Showing 3001 words to 6000 words out of 96493 words

Chapter 2 - Kana Naka Book 1 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

192

yace"Ruwa k'adai ne kuke dashi agidan..?
Yafada muryansa asama kusan fa Fa'iza ta fara maida shi Sama sama ko ba da ita yake mgana ba ya yi mugun Sabon da sai ya Daga murya.
Cikin Ladabina nace"Taliya Hafsatu ta Dafa ma su Amir ina jin ta kare ma..Sai dai bari da sauri nayi maka ko Faten Dankali ne..
Dayake bansan kana Hanya ba."
Komawa yayi ya jingina jikin kujeran dayake kai yana maida Hankalinsa kan Tashar Mbc action din Daya sanya Reastling din da ake yi ya Fara Daukan Hankalinsa ganin haka yasa na Mike jikina na rawa na kwashi Farantin Dana shigo dashi na Fice ya Bita da kallo kamar ya saka kuka ai bazai ce A'a ba  inda kuma bazai Zagi Fa'iza ba kenan ta iya girki,girkinta ba inda baza'a Kaisa ba,Shi kadai ne abu mai kyau a rayuwar Fa'iza ban dashi shi dai bai gani ba ya Dade yana ganin mutane marasa sa'a a rayuwarsa ammh Rashin Sa'ar Fa'iza na musamman ne ta rasa wasu abubuwa masu Muhimmanci a Rayuwarta Rashin Sa'arta ne ma ya shafesa shima Gabadaya Rayuwarsa na neman komawa irin tata ba Domin Mama na Tsaye kansa ba, da Shima ya koma Dangin KURAME kamar yadda Zama da Kaddara ya Hadasa da Fa'iza.
Minti Talatin da wani abu na Sake Dawowa Dauke da Voul cike da Faten Dankali da Hanta sai maltina mai Sanyi Dana Hado mai dashi bai yi Tsaya mgana ba Domin yunwa yake ji Gidan Mama Tuwo sukayi shi kuma na Cimarsa bane abaya dai yaci banda yanzu Dayake cin guminsa.
Kasa ya Sauko ya tankwashe kafa ya sha Fantansa sosai,ya Dora da ruwa Maltina,Yayi gyatsa Lokaci D'aya da Hamdala Duk Fa'iza na gefensa yana Gamawa Jikina har rawa yake yi wajen kwashe kayan daya yayi amfani da su, na maida Kitchen adaran nan na wankesu domin Fa'iza in akwai abunda ta tsana kwano ya kwanar mata akitchen ba'a wanke ba.
Ita dai barta da barin shirgin yara da Rashin Shiga mai Fasali ammh ita da ya'yanta basu da kazanta ko yaya ne wanka ne Safe da yammah ita da yaran Duk Ranar duniya har sun saba suma.
Sai da nagama na kara leka Dakin na wajen Ahmad in sauri ban tsaya na  Tofe shi da addu'a ba yasa na bata Lokaci Wajen Yimai addu'a Hafsatu bata Dakin kila tana Dakin datake sauka in tazo Gidan.
Dayake nayi wanka Dazu da mangariba ban yi Tunanin Sake wani wankan ba na Sauya kayana zuwa wata Dogouwar Riga ta barci mai Taushi mai gajeren hannu,Duk da ina na da masu wando basa Burgeni nafi son Dogayen masu rufe min Har Cinyoyina Fa'iza ta Tsani ta saka kaya taga sun kamata ko sun nuna Tsiraicinta.
Ina cikin Daure gashin kaina Da na Tsefe shi yau da Safe,Hafsatu ce zata min Kitso yau bata samu Dama ba Karfanfan gashina tun na Virgin Dakyar yake Haduwa cika garesa bai da Tsawo inaa Hakin kamasa na Daure cikin Ribbon baji muryan ISHAQ asama yana Faman kiran sunana kamar yadda ya saba.

"FA'IZA.."

"FA'IZA.."

Da sauri na bar abunda nake yi lokaci daya na Rarumi Hulata ta barci na Saka ina niyar fitowa Daga Dakin ya shigo,ganinsa Tsaye a gaban ba Kikam da irin kallon Dayake min yasa nq rankwafa da Sauri ina Fadin"Gani ina..ina..!
Ban karisa ba ya Daga min Hannu Lokaci Daya yana Fadin"FA"IZA hala baki sam zan kara aure bane..?
Yafada yana Tsareni da manyan Idanuwansa.
Gabanna ya Fadi Ras! Sai na Daburce Da yanayin da yayi mganar,ba da karfi bane sai dai ai mganar auran nasa na Haddace ta akaina shiyasa nq karancin Bakinsa.
Cikin Fusata yace"Wai bada ke nake mgana bane kikamin banza..?
Da Sauri nace"Eh..Eh..Na sani..Mamakofar soro ta fadamin..Sannan sannan.."
Daka min tsawa yayi yana Fadin"Sannan me..?
Kinsan bana son wannan sanyin naki in muna mgana ko..?
Mgana bata kai ta kawo ba kiyi ta uban Rabata kamar wani abun arziki zaki Fada.."
Kokarim Boye Raunina nayi Cikin Dakewa nace"Anty Binta batagwara ta Fadamin wanchan satin da muka Hadu gidan Mama."
Wata Uwar Harara ya jefa min kafin yace"Kin sani ammh ko Fatan Alheri bazaki min ba Fa"iza..?
Kina bakinciki ne saboda zan kara aure..?
Da Sauri nace"Ahah.Naga baka nan ne,Shiyasa.."
Takaici ya kamasa kafin yace"Baki da waya ne..?
Ko lambatace baki da ita..?
Koda yake ke ai ba matar kiran jin Lafiyan miji bace za dai ki kira in wata Bukatarki ta taso miki."
Ya karishe Fada yana kallona Cikin Doguwar Rigar Barcin dana sanya kadan ya Rage bai yi Dariya ba.
Dariyan Takaichi wai zaki kwana da Miji ki saka wannan abu kamar kullib goro.
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Na zata kina Bakinciki ne nace kin so kanki Fa'iza Shekara Takwas nayi ina Zaune Dake ban kara aure ba..Tsakaninki ga Allah ban miki alfarma da Mutumci ba Fa"iza..?
Fadamin da bakin ki na yi miki adalci ko ban yi miki ba..?
Ya fada da karfi yadda Zan jisa jikina  na rawa nace"kaayi min..sosai kayi min adalci.."
Naso na Daure ammh ina Raunina ya bada ni sai kuka hawaye sharr Tsayawa yayi yana kallon na kafin ya Tabe baki yace"Naji Dadi da kika Fahimci haka..Kada Goggon karofi  da yan'uwanki su tasaki suna Faman tambayanki kice musu ban yi miki adalci ba kiga yadda zamu kwashe.."
Malama ki kuma cire min wannan bargon Dake jikin ki wlh matukar wajena zaki kwana na Haramta miki kara sakamin wadanan Rigunan ai ba Cinikaya zamu yi ba..Ke kinga ma sha ma Zamanki ana tabaki Ke mai cikin Haihuwa Zan D'aure nan da Wata D'aya ne kamar gobe ne.."
Yafad'a Lokaci D'aya ya juya zai Fice Daga Dakin na Bisa da kallo ina D'igar kwallah duk da ba Duka mganarsa na ji ba ammh nasan yana kushe ni  ne kamar yadda ya saba.
Har ya fita Daga Dakin ni kuma har na juya kawai naji dawowarsa da kara Kiran sunana da yayi da karfi.

"FA'IZA..!

Da Sauri na Juyo  Cikin muryata Data Fara sauyawa saboda kuka nace"Na'am..!
Kallona ya tsaya yanayi lokaci d'aya yana rike da Kofar Cikin Mamaki na yace"Kuka..?
Na Dake ki ne..?
Da Sauri na Share hawayena ina Fadin"A"ah kamar wani abu ne ya Fadamim a ido na..!"
Bai Damu ba Kafad'a ya Zakud'a kafin yace"Mama ta fada miki gidana na Abuja Zeey zata zauna..?
Kai na gyada mai bai bani Damar mgana ba yacigaba da Fadin"Fa'iza kinga barin yaran nan suna bata gidan nan Duka duka yaushe muka tare acikinsa ammh kalli yadda suka maidasa..?
Komai naki ba kula ba Lura..?
Ko da yake ke kanki abar akula Dake ne bama ki kula da wani ba Anyway dai tunda kuka lalata gidan in ma mugunta ce ke zata ci..Sai da Safe.."
Daga haka ya Sakar min kofa ya fice na Bisa da kallo hawayena  na kara cika Idanuwana ina jinsa ya Bude kofa ya shiga D'akin  yaransa ya Dade kafin naji ya Fito ya Tafi bangaransa.
Kamar wacce aka Mangara kawai sai na fashe da kuka wiwi,Sai kuma nahau Rufe Bakina,lokaci D'aya da wayata Dake samam madubin dakin ta D'auki Karan neman agaji.
Da Sauri na mike na nufi wayar kirar Kamfanin Itel karama Tunda Anum tataba Fasa min Sreen din Samsumg din da Ya Ishaq ya siya min bai kara siya min wata babbar wayar ba ya Had'ani da karama acewarsa ba amfanin ma Siyan min Shafa shafan tunda ba iyawa nayi ba, ta bakinsa Fa'iza ba turanci.
Gabana sai da ya amsa ganin wacce ke Kirana Maman Naja ce Yaya ASIYA,Sunan d'iyarta ta fari ce wacce ta rasu Naja'atu ammh dayake sunan ya riga ya bita da Maman naja ake kiranta.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA. SANNAN BASU DA BAURI MASU KIDIMARWA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*TUNTU'BI WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.




*Janafty*
*KANA NAKA...*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Fatan alheri gareki SURAYYAH DAHIRU GWARAM,Madallah da kawar arziki irin ki da karfafa Gwiwarki,Labarin nan yazo ma masu karatu Ina miki fatan alheri a koda yaushe na gaida Uwar Dakin Sa'ada da Gudiyo,sannan na ce Madallah da Uwar Dakin Yabi*🥰


            *🅿️02*

Da sauri na share Hawayena nayi kokarin daidaita yanayina domin ni Fa'iza ko Uwar data Haife ni bana kaunar taga raunina ballatana yan'uwana  da kullum suke kallona abar Tausayi wacce batayi dacen Gidan aure ba acewar su.
Saboda yanayin Raunin ji na, in aka kirani a waya a speaker nake saka ta wato amsa kuwwa yanzu din ma haka nayi na Daga kiran sannan na saka a speaker daidai Lokacin da naji muryan Ya Asiya na kiran sunana na amsa mata cikin dan D'aga murya.
Dagachan bangaran Ya Asiya tace"Fa'iza Ashe Yaya  Ishaq zai kara aure bamu sani ba..?
Fa'iza tayi wani mirmishin yak'e kafin tace"Eh Yaya Asiya zai kaara aure.."
Ya Asiya tace"Shi ne baki Fadamin ba,  kuma baki fada ma Mariya ba ko..?
Fa'iza tayi shuru batayi mgana ba Ya Asiya Haushi ya kamata ta fara Fada Tana Fadin"Kila ma baki sani ba..?
Domin sai ma an Dauke ka da Daraja da kima ne ake sanar dakai wani abun."
Da Sauri nace"Aaha nasani fa..Wlh na sani Mama ta fadamin sannan Anty Binta batagarawa itama ta fadamin."
Ya Asiya Dagachan bangaran ta jimjina kai kafin tace"Shi Uban gayyar bai Samu Fada miki ba kenan..?
Sai a bakin Uwarsa da yayarsa kike ji kenan..?
Anya Fa'iza wannan Rayuwar zata tafi ahaka kuwa..?
Shekara Takwas ai ba kwanaki Takwas bane."
Fa'iza ta share hawayenta da suka zubo mata kafin tace"Ai shima ya fadamin yau daya dawo.."
Ya Asiya tace"Umhh..!
Saboda takaici ma ta kasa mgana,Fa'iza kuma Daman ba ma'abociya mgana bace Ya Asiya Tagaji da shurun Fa'iza yasa ta katse mganar da cewa"Goggon Karofi ke Fadamin Zai yi aure yanzu muka gama waya da ita..Ita kema Fadamin Hafsatu tazo wajen ki shekaran jiya."
Fa'iza tace"Eh tazo shekaran jiya..tazo..."
Sai ta saki wanchan mganar Saboda bata son tayi Tsawo ita kanta Ya Asiya ai ta sani Fa'iza bata kaunar mganar Data Danganci Ishaq da Danginsa in ma ka matsa sai ta saka maka kuka Ajiyar rai ta sauke kafin tace"Yaushe ne Bikin..?
Fa"iza tace"Bansani ba.."
Ya Asiya tace"Allah ya kyauta zan shigo katsinar nima In nazo Duba Tamadina hala ba ma kiji bata ji Dadi ba..?
Ciwon kafafu take fama dashi."
Fa'iza tace"Naji Da Hafsatu tazo ta Fadamim."
Ya Asiya tace"Yaushe zaki leka ki Dubata ke da ke kusa ma Fa'iza yaushe Rabon ki da Dutsenmah Tun Sanda Ta madina ta kwanta asibiti an kusa shekara fa"
Fa'iza tayi shuru ta kasa mgana Saboda bata da tacewa Ishaq ne baya barinta tana son zuwa inda Mahaifiyarta take sai yace me zataje yi tana gidan wani..?
Ya'yansa bazasu je gidan wani suna Rab'e Rab'e ba.
Ya Asiya tayi  shuru yasa ta kyaleta sai ta shigo da mganar"Ina yaran nan..?
Hala sun yi barci..?
Ta amsa mata Ya Asiya tace"Shikenan Sai mun shigo zamu karisawa Tattauna ki kara Hakuri Fa'iza kowani bawa da irin tasa kaddaran..Mu Tamu kaddaran Rasuwar Baba ne itace silar Shigar mu duk Halin da muka shiga."
Fa'iza tace"Haka ne Daman ai KANA NAKA  ne Allah na nashi ne..Sannan na Allah ne Daidai."
Ya Asiya na jinjina kai tana Fadin"Hakane Fa'iza Allah ya mana mai kyau..Mu kwana Lafiya.
Fa'iza ta rakata da Fadin ta gaida yaranta Daga haka sukayi sallama Sannan na  ijiye wayar nq koma gefen gado na zauna ina mai kura ma Madubi Ido duk da ance ba kyau kallon kai a madubi in Duhu ya shiga ammh ni sai ta samu kaina da kare ma Jikinna kallo.
Tare da Fuskata ina Ayyana adadin Lokuta nawa ya Ishaq ya kalleni ya yab'a min..?
Koda yaushe cikin kusheni yake yi an samu ma bayan sun fara Tara zuru'a ya Daina jifana da kalmar Mummuna ammh kalmar Baka sai dai in yan Cin mutumcinsa basa kusa ni na sani Tazaran Dake tsakanina da Ya Ishaq kamar Tazaran kasa da Sama ne ko abaya ban taba mafarkim auran miji kamarsa ba Domin ba Tsarana ba ne, sannan ba kuma Had'i shi kanshi na san ni ba irin wacce ta Dace dashi bane Mama kofar soro kullum tana Fada min hakama Anty Binta batagarawa,To ammh Ba kai kake Tsarama kanka Rayuwa ba Allah ne Kana naka ne yana nashi kuma Tsarinsa ne akan gaba.
Na tabbata ba Domin kakkausan Bakin Baba kan Ya Ishaq ba, da Tuni bayan kasa ta shafe idonsa ya rabu dani  ya samu salama kamar yadda yake Fadi sai dai ina Ya Ishaq bazai iya Tsallaken mganar Baba ba Shiyasa har yanzu muke tare ina D'aukan dukkan cin kashi da Tozarcinsa
Bani da wani gata nan Duniya sai Ishaq shine uwaa na shine Ubana  da Duniya ta Tamadina ga yanayin yadda Rayuwa tazo mata sauran yan'uwanna ba waje daya muka tashi ba Bayan Rasuwar mahaifinmu  Raba mu akayi ni a karofi na fara Rayuwata Kafin dalili ya yanke zamanna achan Baba Kabiru ya maido ni katsina ya Damkani Hannun Mama.
Hawaye na haka suke faman zuba ban iya saka Hannuna domin na tare su  ba Saboda ko na goge su wasu ne zasu kara fitowa a irin wannam Lokacin nake samun Fitar da abunda ya dade yana Damuna,Ba bakinciki nake yi Saboda Ishaq zai kara aure ba,A'a ai daman na sani yafi shekaru yana ikararin zai auri Zab'insa Daidai da Ra'ayinsa tun kafin ma yakai haka zama a rayuwa ballatana yanzu dayake jin kansa ashi wani ne.
Sai dai abu D'aya na sani zuwan Amarya nan tozarcin danake sha sai ya Ninka wanda nake sha abaya abu daya ne naake gudu wulakanci ina tsoro da firgicin Amaryan tazo tasan duka labarina tazo tana ganina a wulakance ta goraanta min Kamar yadda Shima yasha Fadi Fa'iza ba kyau ba Turanci komai nata Total zer0 ne. ammh a raina bana mai Bakinciki don zai kara aure ai yayi ma kokari da muka kwarari wad'anan shekaru bai kara ba,sai yanzu na kuma ji Dadi da matar zatayi nesa damu ko Bakomai kazantar da baka gani ba Tsabtace akasan chan raina kuma ina da kishi Domin ina son mijina so irin wanda Duk Macetagari zata nuna ma uban ya'yanta,duk da tarin Nakasun da auran mu ya kunsa, duk da ko shi din' bai taba sona ba.
sai dai bazan barsa yayi wani Tasiri a kaina ba tunda inda Son ke da muhalli baza'a martabasa ba, zan iya Rantsuwa ko Kaffara bazan yi baa Ya Ishaq baya sona karfin Biyayyar Baba ce take Rike da igiyar auranmu.
Naso na sauya Rigar Jikina kamar yadda yace sai dai kuma Tunda yace na bar shi nasan ko da na bisa Shashensa sai ya koreni shiyasa ban bata ma kaina Lokaci ba na Haura kan gadona naa jawo Ahmad jiki na,na Rumgume sa Abu D'aya ke sanyayamin Rai ya'ya na Domin duk duniya bayan Ishaq bani da kamarsu basa san iya adadin Lokacin Dana Dauka inaa kuka ba ammh nasan Har barci ya kwasheni kukana bai Tsaya ba.
Kiran Sallar Farko na  tashi kamar yadda ya zame min  Jiki Fa'iza bata barcin Rana sannan karfe Hudun Asuba take tashi sai kuma wani Dare.
Fita nayi naje Dakin yaran na Tashi Amir da Mustapha zasu bi Babansu masallaci Bayan sun tashi na fita zuwa Dakin Hafsatu na isketa ta tashi har ta Shiga Tiolet sai na Fice su Amir ta Tsaya akansu sukayi alwala Daidai Sanda Ishaq ya fito Daga bangaransa Sanye da Jallabiya baka da Carbi Kofar Dakin yaran ya Coge duk Fadan sa bai isa yayi ma Fa'iza Fadan rashin Tarbiya da kula da yaransa ba wannan in bai Gode mata ba ai bazai Zageta ba.
Amir ne ya karisa ga Baban yana Fadin"Oyoyo Daada sannu da zuwa.."
Yafada yana rumgumesa rike sa yayi yana Shafa kansa kafin yace"Jiya na dawo lokacin kun yi barci.."
Ina musty..?
Yafada yana kallonsa Fa'iza na kiciniyar saka mai wata riga bayan ta cire mai na barci sai faman mutsike ido yake yi alamun barcin bai sake sa ba.
Dariya yayi yana kallonsa kafin ya Bude Hannunsa yana Fadin"Oya come Here..!"
Da gudu yaron ya nufessa ya Fada jikinsa yana Fadin"Daada.."
Shafa kansa yake yana jin Farimciki acikin ransa Fa'iza ya kalla Dake tashin Anum da dan karfi yace"Kyaleta mana.."
Fa'iza ta Dago tana Fadin"Suna da Hadda yau."
Yana rike hannun su Amir yace"Ai da Sauran lokaci ke komai naki na Hanzari ne karfe Biyar din Asuban ne zasu tafi Haddar..?
Bada karfi yayi mganar ba saboda Haka ban ma jisa ba nadai san yayi mgana kuma nasan bai wuce Fada ne irin nasa Daya saba ba,  shiyasa har yaja su Amir suka fice ban kara mgana ba..
Suna Fitan nayi kokarin tashin Anum Saboda tayi sallah ta wartsake kafin su Dawo Daki na muka koma Tare nima na Dauro alwala mukayi sallah Tare da Anum muna idarwa Ahmad ya tashi na Daukesa naga ya bata pampers dinsa,sai na mike na Goyasa na shiga Kitchen bayan na gargadi Anum kada ta koma barci ta zauna tayi azkar din Safe wanda yaran duk sun Haddace..
Ruwan Zafi na fara sakawa saboda nayi ma Ahmad wanka kafin sauran yaran su Dawo Sai kuma na fara kokarin Fere Doya saboda na soya musu na Tafiya dashi makaranta sai ga Hafsah ta shigo Kitchen din da Hijabinta.
Fa'iza Hankalinta na wajen aiki bata san Hafsatun ta shigo ba sai da ta tabata sannan ta dago tana kallonta kafin tace"Kin fito Hafsah..?
Da yanayin mganarta Hafsah tace"Eh Ina kwana.."
Da dan daga Sauti Saboda Fa"izan ta jita sosai.
Ta amsa mata Cikin Sakewarta Hafsah tace"Bari na amshe ki."
Fa"iza tace"A"a barin min wanan aiki..Ga dai ruwa nan na saka in ya Tafasa ki juyo ki yima Ahmad da Anum wanka kafin su Amir su dawo."
Tafada cikin yanayin Raba mganarta Hafsah ta amsa mata da Toh,ba Dadewa ruwan ya Tafasa ta Dauko wani Karamin baho ta juyo ruwan ta kai Tiolet din Dakin Fa'iza da suna da Shower na wanka ya lalace kuma ya Ishaq yace da gan gane saboda haka bazai gyara ba.
Dawowa tayi ta karbi Ahmad ta je ta fara mai wanka ta shiryasa sannan tayi ma Anum nata wanka alokacin har su Amir sun Dawo masallaci suna Falo Tare da Ya Ishaq Sanda Hafsat ta fito Dauke da Ahmad daya fara Rigima ne Fa'iza ta fito Daga Kitchen din tana gaida Ishaq ya amsa mata bai ko kalleta ba Hankalinsa na wajen Amir Dake bashi Labarin abunda ya Faru a makarantasu jiya shi kuma Musty bai da Hayaniya yana Lafe jikin Uban..
Hafsah ma tabi ayarin yar'uwanta ta gaisheshi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login