Showing 18001 words to 21000 words out of 96493 words

Chapter 7 - Kana Naka Book 1 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

200

ba bata iya cin abinci,Shi ko Baba kullum Mama yake godemawa yana ganin ita ta tallafamin na iya girken girken zamani zuwa kuma Lokacin na rage wasu walwahalun,Saboda Mama ta daina aike na ta samu yaron aike bangaran kasuwancinta kuma komai ta waya ne sai dai a saka mata a mota a aiko mata dashi,sannan ta dauki masu wanki da guga da kuma mai wanke wanke na koma gyaran gida da girki.
Jin baki ya ishaq zai zo da su na Zage nayi musu girki mai rai da lafiya fatan pototo,da Hanta sai white rice da Miyar kifi,Sai nayi musu lemun Abarba Sai na hada musu da na Gwangwani kafin ya kariso Mama ta sani na je na shirya komai afalon Baba,na koma kitchen na Dora abincin dare na gida har bakin suka zo ni bansani ba Na gama girkin Dare doya da Miya Mama tace ayi naje nayi sallar mangariba ina zaune saman sallaya Jamal ya shigo Dakin da nake mai karamar katifa sai tarkace yace min Ya Ishaq na kirana afalon Baba sai da gabana ya fadi ban cire Hijabin jikina ba yamin yawa yana neman gadani na nufi Falon Baba
Ina shiga da sallama gabadaya zaratan mazan dake falon suka Dago suna kallona ni ban iya kallon su ba,Saboda yadda jikina ke kyarma,ina ji Ya Ishaq ya dakamin Tsawa yana Fadin in kariso,Ni dai nasan nazo gabansa na durkusa kaina na kasa ina ji yace musu"To ga wacce tayi girkin nan da kuka matsu ku ganta"
Ya fada cikin sigar Dariya da karfi yayi mganar yasa naji abunda yace gabadaya shuru sukayi kafin naji sun kaure da Dariya gabadayansu sai naji na muzanta matuka muzantan da ban taba yi ba suna ta mganganu wasu ina ji wasu kuma bana ji nadai ji sanda Ya Ishaq yace"Kai ka yi mata da Hausa No Turanci..Sannan Ears."
Gabadaya suka gwalalo ido kafin ya kalleni yace"Yes..sai kunyi mgana da karfi zata jiku Bebiya ce"
Na kusa dani ne ya matso saitin kunnena yana Fadin"What is your Name.?
Aoh Sorry ya sunanki..?
Na dago idanuwana sun cika da kwallah nace"Fa'iza"
Cikin yanayin mganata gabadaya sai suka sheke Da Dariya har suna Tafawa da junansu Sai naji na kara raina kaina Nasan ni ba bebiyace ba ce ina dai da Raunin ji ammh ba Kurma bace ni Mutane ne suka kara Raunana jina da kushe da Tsangwaman su akaina,Ninasan inaji sai dai sai an yi mgana da karfi Sannan mganata tana  da Tsami Tsami Kuma ina Rabe ta kamar ina in ina kuma saboda Raunin ji na ina karantar bakin mutum in yana mgana Ko Tamadina ba Kurma bace tana mgana sai dai mganata tafi nata fita sannan na fita karfin ji.
Ammh yadda suke kankanba Bebanci na abun bai kai haka ba.
Ban taba jin guilt irin wanda naji ba  Ranar hawaye suna bin fuskata na mike zan fita Ya Ishaq ya dakamin tsawa yana fadan sun sallameni ne..?sai na Dawo kawai na Durkusa ina jin Ya Ishaq na fadin bai taba ganin baki da muni ba sai a wajena su ma abokan irin sa ne suna ta Dariya na kamar sun ga abun dariya ajikina ko acikin Abunda suke ma Dariya aciki akwai wanda na bama kaina ba Allah ya bani ba? abun da nake sakawa araina kenan ina jin wani irin abu a kasan raina.
Sun dade suna kallona suna Dariya kafin Ya Ishaq yace na kauce daga gabansa na mike idona ya rufe bana ko gani,bansani ba na ture Teburin dake gaban su jug din lemu ya fado ya zube Lemun ya fallatsa a jikin abokan nasa dashi kanshi har ga Allah ban lura ba,ba karfi ji ne dani ba shiyasa ban ji karar faduwar wani abu ba,ba ma haka ba yanayin da nake ciki gabadaya ji na sa ganina ne suka Dauke a lokaci d'aya.
Na dai san kafata ta bigi wani abu ammh yanayin da nake ciki bai sa na Tsaya Dubawa ba.
Sai ji kawai nayi an dawo dani baya an yarfar dani akasa ya Ishaq ya Daga Hannu ya wankeni da mari acikin kalmominsa na tsinci kalmar"Banza Jaka,Mummuna useless har na isa na wulakanta abokansa ko akwai sa,a na acikin su ne..?
Ina dafe da kuncina na bisu da Kallo ya fadi gaskiya ba sa'a na acikin su kamar yadda yake kyakyawan gaye haka suke suma,jikina na rawa na fara bashi Hakuri sai yace sai na juya na basu hakuri haka na Durkushe ina basu Hakuri sai da sukace sun hakura ya bi ni da Hambari ina Rarrafe na bar Falon ranar kwana nayi ina kuka har na fara neman nayi Sabo sai na zauna nace meyasa Allah bai yo ni mai kyau kamar kowa ba..?
Ko dai da gasken ne bani da Sa'a..?
Washegari Da Mama taji Labari Allah ya kara tayi har da fadin da ya fada mata Tun jiya sai ta karamin da Duka.
Ina Falon ina goge goge ne alokacin naji sanda Jamal yace"Kai ma Bro meyasa ka kirata cikin abokan ka.?
Sai da yayi tsaki mai karfi kafin yace"Su suka matsa sai sun ga wacce tayi abincin"
Daganan ban ji meya ke fad'i daga karshe ba,Saboda ya Rage murya Ranar ina aiki ina kuka abaya bana Damuwa in an kusheni ammh yanzu sai naji kamar da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a
Ashe abunda Ya Ishaq bai sani ba Matarsa ya Tozarta,Agaban abokansa Domin ko sati ba'ayi ba Baba ya tafi Karofi Sakamakon kiran da Goggo tayi mai kan cewa jikin Hajiyar ya tashi Abun mamaki tana ta kiran sunan sa shi da Mama da ya Ishaq suka tafi suna chan ne nima ina gida Hankalina nakan Hajiya ban san me ya faru ba, ni dai nasan sun Dawo gidan cikin Hargitsi da Rashin kwanciyar Hankali mama sai kuka take yi tana Fadin bamai hada mata zuru'a da Dangin munana da kurame.
Washegari fada ita da Baba har Falo alokacin naji Baba yace"ko bayan Ransa sai auran Fa'iza da Ishaq ya kulli sai dai ta mutu"
Dayake da karfi yayi mganar naji sa ni kaina sai da na gigice ana haka sai ga Ya jamal yazo yana fadin Ya Ishaq ya kwashe kayansa ya bar gida Mama ta fadi kasa Hannunta akai tana kururuwam ta shiga uku ta Lalace
Haka Baba ya tsallake ya barta ban bari kowa ya ganni ba na koma Daki ina rawan jiki mai nake ji,Wai ni Ya Ishaq zai aura.?
Tirkashi ni kaina na hango tashin Hankali acikin lamarin ranar har Anty Binta tazo ita da Anty Mahma da kawayen Mama na kusa,sai mganganu suke ni,ni ina Daki baji nake yi sosai ba, ranar ko girkin ban iya yi ba kuma ba wanda ya nemeni.
Nima Badariya ta shigo take fadamin Wai Hajiyar Karofi tace a hada aurena da Ya Ishaq,ance Dakyar ma aka gane me take nufi Saboda Harshenta ya karye.
Ba Ya Ishaq kadai Hajiyar Karofi ta cuta ba  wlh har dani ina ni ina Ya Ishaq ai tazaran ma mai yawa ne.ranar kafin Baba ya Dawo Mama da su Anty Binta suka kirani Falo suka min Fata fata zagi da gori ba wanda ba su yi min ba har da gorin mu dangin maciya Amana ne to wanda ma naji kenan wanda kuma ban ji bansa me suka fada ba,Dayake da karfi suke mganar Anty Binta ko har tana Hadamin da dunguri Mama taci kuka har ta godema Allah idanuwanta sun kala sun yi jajir Ita damuwarta Ishaq ba bawanda yasan inda ya tafi ya kuma kashe duka wayoyinsa Mama taja kunnina da cewa in Baba ya Kirani ya tambaaye ni in na amsa mganar auran nan sai na gwammace rashin amsawata Domin bata fatan Had'a zuru'a dani Har gaban Abada.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Littafin KANA NAKA paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*





*Janafty*
*KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* 🥰🤗

      *🅿️05*

Lokacin da Baban katsina ya kirani Falonsa adaran da su Mama suka ja kunne ne ammh na kasa iya d'ago ido na kalli Baba ballatana nayi mai gaddama kan lamarin da yazo min dashi cikin wani yanayi na roko da Tausasawa Baba ya sanar dani Umarnin Hajiya na had'a aurena tsakani na da Ya Ishaq shi Uba ne gareni zai iya aurar dani ko da ban sani ba addini ya basa wannan damar ammh bai yi haka ba, sai ya zabi da  ya kirani yana Roko na na amince don ya samu damar da zai cika Muradin Hajiya..
Ina kallonsa da kumburarrun idanuwana da suka tasa saboda kuka Da damuwa Hawaye suna Biyo Fuska ta wasu na korar wasu Baba nake kallo wani Mutum da nake gani Da kima da Daraja mutumin da nake ganin shi Kad'ai ne ya ragemin gata na aduniya ta ya ya zan iya bude baki nayi mai gaddama.? Amsa masa kuma Daidai yake da Fadawa Ukuba kamar yadda Mama ta shaidamin ita da su Anty Binta..
Na bude baki da niyar nayi mgana kalmar
" Baba.."
Kad'ai ya iya fita a bakina sai kawai na saka ma Baba kuka shi kuma bai duba yanayi na ba ya shiga sakamin albarka da Fatan gamawa da Duniya Lafiya sai harshe na yayi nauyin da har Baba ya sallame ni na kasa Furta ko kalma d'aya ammh a kasan raina nasan wannan auran bai kamata ya tabbata ba Domin babu had'i ko gami acikin sa gabad'aya.
Ranar nasha kuka kamar raina zai fita Tun cikin Dare Mama da Baba suke Rigima da karfi suke mganar Shiyasa nake jiyo su sama sama Tunda Baba ya fita sallar asuba bai Dawo ba Mama ta rude ta shiga tashin Hankali Saboda rashin Sanin inda Ya Ishaq ya shiga Tunda yaji mganar auran mu
Ni dai ban san ya akayi ba ina kwance sai ji nayi an rufeni da duka kota ko'ina,ina kuka ina ihu ammh Mama bata Tausayamin ba kuka take yi tana Dukana fadi take yi"Dangin jaraba dangin masifa Saboda ke Abban Ishaq yace zai iya rabuwa dani...?Saboda ke Ishaq ya bar gida ban san ina ya shiga ba..? Kuma ahaka zan amince na hada Zuru'a dake..?wlh sai dai ki mutu ammh ni Saudatu bazan taba Hada zuru'ata da b'ara gurbi irin ki ba Shegiya ya'yan shegu dangin maciya amana Mummuna dake D'ana yafi karfin ki"
Da karfi take mgana shiyasa na ke jinta ina ta bata Hakuri bata jini ba Badariya na gefe tana kuka tana rokon Mama ta kyaleni ammh bata tanka ta ba Jamal kuwa yana Tsaye shima Fadi yake yi"Mama duka wayoyin ya Ishaq suna kashe ne sannan na kira abokan sa na kusa sun sanar dani bai zo ba kuma bai kira su ba..Gaskiya Baba shima bai yi Tunani ba Ta ina Ya Ishaq ya Dace da Fa'iza..?
Ina ji Mama ta wurgoni Falo tana Fadin"Ai yadda ta saka ya bar gidan nan nayi Rantsuwa bazan yi kaffara ba itama ta gama zama a wannan gidan yau ba sai gobe ba sai ta bar min gidana"
Da duka da gori da Tsinuwa Mama ta rakani waje ta maida kofa ta Rufe,Dagani sai rigar jikina ta atamfa sai dankwali shima tana Dukana na Rarumeshi na rike a hannuna kafata ba Takalmi Mama ta koreni nan na rakube jikin gidan ina ta kuka na Duba gabas da yammah kudu da arewa bani da wani gata a garin katsina kuma Mama Tunda tayi Rantsuwa to da gaske take Dankwalina na warware na yane kaina Dashi gidan Anty Mamah ya fadomin tana da Sauki Sauki kila ita zata iya taimakamin da kudin motan da zan koma karofi domin chan ne gata na anan duniya..
Da kafata Tun daga Kofar soro har Cikin asibitin kashi,A kafata ina tafe ina kuka kamar zararriya,ban gaji ba Domin halin da nike ciki gajiya bata da Muhalli a wajena Sai dai Anty Mahma ta ganni kwatsam kamar Daga sama tayi matukar kad'uwa da na zube ina bata labarin korar da Mama tayi min Kai ta girgiza kafin tace"Kai Mama meyasa bata bin abu a Hankali ne..?
Bari na kirata.."
Da Sauri na rike mata Hannu naji tana mgana ban ji me tace ba sai dai Yanayin mganarta da wayarta data Dauka sai Tunani na ya bani Mama zata kira ko Anty Binta ni kuma na shiga Tsaka mai wuya acikin wannan Halin Karofi nake son zuwa na Durkushe gaban Hajiya na Roketa ta janye wannan mganar in tana so na cigaba da Rayuwata yadda Allah ya Tsaramin in  bata so ta kara jefa Rayuwata cikin wani Sabon kangi.
Dakyar Anty Mamah ta amince da Rokona ta bani kudin mota ta Daukeni a motar ta da kanta ta kaini Tasha ta sakani a motar Karofi ina ta kuka ta Tausayamin ta Dafa kaina Dake cikin Sabon Hijabin data bani da Takalmi tace"Ki daina kuka Fa'iza ba matsala in sha Allahu Mama zata Sauko"
Har na kai karofi kuka nake yi sai da Muryata ta dishe kukan rashin gata da kuma Tunanin yadda yanayin Rayuwata ya fara na fara jin kamshin gaskiya kila bani da sa'a ne komai nawa ba mai kyau ba ne irin na kowa rayuwata ba Daidai take da Sauran mata ba.
Sai dai Goggon Karofi ta ganni yarkace yarkace kafin na fadamata abunda ya faru sai ta nemi dukana sannan na Zayyane mata komai bazan manta ba sai da ta share kwallah ta kamani ta Rumgume tana Fadin"Abunda Saudatu ta aikata miki kenan..? Daina kuka Fa'iza watarana sai Saudatu tayi kuka idanuwanta akan abunda ta aika miki akwai Allah"
Araina ban taba Hango hakan ba ni kuwa wani matsayi zan taka da Mama zatayi kuka Saboda ni..?
A daran ta Kira Baban katsina ta fadamai Halin da ake ciki yace da Safe zai shigo garin ni kuwa Lallashina Goggo ta dinga yi Hatta Hafsatu dake da karancin shekaru ta shiga Damuwa ganina cikin wannan Halin Hajiyar karofi kuwa tana kwance sai bina da kallo take na kasa na mata wata mgana domin sai naji bakina yayi nauyi ganin yanayin datake ciki Goggo tace tun ranar da Baba ya bar nan jikin Hajiya ya kara rikicewa.
Washegari Baba yazo sun kai ta ba dadi da goggo ta nuna mai ya janye mganar auran nan ita zata rikeni Allah ya bani wani mai sona in yi aurena ammh ba Ishaq d'an Saudatu ba shi kuma Baba yace indai yana Raye sannan shi ne Uba ga Ishaq kamar ya aureni ya gama ina Durkushe gabansu suka rika wannan Hayaniyar ad'akin da Hajiya take jinya itama tana kwance bata iya mgana ba sai gyad'a kai hawaye na bin gefe da gefen Fuskarta.
Baban katsina ya tafi ko sallama bai yi ma goggo ba Allahu akbar adaran Hajiya ta amsa kiran Mahallacinta,Tun daga Lokacin da naji goggon na Salatun mutuwar HaJiya da kaina ya amsa Dum! Har gobe in na Tuna da mutuwar Hajiya sai yanayin ya Dawomin da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a?
Meyasa duk wad'anda suka Tsayamin suke tafiya su barni Farko Babanmu Sannan ga Hajiya itama har aka kai Hajiya kushewarta bana cikin Hayyacina gida ya cika Har Hajiyar Dala da duka zuru'arta suna nan Hadda Mama da su Anty Binta su Ya Asiya sun Dauka mutuwar Hajiya ce ta tab'ani basu san abunda ke Faruwa ba har kuma lokacin ba'a san ina ya Ishaq ya shiga ba.
Ranar da bazan manta ba,Itace Ranar da aure ya kulli tsakani da Wanda bai Taba sona ba har ko yau da muka Tara zuru'a dashi aurena da Ya Ishaq wanda yau har gobe Mama bata daina aibatani da zuru'aar maciya Amana Dangin Tsiya ba,Ranar addu'ar bakwai din Hajiyar Karofi Baba ya tara Mutane ya Biya Sadaki aka Daura aure na ba wanda ya sani sai da aka Daura Gidan mutuwa sai ya koma Gidan Fad'a da Hayaniya domin Mama kaina tayi tana fadin sai taga bayana Goggon Karofi ta shiga Tsakani Ranar ba iya ni kad'ai ba hadda Mahaifin mu dake kasa yasha zagi Taamadina na gidan sulalewa tayi ta koma gidansu tana kuka,kukan maraici da Tausayin ya'yanta.
Sai alokacin kowa yasan Halin da ake ciki Goggon Karofi ce kad'ai da ya'yanta ke tare dani ban da Hajiyar Dala data mara ma Mama baya,Aranar Mama ta koma katsina ta sha alwashin sai taga yadda auran nan zai Tabbata shi kuma Baba yace sai dai in ba shi ya Haifi Ishaq ba.
Ya Asiya da Yaya Mariya sun koma Gidajen su da Tunanina aransu da Tausayina su kan su sun hango Yadda rayuwa da kaddara suka kara gangarawa dani.
Kwana Ashirin da Rasuwar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login