Showing 24001 words to 27000 words out of 96493 words
ya mllaka ya siya mama nata,Budi ta ko'ona sai hamdala da Godiya yana Dinkamin suturu daidai gwargwardo sai dai na yaransa Dabam suke,Ni wani Lokacin ko yayi niyar yimin Rantsatsun kaya sai kalaman Mama su Dishe niyyarsa tunda tasha fadin siyamin kaya na alfarma barnan kudi ne, Tunda ba kyau zasu yi min ba sannan bansan yadda ma ake gayun ba kuma gaskiya suka fada ba karya sukayi ba ban san komai na gayu ba.
Ni dai iyakata nayi wanka na shafa mai na saka kaya,Abaya telan su mama ke min dinki Mama ta koma ba wata mace saboda sai nace yana kamani ni kuma bana so kaya su kamani na fison a shatamin na rika yawo aciki,ya Mariya ko Ya Asiya ko da wani Lokaci suna kokarin gyarani ni ko bana jin su gani nake yi gyara da gayu na wajen mata masu kyau da gata ban da ni da bani da ko d'aya daga ciki Dalilin dayasa Ya Ishaq yake Biye ma Mama kenan in ta fadi mgana hakan take indai a kaina ne ballatana ba ran Baba ita ke tafiyar da komai.
Mama ta bada shawaran nayi Tsarin iyali sai dai bai karbeni ba wannan yar ashanan aka sakamin ya sakarmin jini Dole aka ciremin ana ko Ciremin ko wata Biyar ban yi ba na Samu Cikin Ahmad,na haife su kusa da kusa domin a shekara ta takwas da auran mu da Ya Ishaq duka na Haifesu haihuwan gwarne na rika yi don ma Allah yasa ina da jarumta daukan duka kwarmiyan yaran
Cikin ikon Allah cikin ya'yana ba wanda ya Dauko Lalurata sai na godema Allah Ammh wani ikon Allah susan Lalurata barin ma Anum da Amir susan bana ji sosai in zasu yi min mgana sai sun daga muryansu.
Allah ya bani yara masu kirniya,musty Da Amun basa jin mgana komai suka gani sai sun taba abunga ga wanda bai da karfin ji ina chan ina aiki su kuma suna Falo suna barna bana sani kuma Duk abunda suka Lalata sai Ya Ishaq ya dora komai akaina,Shiyasa ya dinga masifan na bari duk sun bata gidan sun bata kayan kallo sun bata in ji min wanki kuma Mama sai tace bazai kara siya ba, a kyaleni na wahala ai da gangan na bari suka bata komai.
Ni kuma bana cewa komai,Saboda bani da wani zabi,Har zuwa yanzu da girma ya kamani da ya'yana ban daina samun tozarcin Wajen Mama da Anty binta ba tun ba'a sani ba har kowa ya sani,Goggo karofi dai hakuri take bani,in ta kirani a waya sai dai fa ta wayan ammh Sai na shekara kafata bata taka Karofi ba Tunda nayi aure Sau Daya naje naga Tamadina Shima Haihuwan Mustapah ne da naje karofi da Ya Ishaq yaji Labari masifa ya farayi wai baya son ya'yansa suna zuwa gidan wasu suna Rabe rabe.
Haka nan nake daga ni sai ya'yana sai Danginsa alhalin yasan bana jin Dadin su ammh ni nawa yan'uwan sai dai zumunci ta waya ya rabani da kowa nawa.Hafsatu ce kawai tana ta da Kulafucin yan'uwana bai da yarda zai yi da ita in sun samu Hutu tana zuwa ta zauna dani hakan sai yasa na Shaku da ita fiye da su Yaya Asiya.
Nasan Tabbas Ya Ishaq zai kara aure watarana ban daukesa alokacin da najisa ba Nima abakin Anty Binta na farajin mganar auran sannan Mama ta Fadamin nasan bani da wata Daraja a wajen ya Ishaq ammh na Dauka zan ci albarkacin ya'ya ashe bani da wannan alfarman na Kunshi Bakinciki Tundaga ranar farko da na wayi gari agidan Ya Ishaq a matsayin matarsa,Na kunshi takaici a matsayina na Uwar ya'yansa na fuskanci Tozarci a matsayina na kanwarsa tun a baya to wani tozarci ne ni Fa'iza da ya rage ban gani ba..?
Nayi Rayuwar aure shekaru Takwas da wani abu ammh Daidai da Rana d'aya ban Taba Danda'na yadda Dadin aure yake ba na dai yi shekaru Takwas ina Sanin yaya matsayin Tozarci da Gori yake sannan na kara zama Guilt akan kushen Hallita da kuma aibata Nakasa ta nayi rayuwa cikin Guilt din jin ban da sa'a na rayu cikin Guilt din Sannin ni bani da gata na zauna cikin Tunanin Mata ire ire na basu dace da suyi Farinciki ba.
Basu chanchanci miji mai kirki ba, basu chanchanci samun soyayyar ko wani Namiji ba,Sannan basu chanchanci Rayuwar Farimciki ba.
Mata ire irena Rayuwar kaskanci da Torzarci da Bauta ya dace damu,Ba kokarin mu goga kafad'a da kafad'a da mata masu kyau da gata ba shi yasa na Rayu cikin Tunanin kayan alfarma da shigar alfaarma da Kwalliya basu dace da ni ba, sun fi dacewa da mata masu kyau da Nagarta kamar yadda Ya Ishaq da mama ko Anty Binta ke yawan fadi akaina.
Tabbas na aminta da duka zencen su da Tunaninsu"
*Littafin KANA NAKA book 1 free ne book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Janafty*
*KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*
*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.
*🅿️06*
Filon da nake kwance akai sai da ya jike saboda hawayena,na kara birginawa ta b'arayin hannun haguna domin hannuna na dama yayi min Tsami sai naji kamar na Danne Gefen Kafafun Ahmad dake kwace gefena da Sauri na mike ina kara gyara mai kwanciyarsa barci yake yi hankalinsa kwance domin akwai haske acikin dakin ban riga na kashe ba ina kallonsa ne ammh a kasan zuciyata fad'i nake shi kam ya huta bai san duk wasu walhalhalun duniya da tashin Hankalin dake cikinta ba.
Hawayena har suna d'iga saman cikinsa nayi saurin matsawa ina sharesu da duka hannayena kafafuwna na zuro kasa kafin na dukar da kai na haka kurun nake jin kamar na yi ta rusa kuka da dukkan karfi na,na Dad'e ina so nayi kuka da karfi ammh bansan Kafad'an da kirjin da zan kwanta na rera kuka a lallasheni ba kawai sai na durkushe saman Dadad'den Cafet din dake cikin bedroom dina na fashe da wani marayan kuka hannayena duka biyu na tallafe fuskata da su wani irin kuka ne dake fitar da karar sauti cikin Yanayin da ni ke ciki.
Meyasa zan damu don Ya Ishaq yace zai jingine aure na dashi..?
Na dauki tsawon Lokaci daman ina jiran ranar da zai auro zab'insa na yi tunanin zan fuskanci tozarci ninki ba ninkin wanda nake karba a wajensa da wajen su Mama ammh bantab'a Tunanin zan fuskancin irin wannan cin Fuskar ba duk da nasan kalaman Baba sune suka yi ma wannan auran nawa tsakani da Ishaq sarka ba domin haka ba Tuni ban kawo lokacin nan acikin gidan sa ba.
Menene laifina domin na kasance a yadda Allah yake fatan ya ganni..?
Nayi kuka,kukan da ban taba irin sa ba Tun bayan da abubuwan suka fara zame min jiki sai dai wannan kukan nawa ya sha bambam da na kowani Lokaci na yau ina kukan yadda Rayuwata zata kare ne ni da ya'yana.
Kwarin gwiwa naji yana shigana irin wanda ban taba ji ba alokacin da wata zuciya ta tunasar dani ni uwace ina da ya'ya bai kamata na zama mai Rauni ba in na Raunana ya'yana suma zasu Raunana in na karfafa nima watarana ya'yana zasu zama karfafa.
Nasan Rad'ad'in maraici daga na uba har na uwa Tamadina tana raye ammh ban san Dad'inta ba,bayan Laluranta kaddara tazo ta raba tsakanimu da ita gwara ko wa dani Domin ni kam Ya ishaq ya rabani da kowa nawa ciki da har da uwar data Haifeni.
In ni nayi maraici ya'yana bazan bari su yi wannan maraicin ba, zan zame musu komai a wannan rayuwar zan zauna na basu tarbiya sannan na zama Tsani wajen inganta rayuwarsu domin sune Duniyata a yanzu bani da kowa daga Allah sai su sai yan'uwana.
Kamar kiftawan ido naji kukana ya Dauke na kurama Bangon Dakina ido ina Lissafin yadda zan fara gudanar da Sabuwar rayuwar da kaddara ta kara Budemin.
Abaya komai lalacewar aure na da Ya Ishaq bai furta zai jingine ni ba ammh ayau ya furta kuma alama ce ta angaji dakai ana neman maraba dakai,ni ba jahila bace ta bangaran addini nasan menene ma'anar Jingina amusulunci,Nasan zai kula da ya'yansa Saboda Dolensa ammh a yanzu ni ban zama Dolensa ba ya zama Dole na sama ma kaina mafita mafitar rike kaina tsayawa ga kafafuwa na ba saboda kaina ba sai Saboda in inganta rayuwar ya'yana anan gaba.
Ji nayi wani irin karsashin gwarin gwiwa na kara shiga har cikin Tsokar jikina,Hawayena na share kafin na yunkura na mike,Fuskata nake ta faman gogewa araina ina nanata sunan Allah,Afili na furta"Tunda ka bukaci hakan ya ishaq zan yi maka hakan kamar yadda ka fad'a domin rama alheri da Baba yayi min..Sannan kamar yadda nayi maka alkawari babu wanda zai ji wannan mganar indai daga bakina ne sai dai daga bakin ka da ikon Allah zan zama Jajirtattaciya uwa ba domin na karfafa kaina ba sai domin na inganta Rayuwar ya'yana anan gaba"
Daga haka na fara laluban wayata dake saman madubin Dakin,Na dannata naga 1pm na dare ta wuce biyu saura,sauke wayar nayi nan saman madubin dakin nawa na Tura kofar Tiolet na shiga na dauro alwala nafito nazo na shimfida Darduma na Fara Nafilar da tazame min jiki duk daare na saka yakinin araina Bayan kowani Tsanani Allah na samar ma da bayin sa masu hakuri Sauka'kawa
Abaya in nayi sallolina na cikin Dare ina addu'ar Allah ya shiryamin yarana,ya saka musu tausayin junansu aransu,ya inganta goben su ya saka musu albarka acikin karatun su,Sannan na kan roki Allah ya sausauta zuciyar Ya Ishaq a kaina Ya sa ka Mama tasoni ta kaunaceni,ammh daga daran yau sai na sauya alakar addu'ata na roki Allah ya bani karfin gwiwa ya ciremin rauni da karaya yasa na tsaya nayi tsawon rai da zan zama Bango abun jigina wajen ya'yana na roki Allah da kyawawan sunayensa Chasa'in da tara akan ya tayani Tarbiyan y'ayana ya kular min da su ya zama gatansu ya tausaya musu ya shiryamin su duniya da Lahira yasa su zama abun alfaharin al'umma da musulaimai gabadaya.
Ban kwamta ba sai wajajen karfe uku na Dare,shima Ahmad ne ya farka da kuka na isa garesa na Daukesa na Fara Lallashinsa ganin yaki daina kuka sai na bashi Nono yana kamawa sai shuru ashe yunwa ce yana koshi sai barci,Garin nima na shimfid'ar da shi sai barci ya kwasheni sai jin Mganar Hafsatu nayi a kaina tana ta kiran sunana Lokaci d'aya tana Buga kafafuwana..
Firgigit din da nayi na farka sai da Ahmad dake rumgume dani ya farka shima a tsorace sai ya fashe da kuka mikewa nayi ina mika Sosai Hafsatu kuma na Tsaye a kaina ita ta D'auki Ahmad tana fadin"Kai sarkin kuka ai garin ka ya waye"
Sama sama na jita mikewa nayi a kasalance,na sauko daga kan gadon cikin yanayin mganata nace"Lokacin sallah ya yi ne..?
Tana zama gefen gadon da Ahmad a Hannunta tace"Eh har su Ya Ishaq sun tafi masallaci da su Amir yau kin makara"
Da karfi tayi mganar shiyasa na jita idanuwana na mutsike bina da kallo tayi lokaci d'aya tana nazarina kofar Tiolet na Tura na shige na rufo alwala nayi a gurguje na fito na iske tana cire ma Ahmad Pampers naji tana fadin bai ma yi komai aciki ba.
Ina kokarin Tada sallah domin har na sanya Hijabi na juya ina kallonta Lokaci daya ina fadin"Ha..Hafsatu..Kin yi sallar ne..?
Kai tsaye tace"ina Hutu dame zan taimaka miki kafin ki idar da sallar..?
Shuru nayi ina nazarin abunda zasu tafi da shi makaranta babu cefane komai ya kare hatta lemun yaran da Biskit sai kawai cikin yanayina nace mata"Babu indomie ta kare dafa musu farar shinkafa ki yi musu amfani da miyar nan"
Da toh ta amsa min ta fice Dauke da Ahmad ni kuma na tada sallah sai da nayi raka'atul fijir sannan nayi sallar asuba ina cikin azkar sai ga Anum ta shigo da karamin hijabinta alamun itama tayi sallan ne bayana ta D'ane tana fadin"Umma ina kwana"
Yaran sun san raunin jina in zasu yi min mgana sai sun daga murya musamman Anun da Amir.
Mirmishi na saki na saka hannu na Jawota gabana, na zaunar da ita ina Fadin"Ina kwana Anum d'ita"
Lokaci d'aya ina jan kumatun ta Anum irin yaran nan ne masu yawon tsiya in suna mgana sai ka zata ana gaya musu ne.
Kuri tayi min da ido ni kuma hankalina na kan littafin azkar din dake Hannuna ina karantawa sai ji nayi kamar daga sama tace"Umma kuka kika yi ko..?
Waya dake ki..?
Ban ji mamakinta ba sanin Halinta da Sauri nace"A'a wani kwaro ne ya fadamin a ido Anum."
Da Sauri ta bata rai kafin tace"ko Daada ne ya yi miki Fad'a?
Shuru nayi ina bin ta da kallo yarinya ce yar shekara biyar da wannan mganar ina laluban amsan da zan bata sai ga su Amir sun shigo yana rike da Hannun Musty dukkan su jikina suka fada Amir dai gefe yayi agabana kusa da Anum yazauna Musty daman akwai son jiki shi ya lafeni sai na rike sa ina jin wani Farinciki in na Tuna nima uwace ina da iyalaina da zasu iya zama abun alfaharina watarana.
Amir ne ya daga murya yana fadin"Ina kwana Umma"
Na amsa masa ina shafa kansa Musty ma da gwarancinsa ya gaisheni na amsa ina Dariya zama na gyara ina Fadin"Kun yi azkar din Safe..?
Amir yace"Umma Daada bai barmu mun yi a masallaci ba ana ta kiran sa a waya sai muka dawo gida"
Amir da kasafai ya cika mgana ba, sai in yaga dama,ban ce komai ba sai na kauce mganar nace su karanta azkar din su na Safe kafin Lokacin wanka yayi.
Nan suka zauna gabana suna karantawa in da suka yi kuskure sai na gyyara musu har Musty da bai gama iya mgana ba yana ta garancinsa.
Muna cikin Hakane Hafsatu ta shigo tace ruwan wankan su yayi zafi sai nace ta bari zan yi musu wankan ita taji da abun karyawan su.
Ko kafin bakwai na Safe gabadayan su sun shirya cikin Uniform din Tahfeeez din su,Babansu ban gan shi ba Domin tun jiyan nan bamu sake had'uwa ba.
Farar taliyar Hafsatu ta dafa musu sukaci da Sauran miyan jajjagen da nakedashi,Sauran kuma nace ta saka musu a basket din su babu lemo ko Biskit sai kawai nace ta dura musu aruwa a gororin su.
Suna zaune afalon suna cin abincin ni kuma ina gyara ma Anum littafanta da ta wargazasu,Ahmad na bayan Hafsatu yayi barci tun da yaji Ruwan zafi ni ban yi wanka ba Hijabin da nayi sallah ne dogo ajikina.
Hafsah na Durkushe gaban Musty ta na bashi abinci abaki Anum sai ta rika Sako hannu tana d'ibar masa abincin sa da karamin Fork din su farare na cin abinci shi kuma sai ya fashe da kuka daman duk ya fisu Rigima.
Hafsah ta gaji da mgana ta kai ma Anum Rankwashi akai tana Fadin"Babbar banza wacce bata san kaninta ba"
Ni ban jin me suke fadi ina dai kallon su Lokaci bayan Lokaci ina Mirmishi sai kukan Anum naji kamar wacce ake yankata na saki littafin Hannuna na mike a firgice da yanayin mganata na fara tambayan Hafsah me ya faru Hararan Anum tayi kafin ta fara min bayani ta karishe da fadin"Anty Fa'iza rankwashinta fa kawai nayi shine ta wani yanka mana ihu kamar ana yankata in baki ma mutane shuru ba sai na bige ki yanzu nan"
"Karki kara dukar min yarinya kada ki Sake Hafsah.."
Kamar daga sama domin mu dai bamu san fitowarsa daga shashensa ba dagani har Hafsa mun ji mganarsa Saboda a kausashe yayi maganarsa,Da sauri dukkanmu muka juya muna kallonsa yana sanye da Jallabiya mai ruwan madara Kansa ba Hula fuskar nan nasa kamar ko yaushe a had'e,Anum na ganinsa ta tashi da gudu ta nufesa lokaci d'aya ta fad'a jikinsa cikin sangarta da shagwaban da ya bani mamaki tace"Daada kaga Anty Hafsah ta Dake ni ko..?
Riketa yayi Lokaci d'aya yasa ka hannu ya Dagota ya riketa a hannunsa ya Tako falon duka yaran suka mike suka bar abincin gabansu suka nufesa suna fadin"Daada.."
Zama yayi kan daya daga cikin kujurun falon yana Daga musty shima ya Daurashi kan cinyarsa Amir ne kawai ke tsaye a gabansa.
Kansu ya Shafa gabadayan su yana Fadin"Eyee..Ya'yan Daada yan makaranta..Mutsy me kaci haka bakin ka duk maiko.?
Da yanayin mganarsa yace"Chaliya"
Dariya yayi yana kwaikwayonsa Hafsah ce ta rankwafa ta gaisheshi ya amsa yana wani had'e rai nima na gaisheshi ya amsa a Dakile.
Kallonta yayi kafin yace"Hafsah ba na so ana dukan min ya'yana..Bana so..Har nawa Anum take da zaki dake ta.?
Hafsah mamaki ya kamata cikin mamakin tace"Rankwashin ta kad'an nayi akai kuma musty take sawa kuka"
Kai tsaye yace"Nace dai bana so kiyaye Ok"
Kai ta dagamai cikin wani yanayi kafin ta Dago ta kalleni sai naji wani iri araina ashe Ni ma kenan bazan iya Hukunta Anum ba tunda Hafsah ai kanwatace,Ahmad ya tambaya tace gashi a bayanta yayi barci daganan ta shige Daki jikinta duk ba Dad'i sai naji ban ji dadi ba sama sama nake ji yana Hira da ya'yansa ni kuma ina Had'a musu jakunkunansu waje daya na shiga kitchen na fito musu da Baskets din su guda uku nazo na ijiye ina Fadin"Anun Amir Musty kowa yazo ya Dauki jakarsa da abincinsa"
Amir da yazo ya Dauki nasa na taimaka masa ya rataya jakarsa,Anum kuma sai ta fara rigiman ba Biskit ba lemu.
Ya ishaq ya Dago yana kallona ni kuma kawai sai na Dauke