Malik ya fada cikin nitsuwa

da sauri Mohammed ya kali Miram ya ce " maciya Amana kawai "

wani murmushi mai dan sauti Miram ya yi kafin ya ce " Ai kai ne wanda za a kira da maciya amana , kai da kashe mijin kanwar matar ka , sannan ka yi wa yarinyar mutane fyade , ko kunyar shekarun ka ba ka ji ba "

da sauri Najoua ta ce " bai yi nassara ba "

wani dan karamin murmushi Miram ya yi kafin ya dago kai ya kale ta ya ce " ai ni ba a kan ki na ke magana ba "

da sauri Mohammed ya ce mishi " kai Miram kar ka yi min Kazafi dan kwatar kan ka "

hararrar shi Miram ya yi kafin ya juya ya kali Malik ya ce " ranka shi dade , mai girma Rafik , Mohammed shi ya kashe maka yarinyar ka , Tun da lokacin tonan asiri ne , ba zan kyale ka ba "

a dubu dari Rafik ya mike ya na fadin " Miram , ka na nufin Mohammed shi ya kashe Rhalida ? "

gyada mishi kai Miram ya yi ya na fadin " shi ya kashe ta , har school din su ya je ya dauke ta da sunnan zai kai ta gida , da ga nan ya wuce da ita gida na da ke Riyadh ya yi mata fyade , da ya ga ta mutu , ya bunne gawar ta a cen , yadda babu wanda zai samo ta "

cikin bacin rai Rafik ya nufi Mohammed a zafafe ya na isa ya wanka mishi wani gigitacen mari har sai da ya bidi faduwa

ya na shirin magana ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " Rafik ! "

wani mugun kallo Rafik ya wurga mishi cike da takaici , ba tare da ya ce komai ba ya koma saman sofar shi idanun shi na cikowa da ruwa gaskiya Mohammed bai kyauta mishi ba , inda ya fada mishi ya na son yarinyar shi da ba abun da zai hana shi ba shi auren ta , amma yanzu ga shi yayi sanadiyar mutuwar ta ko gawar ta bai gani ba tsawan shekara biyar har yanzu su na jimamin rasuwar ta

a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya kafin ya yi wa Hakim allamun ya karaso da hannu

ba musu Hakim ya saki Najoua , ya fara takawa a hankali ya karaso gaban Malik

har zai zubewa saman guyiwowin shi Malik ya taro shi , ya koma ya tsaya ya na kallon Malik

a hankali ya tako ya zo dab da shi ya kai hannu ya riko hannun Hakim , sannan ya zagayo da dayan hannun a bayan shi ya fido gun ya daura saman Hannun Hakim

sannan ya kai bakin shi saitin kunnen shi ya ce " Duk duniya babu laifin da ya kai cin zarafin mace , ba zan kama ka da laifin kisan Malik ko ni ne zan iya yin fin hakan for my Cutie dan haka na ba ka dama , ka karbawa matar ka hakin ta "

ya na gama fadar haka ya yi taku biyu baya ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ya na kallon Hakim

kallon gun din Hakim ya yi kafin ya dago ya kali Malik da ya tsare shi da idanu

a hankali ya gyada mishi kai allamun ya yi abun da ke cikin zuciyar shi

dawo da kallon shi Hakim ya yi kan gun din ya yi charging din ta ya sauke ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi a hankali kafin ya sake bude su cikin na Malik , cikin dakikan da ba su kai biyar ba , ya yi wata irin juyowa ya saita zuciyar Mohammed ya harbe shi , sannan ya sauko ya saita Miram a kai ya harbe shi

kowa cikin Fadar sai da zuciyar shi ta buga dan ba karamar razana su ka yi ba

Hafsat kuwa har da Sakin kara ta tashi da gudu ta nufi Mohammed ta na kuka

Malik kuwa bai bi ta kan su ba ya juya ya sa hannayan shi biyu ya dauki Inaya cak kamar baby , sannan ya dawo da kallon shi kan Hakim ya ce " Diya , ka sa a shirya jirgi nan da one hour a mayar da Hakim da matar sa Marocco "

ya na gama fadar haka ya fara takawa bai bi ta kan kowa ba ya sa kafa ya fice fadar da Inaya

wata nanauyar ajiyar zuciya Hakim ya sauke jin an ce a meda su Marocco ba tare da an yanke mishi wani hukunci ba , har lumshe idanun shi ya yi ya na sakin wani dan karamin murmushi

ya na a haka ya ji Najoua ta rungumo shi ta baya , a hankali ya juyo ya rungumo ta ya na sumbatar forehead din ta

🤧

kai soyayya dadi

WAI KU TSAYA NI KADAI NA LURA BABU ROUKSAR A WAJEN NAN KO KUWA ?

🤔🤔

ALLAH YA SA BA DAI WATA TA KULA BA , GASKIYA BAN YARDA DA SHIRUN NAN NATA BA YA KAMATA MU LEKO TA



â–ª

ROUKSAR

a tsaye ta ke cikin kitchen na part din MALIKAT AL'UMU , ta na rera wata waka ta na rawa da kugun ta da allamun ta na cikin annashuwa

yankar Fruits ta ke cikin konciyar hankali ta gyara su saman wani tray gwanin burgewa

sai da ta Kamala yankar fruits din nan tsab , sannan ta saki wani makirin murmushi ta lumshe idanun ta , a hankali ta fara motsa lips din ta allamun wani abu ta ke karantawa

a hankali daya da ga cikin jelar gashin ta , ta fara yin kwarri ta goma green , scales irin na maciji su ka fara fitowa , nan take jelar ta koma wani dankareren maciji , ya na fido Tongue din shi waje ya na kukan macizai

wani kyawatencen murmushi Rouksar ta saki kafin ta ware idanun ta da su ka koma tamkar na macijin nan da ke cikin jelar gashin ta

a hankali ta kai hannu saitin kan macijin nan

nan take ya fito da ga cikin jelar gashin ta , ya nade a saman hannun ta , ya daura kan shi tsakanin yatsun ta biyu

a hankali ta matso macijin nan saitin face din ta ta ce " My baby , yau ina ji a jiki na ranar nassara ce , Burin mu zai cika , kar ka gaji da ni ka san abun da na ke bukata a wajen ka "

ta na gama fadar haka macijin nan ya yi wani kuka ya na fiddo tongue din shi , kafin ya juya

a hankali ta matso da hannun ta ta kai shi sama kadan da tray din fruits din

bude bakin shi Snake din na ya yi , nan take poison din shi ya fara fitowa da ga cikin hakwaren shi , ya fara zagaye Tray din nan duk fruits din da ke a sama sai da ya zuba musu poison

sai da ya gama sannan ya rufe bakin shi ya na kukan macizai

wani kyawatencen murmushi Rouksar ta saki kafin ta matso da Snake din nan ta kai saitin bakin ta ta manna mishi kiss a saman jikin shi ta na cewa " na gode baby na , za ka iya komawa ka huta "

wani dan karamin kuka ya yi mata kafin ya yi wata irin burra ya koma cikin jelar gashin ta nan take ya bace a ciki

ya na bacewa Rouksar ta juya ta nufi kofar fita kitchen ta na karasowa bakin kofar glass din ya zuge sai ga wasu mata hudu tsatsaye geffen door din

a hankali ta daga kafa ta fito , ta karaso gaban matan nan ta tsaya ta ce musu " ga Fruits cen Tesnim ta Shirya wa Malik , ku dauka cikin abincin da za ku kai wa part din shi , yanzu nan kafin su Kamala zaman fada " ta na gama fadar haka ta yi gaba abun ta ta na taku kamar ita ce Malik

ba musu matan su ka shiga kitchen su ka fara shirya abincin da za su kai wa part din Malik su ka hada da tray din nan na fruits da Rouksar ta shirya sannan su ka tafi





â–ª

MALIK

kai tsaye part din shi ya koma ya Inaya , amma a floor na Uku ya tsaya , a parlour

zaunar da ita ya yi saman sofa sannan ya zauna geffen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login