Showing 42001 words to 45000 words out of 104658 words
Chapter 15 - Kwai Cikin Kaya Book 1 Hausa Novel Complete
Aliyu da Gimba suma, inda take facing ɗin Jawaad da har yanzu bai kai shayin bakinsa ba yana cigaba da danna lap-top ɗinne.
Amaryar Alhaji kokino ce ƙarshen shigowa cikin shiga ta alfarma, ta samu waje nesa da kowa ta zauna.
Sai lokacinne Jawaad ya janye system ɗin daga saman cinyarsa yana maida hankalinsa garesu.
Shayin yakai bakinsa kafin ya basu dukkan nutsuwarsa yanayin gyaran murya.
“Zakuyi mamakin cewar da nai a tattaromin ku duka, so amin afuwa idan na shiga rayuwarku da yawa. Dama dai akan maganar Alhaji ne, maganar gaskiya a koda yaushe lamarin nan sake rikitar damu yakeyi, musamman idan mukai dubi da lafiyar ALLAH suka baro filin jirgin, ku kuma gashi kunce bai shigo gidannan ba, sai labarin rashin ganinsa aka kawo muku”.
“Hakane kam yallaɓai, mu kanmu mun rasa yanda zamu kwatanta al'amarin gaskiya”.
Kai Jawaad ya jinjina yana duban Amaryar Alhaji.
“Hajiya kece kuka dawo da Alhaji daga tafiya ai?”.
Zamanta ta gyara sannan cikin isa tace, “Tabbas tare muka dawo, sai dai shi gida aka wuto da shi, ni ko gidanmu na wuce saboda uzirin san zuwa na duba mahaifiyata da bata da lafiya, mun rabu dashi akan zaije gida ya kimtsa shima sai ya zo yaga jikin nata”.
Jawaad yay murmushin gefen baki a zuciyarsa ya furta “Kamar yanda aka shirya kenan”, a fili kam sai ya jinjina kansa yana maida hankalinsa ga Uwargidan Alhaji da fuskarta kawai ta isa ta nuna maka tsagwaron damuwarta.
“Maganar gaskiya Hajiya a yanda nazarina ya nunamin Alhaji ya shigo cikin gidannan, cikin abu uku kuma tilas ɗaya ya kasance”.
Kusan gaba ɗayansu zuba masa ido sukai cikin wani irin zumuɗi, suka haɗa baki wajen faɗin, “Yana cikin gidannanfa kace yallaɓai?”.
“No, ba ayanzu nake nufiba” Jawaad ya faɗa yana miƙewa riƙe da kofin shayi a hannu, tamkar malami da ɗalibai haka ya tsaya musu ƙikam dan ya samu damar nazarin fuskar kowa a falon.
“Cikin abu uku dana ambata dolene a samu ɗaya kuwa, na farko shine, ko dai an shaƙama Alhaji wani abu an barsa a motar da aka ɗakkosa sannan aka sanar da ɓatansa gareku, da ga baya kuna cikin wannan ruɗanin aka sake fita dashi daga gidan, kokuma ba'a fitan dashiba yana cikin gidannan har yanzun, ko kuma tunma a hanya drivern sa ya bada ƙafar da akai canjin motar da aka ɗaukesa da wata, ina nufin da haɗin bakinsa a ciki, dama duk wanda suke tare a wannan lokacin
Cikin fusata Amaryar Alhaji Kokino tace, “Ban gane mi kake magana akaiba ɗan saurayi, ya zakayi jam'u akan duk wanda yake tare dashi?”.
Jawaad ya rumtse hannunsa da ƙarfi yana feso numfashi mai zafi, dan ya fara hasala da maganar hajiya Amarya, amma kasancewarsa gwanin ƙwarewa akan aikinsa sai yay azamar dai-daita kansa, “Hajiya ke ai babuke a ciki, saboda tun a filin jirgi kuka rabu kikace? To miye haɗinki ma da tawagar wanda sai da suka shigo har gida dashi?”.
“Hakane” ta faɗa aɗan daburce.
Kusan da yawansu lamarinta sai da ya basu mamaki, amma sai basuce komaiba.
Jawaad ne ya katse musu tunani da kiran sunan Gimba.
Gimba dake daga can gefe yana aikin nazarin kowansu yay saurin faɗin, “Yes Boss”.
“Kiramin mai gadin gidannan”.
Da sauri gimba ya fice, Jawaad kuma ya sake kallon budurwar ɗazun Shema'u data haɗa musu shayi yace, “Zan iya ganin ma'aikatan gidannan duka?”.
“Mizai hana boss” tai maganar da salonta na jan hankali.
Idanunsa ya janye yana faɗin, “Wannan ƴar matsalace” a saman laɓɓansa.......
A mamakinsa sai yaji tace, “Mi kace?”.
Kai ya girgiza mata alamar babu komai.
Cikin mintuna ƙalilan kowa ya hallara, Jawaad ya bisu da kallon nazari, kafin yace, “Inason ku bani haɗin kai, duk maganar da wani ya faɗa daga baya na fahimci ƙarya a cikinta sam bazan yafe masa ba”.
Duk suka amsa da cewar zasu fa ɗi gaskiya.
Kansa ya jinjina musu ya koma cikin kujera ya zauna, “Mai gadi da kai zan fara”.
“To yallaɓai”.
“Kaine a gate, kuma dolene komai nisanka da inda mota tai parking a gidannan sai kaga wanda zai fito a cikinta?”.
“Ƙwarai kuwa yallaɓai”.
“A randa Alhaji ya dawo motoci nawane suka shigo gidannan?”.
“Inaga dai kamar biyarne”.
“Kanaga kokuwa ka tabbatar”.
“Ayi haƙuri yallaɓai na tabbatar”.
“Idan Alhaji zai shigo gidannan kafin ranar yana tsayawa gaisuwa da ku? Kokuwa shigewa kawai yakeyi?”.
“Eh idan aka tsaya da mota ya fito daga ciki sai muje muyi masa barka da zuwa kafin ya shige cikin gida”.
“To aranar kunyi hakan?”.
Jimm mai gadi yayi bai tankaba, sai da Aliyu yace, “Ya dai?”.
Firgigit Mai gadi ya dawo hayyacinsa, cikin in ina yace, “Gaskiya bamu gaisa ba, dan na nufi zan gaishesa kenan bayan rufe gate da nayi sai najiyo suna taraddadin baya cikin motar ai”.
“Waye ya fara ambata baya cikin motar?”.
“Bazan iya ganewa ba, saboda ruɗanin dana tsinci kaina a ciki, kuma darene”.
Jawaad yay guntun murmushi yana lumshe idanunsa, da alama akwai ɗan ɓacin rai tattare dashi.
Da sauri ya sake kallon maigadin da har yaji daɗi an gama dashi, “A daren wace motace ta fara fita a gidannan?”.
“Da yake kasan darene yallaɓai, amma mota kusan uku suka fita, sai dai bazan ce gasuwa da suwanene a cikiba, saboda ruwan sama da ya ɓalle.........”
Da ƙarfi Jawaad ya daki tebirin gabansa a wata irin fusata yace, “Ƙaryane!! Dolene ma ka sani”.
Babu wanda bai zabura ba a falon.
Ya kallesu da jajayen idanunsa cikin matuƙar tsawa yace, “Tabbas wanda ya aikata garkuwa da Alhaji yana cikinku, a cikin gidannan yake!! Akwai haɗin bakin wanda ya sanshi, Idan kuma har ya bari na kamashi da hannuna kashinsa ya bushe!” ya ƙare maganar yana nunasu da ɗan yatsa su dukansu, ya miƙe a fusace yana fisgar rigar suit ɗinsa ya rataya a kafaɗa ba tare da ya sauke hannunsa ba ya fice abunsa.
Aliyu ya miƙe da sauri yazo ya ɗauki lap-top da wayar Jawaad da ya bari yabi bayansa da sauri shima yana faɗin, “Hajiya ku sa ido wa junanku kamar yanda ya faɗa”.
Aiko kafin kace mi, hayaniya ta ɓarke a tsakanin Jama'ar gidan babu maijin ta wani, duk ɗinsu Jawaad ya saka musu zargin junansu da bayanin Aliyu na ƙarshe.
Jawaad kam tunda ya fito a harabar gidan yay tsaye yana dube-dube tamkar mai neman wani abu, nanko nazarin komai yake a cikin ƙwarewar aiki.
Gimba da Aliyu suka ƙaraso, a bayansa suka tsaya suna binsa da kallo, ba tare da ya kallesu ba yace, “Aliyu mika fahimta game da kowansu?”.
“Boss abubuwa da yawa ai, wannan mai gadin da alama yasan wani abu, sai dai kamar yanajin tsoron faɗa, hakama amaryar Alhaji ban yarda da itaba, sai ko dattijuwar data kawo abinci kafin kowa......”
Kallonsa sosai Jawaad yayi, ya tsaresa da idanu tamkar a jikinsa ne zaiga gaskiyar abunda yake buƙatar, sai kuma ya saki lallausan murmushi yaɗan kashema Aliyu ido ya juya a hankali yana takawa cikin izza dajin lallai shi ɗinfa ya kai”.
Murmushi gimba da Aliyu sukayi, dan sunsan halin mai gidan nasu akan iya aiki, tabbas fusatar da yay harya fito ba'a banzaba, yana kan sani ya jefa zargi a zukatan jama'ar gidan baki ɗaya......
_________________________
BILKEESU
_________________________
Yau gaba ɗaya tunda na tashi banajin daɗi, da ƙyar ma na iyayin sallar asubahi na koma na sake kwanciya, kowa yasan ba ɗabi'ata bace baccin safe, dan tunma ina gidanmu na haya bansamun hakan, balle yanzu da aikin gidansu inna zainaba kawai ya isheni.
Cikin barci kawai naji saukar ruwa mai azabar sanyi a kaina.
A matuƙar firgice na tashi zaune jikina na wani irin ɓari na razana da sanyin ruwan, ga zazzaɓi dake jikina daman.
Lawusa ce tsaye kaina tana hura hanci tamkar wata guguwar tsakkiyar rani.
“Sannu isassa, waye ɗan iskanki a gidannan da zai tashi ya ɗaura miki abimci ki tashi kici? K bara kiji, bakifa da maraba da ƴar aiki a gidannan, dolene ki bauta mana mu biyaki da abinci da wajen kwana, inko ba hakaba to lallai kuwa sai dai idan gidan zaki bari”.
Yau rana ta farko a rayuwata da nakejin bazan iya ragama Lawusa ba, hakan yasa na miƙe a bazata na zazzaro mata idanuna dake jajur saboda zafin ciwo, nakai hannu na cakumo mata wuya na maƙureta a bango,
“Tunda gidan Ubanki ne dan ALLAH Lawusa karki barni yau na kwana a cikinsa, ke wai shin jakar wane yankin jejice da bakisan darajar ɗan adam ba?! Ko an gaya miki tsoro kesa ɗan adam shiru-shirune?”.
Na ƙare maganar ina hankaɗata ta bugi da buhun masara dake ɗakin.
Ai kafinma na sake cewa wani abu ta fita a guje tana kururuwa wai akawo mata ɗauki zan kasheta.
Tsaki nayi na zube a ƙasa kamar mara laka a jiki, sai kawai naji hawaye masu zafi na saukamin a kumatu, ga wani irin rawa da jikina keyi tamkar mazari.
A haka naji mutum biyu matan maƙwafta sun shigo suna hayaniya, sai sannama na fahimci daga ni sai Lawusa ne a cikin gidan kenan?.
Sunyi maganar duniya nai banza dasu tamkar banajinsu, sai uhu sukemin a kai wai ban ƙyautaba, kalloma basu isheniba.
Lawusa kuwa tana daga bakin ƙofa taƙi shigowa tana kukan munafunci da danƙaramin zagi ta uwa ta uba da gori iri-iri.
A wannan yanayin inna ta shigo ta iskemu, ta tambayi ba'asi, Lawusa ta zauna ta shirya mata ƙarya da gaskiya, hakama matan da suka shigo, tsabar munafunci harda cewa da ƙyar suka ɓanɓare Lawusa a hannuna.........✍🏻
Page 18
...........A mamakin kowa sai mukaji Inna tace, “To kukam ALLAH ya ƙyauta muku, na lura sam jininku bai haɗuba, bara Aibo yazo, ai na samo maganin wannan yawan fitinar taku mara dalili”.
Ba Lawusa kawaiba, koni kaina nayi mamakin maganar inna, danni a zatonama yau saita koreni a gidan saboda na taɓo ƴar mai ɗinta, amma ji yanda ta nunama halin ko in kula akan zancen, sai daimaganarta na ƙarshe akan mafitar data samo ta tsayan a zuciya sosai, komawa nai na kwanta ina rawar sanyina.
Lawusa kam kuka ta sanya rurus wai dama inna bata ƙaunarta ai a gidan, yau sai ta tattara ta barmusu gidansu, sai inna ta aurama Sha'aibu ni a yau da rana danta nuna ma duniya ni ƴar uwartace”.
Duk surutan nata dai inna bata kulaba, matan kuma da sukazo haɗa munafinci sai gasu suna jan ƙafa suna fita ɗai-ɗai da kunya.
Ina jiyo fitar Lawusa tana cigaba da zagin Inna.
Kaina kawai na girgiza ina mamakin irin wannan tarbiyya ta Lawusa, a hakane wannan zata zama uwar wasu, ita kanta tana buƙatar tarbiyyar balle abinda zata haifa.
A haka wahallalen barci ya kwasheni, ban tashi farkawaba sai lokacin sallar zuhur, shima dai inna ce ta tasheni akan naje nai sallah.
A mamakina kuma na fito zanyi alwala sai naga inna tayi abincin rana da kanta bata tasheni ba.
Salla nayi, ina zaune sai ga sallamar Yaya Shu'aibu ya dawo cin abincin rana kamar yanda ya saba, muryar Inna na tsinkayo tana sanar masa bani da lafiya, hakan ya sakashi faɗin “Subahanallahi, miya sameta kuma?” yay maganar yana ɗage labulen ɗakin.
Sannu nai masa sannan na gaishesa, cike da kulawa ya amsa, ya ƙarasa shigowa ɗakin yana tambayata mike damuna?.
“Yaya zazzaɓine kawai, kuma Alhmdllh yama sauka”.
“Wayyo sannu, ai ko sauron gidannan ya isa saka mutum zazzaɓi, kici abinci saina kaiki kamiz ki amshi magani”.
Nace “to” tare da masa godiya.
Nanma nazata Inna zatace a'a sai naji batace komaiba, sai ma amsar tambayarsa akan Lawusa take bashi, duk abinda ya faru tsakanina da Lawusar ta zano masa, ta ɗora da faɗin, “Ni yanzu na samo mafita akan wannan yawan rigimar tasu, fitar danai yau wani gida ƴar kande ta rakani na samowa Bilkisu aikin wanke-wanke da shara, inasha ALLAHU tananma sai kaga ta haɗa kuiɗin kayan ɗakinta har muma mu mora, kaga bama ta yini gidanba balle wannan fitinar ta cigaba da girmama a gidannan”.
Shu'aibu da fuskarsa ta ɗan nuna alamun damuwa, yace, “Amma Inna ni dai da kinyi shawara dani da ba'ayi hakaba, wane kuma aikin wanke-wanke Bilkisu zatajeyi fisabillahi, ni dai duk da sana'ata ba wata mai ƙwari bace zanyi iya bakin ƙoƙari wajen sauke haƙƙin zuminci akan komai na aurenta, indai dan zaman gidane zanma matarcan ta tsallake magana Bilkisun taje ta fara koyon ɗinkin jakka a wajenta, kinga ko aure tayi ai tasamu madogara insha ALLAHU”.
Ran inna a ɓace tace, “Nikam Aibo bansan miyasa kake nina tamkar ina zalintar yarinyarnanba, yanzu shi aikin da zataje bazai taimaketaba ne? Ko aure tayi ai dai ta samu ta iya komai”.
“Hakane Inna, nima banƙi ta takiba, muyi addu'a to ALLAH ya zaɓa abinda yafi alkairi a ciki, idan ta samu lafiya sai muyi maganar”.
“Shike nan”
Inna ta faɗa a taƙaice, da alama dai har yanzu ranta babu daɗi akan canja mata tsari da yayi.
Bayan mun gama cin abincine ya ɗaukeni a napep ɗinsa zuwa ƙyamiz, an bani magani tare da allura muka dawo gida.
Mamaki ya kamamu saboda iske jibga-jibgan motoci guda biyu da mukayi a ƙofar gidan, sai walƙiya suke.
Na kalli Yaya Shu'aibu ina faɗin, “Yaya baƙinmu ne waɗannan kokuwa?”.
Cikin jimami yace, “Wlhy ban saniba Bilkisu, amma inhar hakane to lallai inaga Kawu Ali ne kuwa yazo, dama lokaci-lokaci yakanzo su gaisa da Inna idan ya samu dama?”.
“Kawu Ali? Shikuma wanene shi?”.
Da mamaki sosai akan fuskarsa ya kalleni, “Bilkisu kina nufin wai baki san Kawu Ali ba shima? Yayansu Inna ne fa, ɗakinsu ɗaya da Inna ai”.
“Wlhy ban sanshiba Yaya, kana nufindai shima babansu ɗaya da Innata kenan?”.
“Ƙwarai kuwa Bilkisu”.
“Yaya to ko shine suke cema Ɗan iya?”.
“Ƙwarai kuwa Bilkisu shine, amma nayi mamaki, na lura dai ke babuma wanda kika sani a dangin kenan?”.
Murmushin yaƙe nayi zuciyata na suka, murya na rawa nace, “Ai yaya sanda Innata nada rai babu wani ɗan uwanta dake raɓarta, nasan dai lokacin ina ƙarama takanje dani wasu wajajen gidan dangi, amma sai na lura saboda tana da nakasa kamar kowa gudunta yakeyi, Inna Zainabu ma abinda yasa ban manta da itaba ita da Kawu Manu saboda Innata na yawan ambatarsune”.
Tausayina sosai na gani a fuskar Yaya Shu'aibu, ya girgiza kansa kawai yana sauke numfashin tsantsar takaici, “Karki damu Bilkisu, komai na rayuwa da kika gani akwai ƙalu bale, watarana sai labari, irinku da kuke tashi cikin rashin gata ALLAH yafi ɗaga darajarku da ni'imomi masu yawa da komawa birge wanda suka juya muku bayan a lokacin da kuke buƙatar taimako, mu shiga ciki kinji, ALLAH ya ƙara miki haƙuri da jimirin cinye jarabawar rayuwa”.
Murmushi nayi ina share hawayen da suka zubomin a fuska, kusan a tare muka fita zuwa cikin gidan.
Ashema ba shi kaɗai bane harda iyalinsa, matarsa da ƴaƴansa namiji da mace su biyu, kallo ɗaya nai masa na gano asalin kamanninsa da Inna zainabu, yana kuma yanayi da innata itama, da yake ni sam ban biyo innata komaiba, gaba ɗaya kamannina na babana ne, dan dana biyo Innata da nazama ƙyaƙyƙyawa kuwa, dan su jinin fulanin asaline.
Inna tanata hidima da baƙinta, bakinta kam a washe tamkar gonar audiga.
Duk tsugunnawa mukai ni da Yaya Shu'aibu muka gaishesu, inna daketa faman washe haƙora tace, “To ka gantanan Ali, wannan itace ɗiyar Asiyar da nake faɗa maka”.
Idonsa a kaina yace, “ALLAHU akbar, ashema ta zama budurwa? Koda yake rabona da ganin Asiya tunfa kafin nabar ƙasarnan, lallai sheɗan ya jagoranci zukatanmu wajen raunana zuminci, yanzu ace ɗan uwanka da kuka tashi gida ɗaya dan aure ya ɗaukesa shikenan sai zuminci ya yanke? Manu ne ma wlhy yake sanarmin rasuwa lokacin bana ƙasar shiyyasa banzo ta'aziyya ba, ALLAH ya gafarta mata ya yafe mata, ke kuma data bari ALLAH ya rayaki kinji”.
Hawaye na share ina amsawa da amin.
Daga nan ya koma kan Shu'aibu yana masa tambayoyi akan yanzu mi yakeyi?.
Matarsa dai da ƴaƴansa basa cewa Uffan, saima faman danne-dannen wayoyi sukeyi.
A cikin tambayoyin da yakema Yaya Shu'aibu ne yakejin ai ya kammala diploma ɗinsa, daga haka karatun ya tsaya, a take yace ya bashi takardun zai nema masa makaranta ya koma, ya juyo gareni yana tambayata nifa?.
Kaina a ƙasa nace, “Ai kawu ni koma Secondary ɗin ban kammala ba”.
Ya ɗan nuna damuwa saman fuskarsa, hakanne ya sakashi maida kallonsa ga Inna yana faɗin, “To nifa inaga wannan itace hanyar dazan gyara kuskurena akan Asiya, Zainabu zan tafi da Bilkisu ta zauna a gidana cikin ƴan uwanta, itama ta samu ilimin da zata taimaki kanta koda anan gaba babumu a raye”.
Take fuskar Inna ta canja launi, hakama matarsa da ƴaƴansa wani kallo na sukemin mai kama da wannan ƙazamar?.
Yaya Shu'aibu ne kawai ya bayyana tsantsar murnarsa a fili, kafinma inna ta bada amsa tuni Yaya Shu'aibun nata godiya.
Hakan ne ya dakatar da ita daga son hawa dokin naƙin datai niyyar yi.
Niko bammasan yazan fasalta muku yanayin dana shigaba,