Showing 57001 words to 60000 words out of 96493 words

Chapter 20 - Kana Naka Book 1 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

219

wanda ya Dakeni kuka kawai nake yi"
Zai yi mgana na girgizamai kawai ina Hawaye Ya ishaq sai jikinsa yayi sanyi Mama kuwa komawa tayi ta zauna tana Fadin"Yau naga makirci"
Anty Binta sai ta kasa mgana na mike na isa ga kayana na ina Tattarawa Amir da Anum suka tayani muka kwashe na Dauki Musty na Sabashi a baya na rike ma su Amir Hannu ban kara kallon barayin su Mama ba na koma D'akina ammh kuka na bai Tsaya ba.
Anum sai fadi take yi "Umma Daada ne ya Dake ki..?
Da Sauri nace"Ba wanda ya Dakeni Anum..ban da lafiya ne"
Amir da yayi shuru yace"Umma Anty Binta naga ta na dukan ki"
Da Sauri nace"A'a bata Dakeni ba..Hakuri take bani sanda kuka shigo"
Daga gani basu yarda ba Domin suna kallona suna kuma kallon junan su,Amir shi ya tayani na maida kayana cikin Wadrope Ranar tare na kwana da ya'yana acikin D'aki Daga ni har su bamu kara lekawa falo ba bansan Lokacin da su Mama suka tafi ba sannan abinci ma ban yi ba,nace zasu sha gari sukace basajin yunwa nima cikina duk ya toshe bana jin cin komai bakina kamar madaciya.
Washegari kuma Ban sani ba Ya Ishaq ya koma Abuja sai da naga an yini an kwana ban gansa ba nasan ya tafi kenan hadda kuma kwana Biyu su Amir basu samu zuwa ba sai Ranar Lititi suka tafi makaranta Lokacin an gyara adaidaitan Haruna.
Duk da bani da Tabbacin Yaya mariya ta fadama goggo abunda ya faru ammh duk sanda na Tuna abun sai naji ba Dadi,Satin Ahmad hudu A karofi Hafsatu ta Dawo min dashi nasha jinin jikina kila Yaya mariya ta sanar da su komai nayi nayi ta tsaya ta kwana tace Goggo tace kada ta zauna an had'ama Ahmad sha tara na arziki su goldemorn da su Madaran yara,kayan Tea har da Ferfesun kaza sai garin kuni da garin danwake Hafsatu sallah kawai tayi ta juya,ko awa daya batayi ba Daganan sai jikina ya karayin sanyi Ahmad yayi kiba sosai Tafiyarsa har ta fara nuna yana Gudunsa ko'ina sai naji Dadin haka acikin raina duk da bana jin kewarsa Domin na maido Anum wajena take kwana ammh shakuwar dake tsakanin Uwa da abunda ta Haifa Allah kad'ai yasanta.
Ko wata Biyu ba'a rufe da Faruwar lamarin da ya faru ba Zainab ta Haihu Namiji nima ba wanda ya Fad'amin Halisan Anty Mamah suka zo anguwanmu ita da Badariya Daga makaranta suka biyo,Shine naji suna Hirar kuma Badariyan ta tambayeni ko naji nace ban sani ba.
Nan take shaidamin shekaranjiya akayi Haihuwan Zainab ta samu Namiji C.S akayi mata Su mama kamar yanzu aka fara samin jika ta nan tana shirin gagarumin Taro sannan Anty Binta kuma tana ta shirya Mutanen da za'a tafi da su Abuja suna.
Ni dai ban ce komai ba,ammh a raina na ma Zainab fatan samun Lafiya da kuma raya abunda ta Haifa bana mata bakinciki Domin ni ban Dauketa a kishiya ba sai miji na sonka ne zai kara aure ka damu kanka, in ka san baka da wani Daraja babu abunda zai Dameka.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.


*Janafty*
*KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

      
           *🅿️13*

Babu wanda ya damu dani ballatana su fad'amin haihuwar zainab d'in, ba domin naji a bakin badariya ba kila har sai in mun hadu na ganta da yaro a hannunta,Ya ishaq tunda ya koma ban kara jinsa ba,Su mama kuma da ni da babu a wajen su duk d'aya ne,
Baza su damu da naji komai,ta bangaran su ba Shi kan shi Uban gayyar ai bai Damu ba,Domin na tabbatar ma kaina da ni da banza duk d'aya muke a wajensa in ya saka kafa ya koma Abuja ina da yakinin baya tunawa dani ballatana ya neme ni ko a waya na Zargin hakan ne,saboda bai taba tambaya ta daidai da rana d'aya da cewa Fa'iza ina wayar ki ba..?
Ko na ji ina kiran wayarki a kashe me ya faru..?Bai taba min makamanciyar wannan tambayar ba sai na sakama raina bai taba kirana yaji bai sameni ba,Ballatana yasan wayata ta lalace.
Na riga na saka ma raina mata ire ire na ba su da wani muhimmanci,na amince ba ni da kyau sannan ba ni da wani gata ballatana nasaba,Ammh ni musulma ce sannan Allah ne ya Halliceni,a yadda yaso ya ganni,ban taba jin kunyar yadda Allah ya Hallice ba Saboda nasan bai fi son masu gatan a kaina ba nasan duka Bayi muke a wajensa kuma mun zo duniya ne domin bautar ubangiji.
Na kuna riga na sakama raina ba sai na samu soyayyar miji ba,sannan ba kima sai na zama wata aba mai Daraja ba ni dai ya kasan ce watarana  zan zama bango ga ya'yana shikenan Burina ya cika bani da wata Damuwa Ban matsa ma kaina sai su Mama sun so ni Dole ba domin akwai mutanen da ko Naman jikinka ka ke yankawa ka na basu suna Dafawa baza su taba sonka ba sai na sakama raina haka,Sannan nasan ba ni da abunda zasu kaunace ballatana na saka watarana komai zai zama Tarihi.
Ban san ma ba'ayi suna ba ashe an kara Sati d'aya kafin taron suna ana gobe sunan Badariya ta zo take fadamin Sakom Mama akan na shirya su Amir da kayansu na kwana Biyu zata tafi da su,Baban su yace a taho da su ban yi musu ba na tashi na Shirya musu kayan su masu kyau Amir da Musty da Anum Ahmad kuma ya cika Rigima daman su ukun Mama tace za'a tafi dasu sai da ta jira suka Dawo daga makaranta jin zasu Abuja wajen Daada Anum da Musty suka fara Tsalle Amir ne ya kalleni yana kwabe Fuska Lokaci daya yana fadin"Umma ni bana son zuwa a bar ni a gida"
Sai na kallesa Badariya Hankalinta yayi gaba kan wayarta sai bata ji sa ba na jawosa jikina ina Fadin"Haba Baban katsina wajen Daadan ku zaku je da Anty ku fa..?ba kwa so kaga Sabon kanin ku da Anty ta Haifa muku..?
Sai ya gyad'a min kai alamun yana so kumatunsa na shafa ina Fadin"To kada ka kara cewa bakason zuwa..Kai ma zaka je ka ga Sabon kanin ku ko Amir di na..?
Sai yayi dariyan su na yara kafin yace"Umma ke bazaki je ba..?
Kai na girgiza kafin nace"Zan zo ammh Daga baya kaji ko..?
Sai ya jinjina min kai,mganar da nayi mai yasa ya shiga cikin kannensa suna Murna sai da suka yi sallar mangariba suka ci Faten Ramar da nayi ina da Tsakin tun wanda Goggo ta kawomin ne yayi saura Gidan Sa'adatu na shiga na samu Rama dayake suna da Fili tayi shukeshuke har da su Zogale yanzu na fahimci mutane sune Rahma ina shiga makota na bayan kwana Biyu mu gaisa nima Sa'adatu da Habiba sukan lekoni Lokaci bayan Lokaci sai hakan yake min Dad'i ko da ba na ganin wani nawa a kusa dani Su din da nake gani sai suka Debemin kaso mai yawa na kewar da nayi shekaru yana Damuna.
Sai da su Amir suka tafi naji gidan yayi min shuru Kuka sosai Ahmad ya yi da yaga yan'uwan zasu tafi sai da na Shige da shi daki sannan suka samu Tafiya,Dakyar na samu yayi barci ballatana daman Ahmad akwai rigima irin goyon da nayi Anum ne itama akwai Rigima kuma har yanzu bata Daina ba tana tabawa wani Lokacin don ma ina had'a mata da Nasiha sai take rage rigiman wani Lokacin.
Sunan zai kama ranar jumma'a da Safe misalin karfe goma na Safe na gama wankin kayan yara kenan ina Daki ina shirya Ahmad da nayi mai wanka,kwata kwata ban ji sallama ba Saboda lalurata sai da naji Mganar ta kamar daga kofar Dakin da nake ciki,Ina juyowa muka hada ido Hudu da Yaya asiya Sabe da Jaririnta da karamar jakar matafiya a Hannunta.
Na saki baki fararan hakora na suka bayyana cikin yanayina da murnar da ta cikani nace"Yaya Asiya.."
Dariya tayi Lokaci daya tana karisa shigowa Dakin tana fadin"Na'am Yar Fa'i"Daman ta kan kirani da hakan in tana so ta zolaye ni..
Sai nayi Dariya,na bar Ahmad kan gado bayan na gama sakamai kaya na karbi jakar hannunta na sauke a gefe sannan na karbi Muhammad Auwal dake hannunta ita kuma ta Dauki Ahmad ta daga shi sama tana fadin"Kai Ahmadu naga ka kara girma ne daga ganinka Yaya Ishaq ka Dauko Tsawon kafa zaka yi"
Dukkanmu gefen gadon muka zauna na kamkame Muhammad Auwal da ya zama Lukuti da shi Dagani yana samun kulawa da kuma Nono mai kyau.
Cikin nuna farincikina na shiga gaisheta ta amsa itama cikin Fara'a kafin tace"Nace ni dai bari nazo na gani ko Fa'ina na lafiya ko bata san na Haihu ba ne? shuru baki ba wayarki sannan ina ta kiran ki a kashe kwata kwata bana samun ki kin gani Karofi zani nace bari na fara sauka naga Lafiyarki"
Tana fad'a tana karemin kallo Lokaci daya da nazarina sai na sunkuyar da kaina ina wasa da showel din dake jikin Muhammad Auwal,Naji kunya sosai shi yasa na kasa mgana na kuma san ko zan mutu Ya Ishaq bazai barni naje kano ba ko da ma nasan Haihuwarta ballatana ban sani ba sai zuwan da su Goggo suka yi,bayan sun baro kano alokacin.
Ganin na ki mgana yasa ta kyaleni ta Fahimci abun sai bata matsa min ba,Cikin Nazarin Dakin tace"Naji gidan shuru su Amir suna makaranta kenan..?
Kai tsaye nace mata"Suna chan wajen Babansu jiya mama ta aiko Badariya ta tafi da su baban su yace a taho da su"
Yaya Asiya tace"An yi haka jiya naje gida na iske su Hajiya nata shiri ni ban ma sani ba sai ajiyan ake cemin Amaryan Yaya Ishaq ne ta haihu aiki akayi mata gobe taron suna..har ma ake fadin Ishaq din ya yi ma mahaifin ita zainab din kara sunan babanta ya saka Lawal ammh zasu rika kiransa Farhan"
Kai tsaye nace"Allah ya raya sa"
Ta amsa da Ameen tana fadin"Ke ba'a je da ke ba kenan..?
Sai da na dago na kalleta sannan nace"eh bai ce a zo da ni ba"
Ta gyada kai tana fadin"Bakomai bayan an kwana biyu sai kije ki yi mata barka in kuma tazo shikenan"
Ban amsa mata ba na daga Auwal a Hannuna ina Fadin"Kai Yaya Asiya naga ya girma ne kun yi wata uku ne..?
Dariya tayi kafin tace"Watan sa biyu ne fa da kwanaki yana da girman jiki ne irin Goyon Husain ne zan yi"
Na mike ina Sab'asa a baya na kafin nace"Eh ai suna ma kama da Husain din"
Tace"haka kowa ke cewa"
Tsab na goyesa a bayana na Saka zani ya lafe Ahmad kuma daman da yaji Ruwan zafi sai barci kan gado Yaya Asiya ta kwantar da shi muka fito Falo muna Hira ni dai ina ta Fargaba kada ta sako mganar abunda ya faru Tsakanin Ya Ishaq da Yaya mariya sai naji batamin ba.
Ita tayi mana girki Shinkafa da wake da mai da yaji,Ita tazo min da yaji da kori a robobin su tunda Sana'arta kenan na Dauka ina shinshina kamshin Korin cikin jin dad'i nace"Yaya Asiya korin nan nada kamshi nima ina so na iya had'awa ko shi na fara saidawa in za'a siya"
Yaya Asiya tace"Indai za'a siya koyan sa ba shi da walaha Fa'iza..Sai na koya miki ke da ma na sanki da Sauri Dauke abu cikin Lokaci zaki gane komai sai ki rika zuwa kasuwa kina Siyo kayan  had'in kina hadawa da kanki kuma wlh akwai samu in dai kika Samu masu siya sosai"
Tun da naji ta ambaci kasuwa jikina yayi sanyi sanin ko sama da kasa zata Hade Ya ishaq bazai bar ni na rika fita kasuwa ba sai na share zencen ban kara mata mganar ba.
Sai bayan mun yi sallar azahar mun zauna muna cin abinci ta dago tana kallona kafin tace"in na kwana anan Gobe da Safe zan yi sammako na biya ta Dutsemah na gaida Tamadina na kwanan mata Daya daganan na karisa Karofi na sauke gajiya achan sati yace nayi kafin na koma"
Kai na jinjina kafin nace"Tamadina ta na lafiya..?
Kai tsaye tace min"Lafiya ke shuru Fa'iza muna saka ran haka kwanki da ina jego mun yi waya da Megidanta da Abokiyar zamanta sun tabbatar min tana lafiya,ban ce a bata ba ne kinsan ko tayi mgana awaya bazan gane komai shiyasa na bari sai nazo naje na ganta"
Na kasa mgana kunya nake ji ni da nake kusa ammh mahaifiyata na Raye sai ta shekara bata ganni ba Idanuwana suka ciko da kwallah Yaya Asiya ta gani ta kalleni sannan ta Girgizamin kai kafin tace"Kada ki dami Fa'iza nasan yanayin da kike ciki..Ki zauna ki yi ma aure Biyayya In sha Allahu zaki Rabauta ranar gobe kiyama a wajen Ubangiji..Sai dai duk Lokacin da kika samu dama ki rika zuwa kina Dubata bayan mu bata da kowa Fa'iza ita kadaice ta rage mana sauran gatan mu anan duniyan"
Jinjina mai kai nayi ban ce komai ba ina Tunanin to yaushe nake samun Daman. ?Ko karofi sai na jima ban je ba,in kuma naje sai mutuwa ko Biki suna ma ba na kowa ba sai wanda Mama ta amince min naje nake zuwa.
Zuwan Yaya Asiya ya D'ebemin kewa sosai,Sannan na Fahimci ko Rashin Lafiya na bata sani ba sannan ban ji  tamin mganar ba sai nima nayi mata shuru ban gayamata ba.
Da yammah na rakata makota na ta gaida su Sa'adatu da Habiba ina jin Dad'i Lokacin da na nuna ta nace yayata ce itace Babba ad'akin mu Sa'adatu ta kalleta tace"Ba kwa kama Maman Amir"
Dariya nayi ban yi mgana ba Yaya Asiya ce tace"Ai mu mun fi kama da Babanmu..Ita yanzu da ace kin taba ganin Mahaifiyarmu sai ki iya cewa yaya da kanwa ce saboda Tsabar kamar da suke da juna"
Haka ma Habiba tace itama kamar yadda ta fad'ama Sa'adatu haka ta fadamata,Da muka Dawo gida Yaya Asiya tace"Ko kefa Fa'i ki rika shiga Mutane don.Allah..Yafi ki yi ta zama agida ke kad'ai kamar mayya..Mutane Rahma ne sannan Makoci yafi dan'uwaka tunda sai wani abu ya sameka kafin wani naka yazo ya kawo maka Dauki makocinka yazo ya taimake ka"
Cike da gansuwa da mganarta nace"Hakane"
Domin ya faru akaran kaina kuma nagani,Tare muka kwana agado daya yaran mu na tsakiyar mu mun dad'e bamu yi barci ba Duk Mganar Yaya Asiya na Hakuri ne da kuma hakuri da yadda zamantakewar aure tazo min kafin mu kwanta sai da tace min"Fa'iza gaskiya ya kamata ki fara wata sana'ar ai zama haka bazai haifar miki da komai ba sai takaici Daman mun yi mgana da Mariya zamu tarfa miki jari tunda kina sha'awar Korin ko shi zaki jaraba ki gani ko za'a dace..?
Nayi shuru ban ce mata komai ba sai ta kyaleni sai da Safe bayan mun karya tayi shirin tafiya ta karamin mganar cikin yanayin mganata nace"Yaya Asiya bazai bar ni na rika zuwa kasuwa ba"
Tayi shuru kafin chan tace"Kuma da wannan don wannan..To shikenan  dai zamu tattauna muga wata sana'ar zaki fara wacce bazata kawo miki matsala da mijin ki ba"
Da haka muka rabu da ita har waje na rakata,ina ta mata godiya tazo min da caryfish da yawa,tace na rika miya da shi sannan da Bushasshan kifin da tazo da shi zata kaima Tamadina da su Goggo ta D'ibarmin na karba ina jin hawaye suna kawomin cikin Idanuwana kalli yadda yan'uwana suka zame min garkuwa ammh ahaka su Mama ke min kallo kaskastttaciya mara gata.
Na bata sakon gaisuwa wajen Tamadina tace min insha Allahu zata sanar da ita Sannan nace agaida su Goggo da kowa da kowa ammh na kasa cewa ta gaida min Yaya mariya ina Tsanaanin jin kunyarta sannan ina Tunanin ta Rufamin asiri bata bayyana ma kowa abunda ya faru ba.
Sai naji ta burgeni ta zama yar'uwa mai Rufa ma yar'uwata asiri.

****

Sai Ranar Litini da yammah Jamal ya Dawo min da su Amir,sun zo da kaya niki niki da jakunkuna mai Dauke da Hoton Zainab da Ya ishaq da kyakyawan D'an su kamar balarabe sannan kaladan ma ta Hoton yaron Dauke da sunan Lawal Ishaq kabir karofi(FARHAN)
yaci kayan alfarma kamar asace sa a gudu in ka gansa kamar d'an larabawa,Dole yayi kyau daga uwarsa har ubansa masu kyau ne masha Allah.
Sun taho da kayan fulawa da yawa da Soyayyan Naman kaza,Samosa,Meatpie,Sprilroll,Cake,Da sauran sai lemukan gwangwani jaka shake da kaya Sannan sun taho da Sabbin kaya yan kanti a bakin Amir naji yace Antyn su ta basu sabbin kaya.
Su Anum yan Abuja sai tsallen murna take tana ta bani Labarin abunda ya gudana achan Jamal na zaune kan kujera mai zaman mutum d'aya yana Latsa wayarsa shi haka yake bai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login