Showing 84001 words to 87000 words out of 96493 words

Chapter 29 - Kana Naka Book 1 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

222

ya mike yana Huci Lokaci d'aya yana fadin"Lalle kin fara rai na ni kin manta waye ni a wajen ki kenam? Gantalin da kika farayi na shiga makota yasa kika koyi rashin kunya da rashin Tarbiya ko..?
Sai nima na mike kai tsaye nace"Na fada maka kada kawo mganar rashin kunya a wannan muhallin saboda kai kanka kasan ba Halina ba ne yanzu ta kamane kasan wasu abubuwa.."
Cikin Hargagi ya katse ni bayan ya tasomin yana fad'in"To nace bazaki yi ba in kuma zaki nuna ban isan ba ne bismillah Fa'iza wlh sai na nuna miki Oder side of me da baki taba gani ba"
Ban bari ya sauke mganarsa ba nace"A matsayin ka na waye kake fad'in bazan yi ba..?
Yadda nayi mganar ta basa mamaki sai ya tsaya yana kallona Lokaci d'aya yana nuna kansa cikin mamaki yace"Ni ki ke fad'ama wannan mganar..?
Kai tsaye nace"Eh tambayar ka nayi a matsayinka na waye..?
Mirmishin gefen baki yayi kafin yace"Ina da matsayin yaya gareki sannan kada ki manta ni mijinki ne"
Nima mirmishin takaicin nayi kafin nace"Mijin jingina..?ko yayan da baisan Hakkin kanwarsa a kansa ba..?
Nace mijin Jingina Yaya Ishaq ka ke kira Miji..?
Mgana takara  girgizasa ban bari ya fita daga Girgizan ba na Dora da Fadin"a shari'an ce kai ba mijina ba ne yanzu.Saboda ka zabi wata matar sama dani,ka jingine aure na shekaru biyu kenan,ni matsayina kawai ina kula da ya'yan ka ne sannan in amtsayin Yaya kake mgana baka da wannan Hurumin saboda sai yaya ya zama nagarttace nagartansa zai yi yab'o har ta yab'anyan, da k'anwa bazata iya zarta da wani abu batare da yardan sa ba,Duka baka cike kowani Gurbi ba shiyasa nace isar taka bata isa wannan karon a wajena ba"
Baya ya juyamin ya kasa juyowa ya kalleni, ban damu ba sai nayi kokarin Dauke Hawayen da suka kawo idanuwana na cigaba da fadin"Tun Lokacin da ka zabi iyalan Zainab sama da ni da ya'yana.isar ka ta zama bata isa akaina ba, sannan tun alokacin na Zab'i ya'yana sama da kai,kuma tun lokacin da ka zabi Dangin zainab Sama da Dangina nima na zabi Dangina sama da naka dangin, ban ce Dole sai ka amince ba ina fad'a maka ne Dole zan fita na nema ma kaina mafita Kuma Dolenka, ka kare mganar hakan daga bakin kowa in kana gudun fallasar Jinginannen auran mu zuwa kunnuwan da bazaka so hakan ba"
Shuru yayi ya kasa juyowa ni kuma da nagama mgana sai kawai na kama Hanyar fita cikin Shakewar murya yace"ya'yana fa wazai kula da su.?
Na juyo muna kallon juna ido cikin ido kafin nace"Nima ai ya'yana ne..Ni nake kula da su Lokacin da ka zab'i zainab da ahalinta sama da su.ai a yanzu ba'a wulakance ka gansu ba, nayi alkawarin zan kula da su domin nan duniya nice gatan su nima sune karfin gwiwata da dalilan da yasa nake zaune cikin kaskantataciyar rayuwa"
Ina gama fadin haka na bude kofa na fice har nakai dakina hawaye ne ke kwaranyomin sai na zauna agefen gado na rumgume abun hannuna a saman kirjina,na fashe da kuka,a hankali a hankali kuma ina samun salama da Sauki acikin zuciya ta.
Sama na kallah nace a fili"Allah kana ji kuma ka na gani.
Ya Allah ka sama min Mafita, mafita mai amfani a rayuwata da ya'yana. ka hananin jin kunyar duniya ka bani dukkan karfi da juriyan daukan duka Jarabawowinka."


*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*..



*Janafty*
*KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Fatan alheri,ga mutane masu kirki da karamci.*

*Aisha muhammad alto(Sisinah)Sannu barka da arziki kin yi kokari da kika Haifa min D'a,Allah ya raya mana Baby boy.*
*Fatan alheri zuwa ga Khadija Salisu yusuf(Ummina)*
*Halima yusuf gwarzo(Besty) ina miki fatan alheri*
*Nana Halima(Masoyiya)ina gaishe ki Fa'iza tace na fada miki,tana kaunarki kamar yadda kike kaunarta.*
*Ina gaida Uwar biyu Mrbb,Allah ya raba lafiya*
*Sannu gwana uwar Dakin gwanaye,Feedhom nace Allah ya sa afi haka.*
*An gaida Uwar Muwaddata da Anum Ramlat Abdurrahaman Manga,Maidambu,ina godiya Allah ya saka da alheri*
*Ina miki Fatan alheri Uwar Farha Fatima miss flower(Rabin raina).*
*Sannu Amina minajo na,Fa'iza na gaida Masoyiyar asali.*
*Sannu Anty maryam,Fa'iza tace nayi miki godiya,da shawarwarki ta fara sanin cewa itama Yar Adam ce.*


*Madallah da mutane masu karamcin irin ku,Nagode sosai Allah ya bar zumunci,ya kuma had'amu a aljannah*



           *🅿️19*

Saboda Zumud'i ko fargaba zan ce, sai wajen uku saura na dare na iya samun, barci kuma cikin ikon Allah Kasala da nauyin jiki sun kasa barina na tashi na dauro alwala.
nayi salollin Nafila sai dai ina daga kwancen ban daina Hailala da ambaton Allah akan dukkan lamurana ba.
Washegari kamar yadda na saba tashi da wuri haka na tashi, na shirya yara na sama musu abun kari. sukaci sakamakon sun saba tafiya ba abinci,yau din ma haka suka tafi sai dai kamar yadda na sabar musu sai sunci sun koshi suke tafiya yadda kafin yunwa ta jigatasu, lokacin sun dawo gida sai na ba ma kowannen su Goran ruwan faro guda d'aya sun tafi da shi koda bukatar shan ruwan ya taso musu.
Suna tafiya nima ban zauna ba, na fara shiri falo kawai na gyara Dakin yara kuma nace sai na dawo nayi wankana na shirya kaina shima Ahmad na shiryasa bayan na Dama mai kokon sa. na duramai a wani karamin jug,Sauri sauri nake yin komai kada farkon fari kuma nayi latti na samu Tsoffin littafan su Amir da suka gama amfani da shi na Dauka da pencil saboda rubutu duk da ban iya Turanci ba, kuma ban iya Hausa ba, ai na iya rubutu da ajami kuma ina iya karantawa shiyasa ban damu ba.
na tabbatar ma kaina duk abunda na Rubuta zan iya ganesa.
Na hada da katin  shaidana na goya Ahmad a baya na daukan mai wasu kayan. ko da ya bata na jikinsa na fito Falo Tara saura,naci karo da Yaya Ishaq a falon yana waya kallo d'aya nayi mai ban kara ba,shi kuma ganin kamar tafiya zan yi yasa ya katse wayar Hannunsa,ta gabansa na gifta cikin yanayin mganata nace"Ina kwana.."
Ina fad'in haka na kama hanya zan fice sai ya mike jiya ya kwana yana mamakina sai da yaga abunda nayi yau sannan ya amince da gaske nake yi,sai ya saka baki ya kirani da karfi na Dakata na juyo ina kallonsa kai tsaye yace"Ina kike shirin zuwa..?
Ni kuma sai naga kamar yana batamin Lokaci sai na juya ina fadin"In da na fad'a maka jiya..Ina Sauri ne kada na makara"
Na fada ina jimke dubu d'ayan da na Dauko cikin kayana sun sha ajiya tun Kudin da Yaya Isa ya bani ne Lokacin da ya maidoni gida, Dubu buya kad'ai na Taba ukun suna na nan ina Boye da su, sai da hakan ta faru na Daga hannu nagodema Allah domin zasu yi min amfani.
Kawai sai naga ya sha gabana a matukar fusace cikin d'aga murya yace"Ni kike nuna ma ban isa dake ba Fa'iza..?
Baya naja ina fadin"Ban ce baka isa ba.Sai dai na nuna maka isar taka ce wannan karon, bazata isa a wajena ba ka bani hanya na wuce ina bata Lokacina"
Sai ya tare hanyar ni kuma sai na kasa wucewa cikin Daka tsawa yace"Ki koma nace ba inda zaki je"
Sai nayi wani kayattacen mirmishi takaici na Fahimci in na zauna haka Ishaq zai cigaba da Nakasa rayuwata kamar yadda ya saba to wannan karon ya makaro domin d'an zaki ya riga ya girma.
Sai kawai na kallesa ido cikin ido kafin nace"Sai dai kayi hakuri wannan karon bazan ji mganarka ba.Na fada maka tun Ranar da ka zabi Zainab da Ahalinta sama da ni..Nima Daga wannan ranar na zab'i Rayuwata da ya'yana sama da kai"
Mganganuna sun dake sa sai ya kasa motsi har na raba ta gefensa na wuce abuna,Kafin na fita sai da nayi addu'an fita gida,sannan na karisa gidan Sa'adatu muka gaisa na kwanto mata Ahmad Allah yasa yayi barci ta karbe sa tare da kuninsa tamin Fatan Alheri daganan na fita na samu Adaidaita sai cikin gari.
Makarantar ta yan mata ne zallah suna barayin su sannan mu kuma inda zamu zauna wani babban aji ne, ko da nazo mata sun fara taruwa sai dai ma'aikatan basu riga sun kariso ba,na gaisa da matan dake kusa dani muka zauna jiran su tara da wani abu suka iso,,Rukuni rukuni suka jeramu a layi mun nuna katin shaidarmu sannan suka sanyamu a rukunin da zamu fara koyan abunda ya kawomu.
Ni rukunin girke girken aka sanya ni shi zasu fara koyar damu sai sun gama sai ayi barayin Had'a lemuka da rana ne Rukunin Koyar da Turaren wuta da Had'a Dilka..
Sai na Fahimci da Safe duk abun ci ne zasu koyar damu shiyasa sai suka raba abun,Ni dai ban tsaya kalle kalle ba na saka ido sosai,ina Fahimtar komai masu koya mana Rukunin Farko,Su biyu ne dukkan su mata ne, Daga ganinsu sun san kan aikin su Sanye da Fararen riga da Hula na masu kirkin da muke gani a Kwatin Talabijin.
Ranar farko wainar kwai suka koya mana da miyar gyada mai allayahu,sosai na karu na kuma rubuta sunayen abubuwan da suke fad'amana bamu gane ba,Suna yi suna yi mana bayani yadda zamu fahimta sannan in baka gane ba sai kayi Tambaya komai da komai na girken girken su, sun zo da shi suka kafa karamin Dakin girki a babban D'akin da muke ciki, nayi tambaya in da naga ban gane ba.kuma sun kara yi min bayani suna da Sauki kai matuka da iya mu'amala.
Daman kuma Koyar damu ne aikin su, har kuma mh iya sun kuma tabbatar mana da cewa zamu iya girke girke masu kyau da inganci.bayan an gama dukkanmu muka D'andana mu biyar ne a rukunin Girke girken,muna ta santi saboda yayi dadi sannan da alkawarin in muka koma gida zamu gwada mu gani.
Sai rukuni na biyu Had'a lemuka,Zobo suka fara koya mana Had'ashi,Duk da na iya zobo sai naga nawa shirme ne ashe ga inda ake zobo nan,Ranar anan Rukunin ya kare shima sun bamu mun sha dad'i,Daga karshe sukace in da bamu gane ba mu yi mgana ni dai akwai karambani daman duk abunda ban ji ba sai da na tambaya suka kara gayamin,Ranar farko kawai da fara zuwana naji araina zan iya komai insha Allahu na dawo gida da Farinciki na iske Ishaq baya gidan ban Damu ba daman na fita da key da na ga ya Kulle gidan sai na bude bayan na Biya na Dauko Ahmad.
Ko girki ban yi ba Dakunan kawai na gyara na share, Lokaci yayi na makara ma a rukunin Rana sai d'aya da Rabi na isa har an fara an raba mutane kowa da Rukuninsa sai da na nuna Katina sannan aka kaini Rukuni na,Abu na farko da suka fara koya mana yadda zamu had'a Turaran kamshi na Icce ne ranar shi mukayi har aka tashi,shima in da bamu gane ba suna bamu ikon Tambaya in da kuma zaka manta sai ka Rubuta na dawo gida karfe hudu da Rabi na yammah na biya gidan Sa'adatu na kara dauko Ahmad sallah kawai nayi na shiga kitchen Saboda yan makaranta suna hanyar Dawowa.
Duk da na gaji ammh ban damu in dai aikin wahala ne na saba shi kuma ya zame min jiki,sai da nayi wanka sannan naji dadin jikina Yara suka dawo makaranta da yammah suna ta Tambayan Daadan su nace ya fita bansani ba,ko saboda abun da ya faru ne sai da yaran suka gaji da jiran sa, suka kwanta sannan ya Dawo ina Falo ina Tattara kayan da suka zubar daya shigo nayi mai sannu da zuwa bai amsani ba sannan bai kalleni ba. ya shige bangaransa a raina nace ko nace a banza.
Washegari ma ya rigani fita,Nima ko Lokaci nayi na yi tafiyata kamar jiya,Sai dai na Fahimce zan rika shan wahala in dai ina jeka ka dawo sai na yanke shawaran in mukayi sati uku, zan fara zama achan sai mun gama Rukunin rana sannan zan dawo gida gabadaya kud'ina kada su kare wajen adaidaita na rasa mafita.
Yaya Ishaq kuma tun daga wannan sa'insan tsakanin mu mgana bata kara Hadamu ba, ni dai ina fita Hakkinsa in mun had'u ina gaishesa shine baya amsani duka duka kwana Hud'u yayi ya koma ko sallama bai yi min ba. ganewar ma da nayi bai kwana agidan ba nasan duk tsanaani in dai yana gari to zai kwana agidansa.nima ko na tattarasa na watsar domin da gaske nake yi na zabi Rayuwata da Rayuwar ya'yana sama da tashi Rayuwar.
Na cigaba da zuwa wajen koyon sana'o'i na hankalina kwance kusan indai akace wannan abun shi kad'ai ne Hope din ka da Fatan ka to gabad'aya Tunanin ka da Rayuwarka zaka Dorasa akansa ne,ya kuke gani in hakan ta faru da mace irina da daman jiran mafita take yi..?to kamar misalin nice Domin na maida gabad'aya Hankalina da natsuwata kan abunda nake koya,Shiyasa duk nafi kowa ganewa a Duka Rukunina tun bamu Rufe wata ba Ma'aikatan suke yaba hazakata da Kokarina,Gashi abubuwa Hudu nake koya ammh kwakwalwata tana Daukan abubuwa dadama. sannan ina gane duk abunda aka koya mana.
Muna rufe wata d'aya da Farawa na koma ina zuwa sau d'aya in na tafi sai Hudu nake dawawo saboda in aka tashi Rukunin Safe sai na zauna sai Rukunin yammah Tunda ma'aikatan suna nan suma ka'ida sai Hudu na yammah suma suke tashi, duk abunda muke yi suna daukan komai sannan suna Rubutawa saboda suna turama kungiyar Bayanan komai.
Yau da gobe zara bata bar komai ba kudin hannuna suka kare sai na koma takawa da kafata yara na fita makaranta nake fita da nisa sosai kafin na kai na jigata ammh hakan nake Daurewa na sama kaina yakinin ba wanda ya isa ko ya samu yana kwance, sai da ya fita ya wahala,Muna Hutu Ranar jumma'a duk sati sau Shidda kenan to ranar ne nake samun na gyara gida, har yi ma yara wanki da Sauran aikace aikace ni kaina nasan na Rame saboda wahala.
Badariya sai da muka raba rabin watanninmu sannan tazo gida ranar wata jumma'a muka hadu a bakinta nake jin Anty Binta tazo sau biyu bana gida ta je ta fad'ama Mama sai Fada take,Tana fadamin Maman ta kira Yaya Ishaq din tamai mgana ba'a san me ya fada mata ba,basu kara mganar ba,Badariya tace ita dai tayi gum da bakinta bata tofa ba, tana ji Mama na fad'an na fara gantalin bin gidajen makota.nayi dariya nace gwara da kika yi shuru baki ce musu komai ba.
Araina naji mamaki ban Dauka Yaya Ishaq zai yi Laushi ba ni dai abunda na sani bazan zauna Damar da na Dade ina jiranta ta Kubcemin ba,Bandamu domin ba ta su nake ba ta kaina nake da ni da ya'yana. Badariya taji dadin yadda na fadamata muna koyan abubuwa da Dadama,sannan wahalata ta ragu saboda Sa'adatu ta Daukemin Laluran Ahmad sai abun yazomin da Sauki,Ban gayama kowa ba So nake ko yan Karofi na basu mamaki Fata na da Dakiyata azabeni cikin mutanen goman da za'a basu tallafi saboda zai yi min matukar amfani.
Yadda Yaya Ishaq ya tattarani da ni da ya'yana gefe d'aya.haka nima na tatrarasa na watsar Sai dai ya'yansa ban isa na cire musu tunaninsu akan sa ba,ko bakomai mahaifin su ne,ya zama Dolen su ni kuma ko da yake mijina ai ba Dole na ba ne,Na riga na jigata da tafiyar kasan da nake yi ammh ban ji ko sau d'aya na gaza ba nayi fashi sau Biyu shima Ahmad ne yayi ta zazzabi ba Halin na fita na bar shi kuma zuwa da yara an hana, shiyasa na zauna na Kula da shi har yaji sauki muna gabda cinye wattani ukun mu,Badariya ta dawo wajena da kwana ashe Mama da Anty Binta Abuja sukaje sulhu Zainab ta samu ciki sai suka yi sa'insa da Ishaq akan Farhan bai yi kwari ba, zata zubar da cikin shi kuma ya hana ita kuma sai ta Ture mganarsa ta yi mgana da mahaifinta yace ta zubar, tako je aka markadesa shine rigima ta kai su ga Har Ishaq din ya mari zainab din ai ko Badariya tace Mahaifinta ya Kira Mama yana fadin Ishaq ya gama marin auransa kuma sai yayi mganinsa sai ya yi kararsa a kotu,Ai ba jaka ya aura masa ba.shine Mama ta rud'e ta yi ma Anty Binta mgana ta rakata suka tafi Abuja su sulhunta mganar.
A raina sai nace tun yanzu..? Auran barikin fa kenan,ai na Dauka ko me zainab tayi Yaya Ishaq zai yi hakuri da ita,tunda ita yar so ne kuma ita ya zaba ban dai nuna komai ba nayi fatan Allah ya Daidaita su Saboda ni bazan yi Dariya don haka ta faru ba Namiji ai duk inda yake yana amsa sunan sa na Namiji ne.
Wajen kwananta hud'u a gida na sannan su Mama suka dawo, sai ta koma gida Saboda harkan gabana nake yi yasa ban damu da na Bibiya ya suka kare ba,Nidai bana fatan tun yanzu auran su ya samu matsala ina Fatan su tara kyakyawan zuru'an da Yaya Ishaq yake mafarki da fata ko zai daina kallona a matsayin wacce ta zama Sillar shiga tsakaninsa da mafarkinsa da Burinsa.
Mun cigaba da zuwa muna koyan abubuwan da ake koya mana har ga shi yau da gobe bata bar komai ba zamu kammalah,Watanni uku kamar kwana uku ne a wajen Ubangijinmu,Ranar jumma'a muna Hutu asabar zamu gama gabad'aya ranar Lahadi kuma za'a sallame mu da Takardan shaidar abunda muka koya, a kuma wajen za'a bama wad'anda suka chanchanta tallafi.
Ranar jumma'an ina gida tunda bama zuwa ranar Sai ga Badariya da Raliya sun zo min da labari mai dadi bayan mun gaisa na kawo musu ruwa su Amir suna haraban gida suna waasa.
Raliya ta kalleni tana fadin"Anty Fa'iza ina tayaki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login