Showing 96001 words to 99000 words out of 104658 words

Chapter 33 - Kwai Cikin Kaya Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

208

da nasaniba ma........”
Saurin katseta mama Atika tai da faɗin, “Ke da ALLAH rufama mutane baki, waye zai sake haɗa sabgarsa da wannan shashashar ƴar taku mai kama da wadda aka yaye jiya, idan barci kike to kidawo hankalinki Ai'sha, badan wawiyar yarinyarnanba da yanzu mun gama mallakar fiyema da abinda muke buƙata, amma tazo ta ɓata mana komai saboda ita shashashar yarinyace taɓararriya, ki duba yanzu wulakancin data jawo mana ne ya saka dukkan manufofin mutan gidannan ya gama bayyana, yanzu kowama yima ƴarsa farautar yaron nan yake, dan dama can shakkatane ya sakasu haɗiye ƙwaɗayinsu a fili, dukda wasunsu na taƙamar komai yana hannunsu ne ai, maimakon kuma a shekaru huɗun nan ku nema hanyar gyara komai tunkan abunma yay nisa ta bashi haƙuri amma sai kuka ɗauketa kuka sake turawa cikin yahudawa, kekuma kika ɗauki fushi damu, yanzu har nai ciwona na gama a gidannan Ai'sha baki leƙoniba, saboda ke mai ƴa ko? To mune muka saketa? Kokuwa mune muka sakashi sakinta? Muda ta ɓatama komai mune ya dace muyi fushi ba keba? ai ko.......”
“Nidai mama naji, ya isa dan ALLAH, sai faɗa kike ko haɗiyar yawu baƙyayi, naji anyi kuskure, amma kuma ai bai ƙyautu a wancan karon kowa yaƙi fahimtar ƙaddarace sanadin komai ba, ALLAH ya rubuta cikinnan bazaizo duniyaba, daga baya kuma dai ai komai ya dawo ya daidaita, amma sai babu wanda ya kirani a cikinku, ta yaya bazan ɗauki fushiba to?”.
“Kedai kika sani, ai kuma fushin naki bai miki amfaniba, tunda gashi kin dawo da ƙafarki ko?, kuma a lokacin da kuka makara keda ƴar taki, dan kuwa a yanzu filin dagar ya zama na mafarauta da yawa”.
“Mama ki daina faɗin mun makara, babu wata makara tunda kowa yasan Jawaad nason Shahudah, kuna insha ALLAHU a cikin watannan zata dawo ƙasarnan”.
Baki mama Atika ta taɓe da yamusashshiyar fatarta ta tsufa, tace, “Kudai kuka jiyo, danni tawa tai ƙyau, dama kune masu amfana baniba, a shekaruna ni yanzu amfanin mi abinda akemawa ɗin zaimin?, komai da kukaga inayi danku nake yinsa”.
Shiru itadai Mummy tayi bata tankaba, tana nan zaune har su Uncle Uwaisu suka shigo gaishe da mama Atika, annanfa suma Mummy ta balbalesu da masifa, ta inda take shiga ba tanan take fitaba.
Wasa-wasa rigima ta kaure a tsakaninsu, dan kuwa yanzu suma ba ɗaga mata ƙafa zasuyiba duk da tana babbar yarsu a ɗakin, duk yanda mama Atika taso suyi shiru sunƙi, har sai da ta saka musu kuka sannan suka dawo hankalinsu sukai shiru.

__________________________________

To nidai sam bansan bikin da akeba a gidan, naji dai Aunty Aamilah na magana akan Aunty Shahudah zata dawo, banji an faɗi rana ba, bakuma a faɗaminba, nima sai banbi takaiba, dan bakowace sabgar gidan nake shigaba musamman ma yanzu danasan ciwon kaina.

Tsawon kwanakin da suka biyo baya a satin ban sake jin komai na faɗuwar gaba ba, hakama wanda muka taro a ranar nan ban sake ganin koda ɗaya a cikinsuba.
Duk da abubuwa masu yawa game dashi sunƙi barin raina, duk kuma ƙoƙarin turesun da nakeyi hakan baisa na damu kaina da rashin ganin nasa ba, na cigaba da harkokin gabana har a yau da mukai safiyar fita aiki kasancewarta Monday tushen aiki.
Kamar kullum nayi tsaf dani, tamkar ka saceni ka gudu, musamman ma data kasance a yau sanye nake da baƙaƙen suit na mata wando da riga, na kawo farin baby hijjab na saka tamkar yanda na saba a kowace rana, kayan sun zaunamin sosai a jiki tamkar dan jikin aka haliccesu, na saka siririn farin eyeglasess ɗina sannan na fito ɗauke da takalmana a hannu.
Babu kowa a falon, na ajiye takalman na nufi kicin, kuku harya kammala haɗa mana breakfast ni da Yah Qaseem, tea na shiga haɗawa muna gaisawa dashi, ban fitaba na zauna a ɗaya daga kujerun huɗun dake a kicin din, tebir a tsakkiyarsu, ina fara shan shayin Yah Qaseem na shigowa shi da Salman.
Nayi mamakin ganin Yah Salman da wannan farar safiyar, shi da kullum sai anyi fama dashi ma yake tashi da safen yay shirin zuwa aiki, da yake a kamfanin Dad yake aikin sai yakai goma bai fitaba ma.
Hannu Yah Qaseem ya miƙomin alamar mu gaisa, amma sai na girgiza masa kai ina murmushi da faɗin, “Yaya ina kwana”.
Hararata yayi sannan ya zauna, Yah Salman da shima ke zama ya taɓe baki.
Shima gaishesa nayi ya amsa a ɗage kamar yanda ya saba.
Ban sake bi takansuba naci gaba da shan tea ɗina nidai, suma kowanne ƙoƙarin karyawan yakeyi.
Ban wani ci abincin kirkiba na tashi na koma falo na barsu a kicin ɗin, ina ɗaura takalmina sai ga Yah Qaseem ɗin ya fito yana faɗin, “Tashi muwuce mun makara”.
Miƙewa nayi muka fice.


★★★★★

Yayin da muka isa office ina fitowa daga mota da shi na fara tozali.
Hakanne ya saka gabana faɗuwa, ganin bamu yake kalloba na ɗauke kaina daga garesa, sai ta gefen ido nake satar kallonsa, sanye yake da jeans ruwan toka da farar shirt mai gajeren hannu, idanunsa sakaye cikin glasess da yay masa matuƙar ƙyawu.
Dole inda suke tsaye shi da wani a jikin wata mota itace hanyar da zanbi ta kaini inda zanje, sai kawai na canja hanya saboda yanda nakejin gabana na cigaba da tsananta faɗuwa.
Nidai nasan ba tsoro bane ba, sai dai yanamin kwarjini da zan iya rantsewa wani ɗa namiji bai taɓamin irinsa ba, bansan miyasa hakanba? Bankuma san minene dalilin hakanba?.
Hanya na canja, sai dai inajin tamkar ana bina da kallo, juyowa nayi kaɗan dan inga ko zanga mai kallon nawa, sai dai banga kowaba.
Na cigaba da tafiya ina karanto addu'ar duk da tazomin kan harshe.
Ikon ALLAH tunda nayi nesa da wajen dana gansa sai na koma normal, harna ƙarasa wajen da nake ƙyautata zaton ganin Ummie.

Ɓangaren Jawaad kam da a yau suka dawo aiki shi da tawagarsa, ya iske ayyuka da dama, musamman waɗanda suke da matuƙar haɗarin da ake buƙatar mutum mai ƙwazo da jajircewa irinsu, wasu ayyukan kuma an badasu ga wasu jami'an ne amma sunata musu tafiyar hawainiya basu ƙarasaba babuma wani bayani mai gamsarwa, hakan yasa yau aka miƙasu gaban su Jawaad ɗin.
Kansa yaɗauki zafi da ganin ayyukan dake jibge a gabansu, duk da kuwa a yanzu sun sake samo dabaru na musamman shida abokan aikinsa da suka samu zuwa wannan horo na musamman a ƙasar amuruka, ya kuma dawo ne da karsashin aikin canja wani abu a ƙasarsa dan bai isa canja komaiba shi yasan wannan, irinsu masu son jajircewa ƙalilanne, tayaya kuwa suka isa canja komai? Sai dai suyi nasu ƙoƙari su koma gefe, UBANGIJI shike da sauran hanyoyin maganin sauran tunkafin nasu, rahamarsace ta saka zukatansu suma jin son gyaran.
Baƙon da yayi wani abokinsa da sukai secondary tare lauya, yazone bincike akan wani case shine ya rakoshi suka tsaya a jikin motarsa suna magana.
Sarai Jawaad yaga lokacin da Qaseem da Bily suka fito a motar Qaseem ɗin, amma sai ya ɗauke kansa cikin basarwa, duk da a ƙasan zuciyarsa yana tunanin minene alaƙar Qaseem da wannan yarinyar? Saboda a koda yaushe yake ganinsu tare da juna.
Sai kuma akai rashin Sa'a shima abokin nasa idonsa suka hango su Bilkisun.
Yace, “Woow, Jay kaga wata ƙyaƙyƙyawar halitta mai tsada da daraja kuwa?”.
Jawaad da ras ya fahimci inda abokinsa ya dosa tsabar rainin wayo sai yay tamkar bai fahimtaba............✍🏻

Page 38

..............Bayan wucewar abokinsa office ɗin Sir Ahmad ya wuce domin amsa kiransa, yana ƙoƙarin shiga yaci karo da Qaseem shima ya fito.
Ƙoƙarin ɗauke kai Qaseem keyi, shima Jawaad ɗin har yayi niyyar hakan, sai kuma yaga rashin ƙyautuwar abun, Murmushi ya saki har kumatunsa na loɓawa, ya miƙama Qaseem hannu yana faɗin, “Assalamu alaika”.
Ƙin miƙo nasa Qaseem yayi, sai dai ya amsa masa sallamar.
Jawaad ya kamo hannun Qaseem cikin nasa tare da faɗin, “Haba ɗan uwana, miyay zafi shiba wutaba? Ina fatan na sameku lfy? Ya jama'ar gidan?”.
Ran Qaseem ya sosu da wannan rainin hankali na Jawaad, danshi matsayin rainin hankali kawai ya kalli abun, dan haka ya kasa daurewa yace, “Da wannna salon kuma ka dawo?”.
Jawaad ya murmusa yana sakin hannunsa, cikin gyara tsaiwarsa yana shafa gemu da tura hannunsa ɗaya a aljihu yace, “Minene abin salo anan Qaseem? Kaifa ɗan uwanane jinina, sannan ga alaƙar musulinci a tsakanina dakai, kuma kai yarenane, ogana a wajen aiki, shekara biyu rabon da ka ganni na ganka, da akwai ƙaddarar mutuwa tsakaninmu maybe wani zai samu saƙon mutuwar wanine a tsakaninmu, nidai tsakanina da ALLAH na gaisheka, ya rage naka ka ɗauka hakan kaima ko saɓaninsa, na barka lafiya”..
Sagade Qaseem yay yanabin Jawaad da kallo harya shige office ɗin Sir Ahmad, yayi kamar ya bisa cikin office ɗin sai kuma ya fasa, ya nufi office ɗinsa yana juya kalamun Jawaad cikin ransa.
Jawaad kam koda ya shiga, bayan yayi gaisuwar girmamawa ga sir Ahmad sai ya nuna masa wajen zama.
Hannu Sir Ahmad ya bashi cikin musabaha suka sake gaisawa, dukda dai Jawaad na nuna jin kunyar haka ɗin.
“Jay kasan miyasa na kiraka kuwa?”.
“A'a Sir”. ‘Jawaad ya faɗa cikin kaɗa kai’.
Zama sosai Sir Ahmad ya gyara, ya fara magana idanunsa akan Jawaad ɗin.
“Wato zakayi mamaki idan nace maka baƙin abubuwa da yawa sun sake shigoma hukumarnan, masu ban tsoro da mamaki. Akwai cases da yawa dakai kanka ka fara ka tafi kabari to ina mai tabbatar maka da yawansu ba'a ƙarasa suba har zuwa yau da nake maka maganar nan, waɗanda kuma aka ƙarasa ɗin sun canzu ga bisa salon daka barsu gaba ɗaya ma. Gashi wasu cases ɗin sun sake ƙaruwa da yawa, akwai jami'inmu mai matuƙar ƙwazo kamar kai ɗinnan, bayan tafiyarku nagartarsa ta sake fitowa, amma kamar yanda na sanar maka ranar ya fita wani aiki sai dai gawarsa aka kawo mana, kasan wani abun mamaki?”.
Jawaad da idonsa ya kaɗa yay jazur ya girgiza kansa.
Murmushi Sir Ahmad yayi na takaici yana cigaba da faɗin, “Abun mamakin da har yanzu yake cizon zuciyata shine bullets guda uku da aka harbi Abdallah dashi a ƙarjinsa da cikinsa dukansu bullets ne na jami'an tsaro, abi mafi al'ajab Bullets ɗin suna cikin bullets guda dubu sittin da shida da aka kawo ƙasarnan shekaru tara da suka wuce, waɗanda a zahirance bayanai sun nuna bullets ɗin sun ƙare gaba ɗaya bayan shekara ɗaya da wata bakwai da kawosu, bullets ne masu matuƙar haɗari, dan inhar akai harbi mutum dasu acikin seconds ashirin dukkanin illahirin jinin mutum ke tsinkewa, idan ba'ai gaggawar kaisa asibiti ba ya samu taimakon gaggawa zai iya rasa ransa a ƙanƙanin lokaci, sannan ba a kowacce bindiga yake aikiba. To abin tambaya anan, yaya akai bullets ɗin da suka ƙare shekara huɗu baya kuma suka kashe mana jami'inmu? Daga ina suka fito? Wasune aka sake shigowa dasu? Koko dai sune ɗin?”.
Gaba ɗaya jijiyoyin Kan Jawaad sun mimmiƙe ruɗu-ruɗu, maƙoshinsa sai kaikawo yake a wuyansa saboda tsabar haɗiyar busashshen yawu mai ƙona zuciya.
Ya matse idanunsa tare da rumtse hannu, muryarsa a matuƙar kausashe yace, “Sir akan wane case wannan abun ya faru?”.
Sir Ahmad yay murmusa idonsa akan Jawaad, mazantakar Jay akan aiki da kishin ƙasarsa yasa ako wane lokaci yafi sha'awar ganinsa akan aiki na musamman, yaɗan ɗage kafaɗa yana buga tebir kaɗan da komawa cikin kujera ya kwanta, har lokacin idonsa akan Jawaad,
“Jay ƴan bindiga daɗi ne kawai, amma ga dukkan bayanan komai anan”. ‘Ya ƙare maganar da tura masa wani file gabansa’.
Ɗauka Jay yayi ba tare daya buɗeba, babu abinda zuciyarsa keyi sai tafarfasa kawai, shiru Office ɗin yayi na wasu mintoci, kafin Sir Ahmad ya katse shirun da faɗin, “A yanzu kana buƙatar runduna ta musamman Jay, fiye dasu Jabeer kawai, munada sabbin ma'aikata masu jini a jika da karsashin aiki a ransu saboda yanzune jinin jikinsu ke zagayawa cikin kowacce jijiya dalilin ƙuruciya da zafin rai mai tare da ɗokin aikin, sannan a cikinsu akwai kwararrun maharban da suka samu horo na musamman a ɓangaren harbi, wanda an daɗe ba'a yaye sabbin horaswa da wannan ƙwazonba a hukumarnan tamu, shawara kawai na baka ba umarniba, dan zuciyata ta yarda da kai, yarda irin wadda ko ɗan dana haifa ban yimawaba duk da kasan cewarsa jami'in tsaro shima, ALLAH yayi jagora haziƙi kuma jarumin yarona abin alfaharin ƙasarsa da ƴan ƙasa”.
Zazzafan numfashi Jawaad ya sauke yana miƙewa idonsa a matuƙar jazur tamkar ya haɗiyi wuta, yay salute din sir Ahmad sannan ya fice tamkar wanda zaije filin daga.
Koda ya isa office ma gaba ɗaya zuciyarsa a dagule take, yama rasa wane kalar tunani ya dace ace yayi, dan lamarin ƙasarsa a kullum sake bashi tsoro take, tsoro irin mai firgitarwa da ban ta'ajibi, komai anayinsane saboda kuɗi, kuɗi! Dai kuɗi! Dai, sai yaushene mutane zasu ajiye son zuciya da burin mallakar kuɗaɗe su amshi gaskiya? Da wannan rayuwarne kuma kullum muke fatan ganin kayinmu cikin aljanna, a haka mukeso ALLAH yay mana rahama, a haka mukeso MANZON ALLAH yayi alfahari damu?,
Ya rumtse idanunsa sosai yana cigaba da haɗiyar ɓacin ran daya tokare maƙoshinsa.
Bai sake fitaba, bai kuma sake barin wani ya gansaba koda a cikin su Aliyu ne, dan kulle kansa yay a Office ɗin yanata saƙawa da kwancewa.
Har sai da lokacin salla yayine sannan ya fito domin gabatarwa.



★★★★★★


Bayan sallar la'asar ya bama Rose damar tattara masa ƙananun jami'ansu sabbin ɗaukar wannan karon.
Duk da tayi mamakin hakan sai bata tambayesa ba, dan bataga alamun wasa tattare da shi ba, a yandama taga fuskarsa a matuƙar murtuke sai abun ya bata tsoro, dan irin wannan fushin nasa mafi yawan lokuta sukan gansane idan aiki ya ɗauki zafi.

Bamusan miya faruba mudai an taramu waje guda, inda aka nema mu rabu rukuni-rukuni akan abinda mukafi samun ƙwarewa dashi a wajen horaswa.
Ina cikin jami'ai masu ƙwazo da suka samu ƙwarewa wajen harbi, dan haka banyi ƙasa a gwiwa ba wajen shiga cikinsu.
Sai da duk muka gama rarrabuwa sannan wanda ya saka a taramun ya fito.

Yanda sautin takun takalman ke fidda ƙara haka nake jin sautin bugun zuciyata na fidda ƙarar bugu, zuwa yanzunkam na ɗan fara jin tsoro, ba komai ya kawo tsoron nawa ba kuwa sai fahimtar da nai kasantuwar wannan mutumin a kusa dani ke kawo min wannan yanayin da bansan dalilinsa ba.
“Miyasa sai a kansa kawai?” naima kaina tambayar da bani da amsarta.....
Na tafi tunani sam bansan bikin da ake ba, sai da naji ƙarar sautin bugawar ƙafarsune nai firgigit, dai-dai zasu ajiye hannayensu da sukai Salutes nashi.
Hakan ya sakani saurin kallon inda yake nima ina ƙoƙarin kai hannuna saman goshina.
Karaf na tsinci idanunsa a kaina yana watsamin wani kallo mai kama da gargaɗi.
Ƙasa na maida kaina, muka ajiye hannayenmu tare da ƴan uwana.
Tsayuwarsa ya gyara har yanzu dukkan hannayensa na cikin aljihun jeans ɗinsa ruwan toka, ƙamshin turarensa na cigaba da addabama ƙofofin hancinanmu, ya ɗan furzar da huci kaɗan yana cigaba da tsatstsaremu da idanunsa masu ban tsoro, gasu yau sunyi jazur alamun yana tattare da ɓacin rai.
Ganin yanda yake mana kallon ɗaɗɗayan ne yasani fahimtar nazartarmu yake ɗaya bayan ɗaya, babu zato muka tsinkayo muryarsa mai tarin nutsuwa wadda yau shine karo na farko da zan jita, sai dai kuma bamu yay ma maganarba, hakan yasa bamuji miya faɗa ɗinba duka bayan kalmomin farko na ambatar suna Rose da yayi.
Rose dake gefensa ta kallemu tana matsowa kusa damu sosai da mana bayani akan abinda yace.
A cikin kowane rukuni yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login