Showing 87001 words to 90000 words out of 104658 words
Chapter 30 - Kwai Cikin Kaya Book 1 Hausa Novel Complete
na zauna na karya, haƙuri na bata akan bazan iya cin komaiba, sannan inason na wucene dan banason wani yace zai kaini a gida.
Haka na wuce bayan na leƙa na duba Amina dake barci, a motarma lokaci-lokaci haka naita share hawaye, har ALLAH yasa na iso lafiya.
★★★★★
Shigowata gidan duk sai suka taho da murnar tarata, sai dai kuma duk sai sukai turus suna kallona.
Zuhrah tace, “Bily lafiya kuwa? Kinga fuskarki a madubi safiyar yau? K..........”
Kafin takai ƙarshe Rebecca ta amshe da cewa, “Ku wannan kuka ne, Bily miya faru?”.
Duk sun rikice, Nazifa da Ummie sukazo suka kama hannuna, ni dai ban iya bama kowannensu amsaba, kallonsu kawai nake tamkar wata gunki, hakan ne ya ƙara tada musu hankali.
Dai-dai Gwaggo hari ta shigo gidan, da gani daga wani waje take, itama da mamaki take kallona, sai dai batace komaiba har muka shige.
Rufeni sukai da tambayoyi har Gwaggo Hari, sai ma na rasa nawa zan amsa.
Ganin sun matsa ne nace musu banajin daɗinefa, subar ɗaga hankalinsu.
Badan sun yardaba suka barni.............✍🏻
Page 33
................Duk wanda ya sanni zaisan inada damuwa tun dawowata gida, a kwana na uku da dawowata mukai ɗaya a cikin jarabawar data rage mana, ranar ƴan uwana suka nunamin ɓacin rai sosai akan abinda nake ɓoye musu, dan badan taimakon Nazifa dake kusa daniba da babu abinda zan rubuta sai shirme a takardata.
Ba komai zai jawo hakanba kuma sai halin da nake ciki na ɗunbin tausayin Amina da fargabar tawa rayuwar idan na koma zaman gidan yanzu.
Ganin sunyi fushi na basu haƙuri, sannan na ɗora da faɗin,
“Ƴan uwana kuyi haƙuri, zan aikata muku babban laifi na canja burinmu nason zamowa ƴan jarida, yanzu na gane ba wan nan bane abinda nake buƙata, martaba da kare sauran ta ƴan uwana itace abar buƙatata”.
“Wace magana kikeyi haka bily, mu bamu fahimceki ba” Rebecca ce mai maganar.
Zama nai da ƙyau na shiga zayyano musu abinda na gani a gida, wanda inaji a raina cewa na manto abinda na koma ɗaukane dan na iske wannan iftila'in, dan ƙila daban ganiba babu mai bani gamsashen labari.
A take naga duk sunyi murmushi mai ciwo, Nazifa ta miƙe tabar wajen tana kuka.
Da kallo mamaki na bita, dan bansan manufar kukan nata ba, “Nazifa!”
Na ambaci sunanta, hakanne ya sakata tsayawa cak sai dai bata juyo garemu ba.
Miƙewa nai tsaye na taka zuwa gareta na dafa kafaɗarta, “Nazifa miya sakaki kuka a wannan maganar?”.
Sai da taja wasu sakanni kafin ta juyo gareni, sosai take hawaye wasu nabin wasu, ta dafa tawa kafaɗar tana sake fashewa da kuka mai ciwo. Ban hanata ba, hakama sauran ƴan uwana babu wanda yay mata magana.
Rebecca dake bayanmu tsaye tace, “Bilkisu, kukan da Nazifa keyi kukane namu mu duka, duk da dai ke mun ɓoye miki dalilin kukan tuni, sai dai maganarki ta yanzu ta sosa mana inda ke mana ƙaiƙayi harma da tuna mana abinda ya shuɗe”.
Kallonta nayi sannan na maida gasu Ummie, kukan da Ummie take har yamafi na Nazifa, dan numfashinta har sama yake tamkar zai shiɗe ta fusgosa da ƙyar.
Hankalina ya sake tashi mtuƙa fiyema da da, nace, “Ƴan uwana ku buɗemin abinda kuka rufemin ko zuciyata zata samu sukuni dan ALLAH”.
Shiru sukai kusan na mintuna biyu, kafin Zuhrah tazo ta kama hannuna dana Nazifa zuwa inda muka taso.
Duk zama mukai har Rebecca.
Zuhrah tace, “Bilkisu kinsan dai mun taɓa baki labarin ƴar uwarmu data rasu sanadin sikila ko?”.
Cikin ɗaga kai nace, “Tabbas anyi haka”.
Zuhrah ta share hawayenta yana riƙo hannuna, “Bilkisu tabbas ƴar uwarmu nada sikila amma sanadin baƙin cikin fyaɗe ta rasu”.
Cikin matuƙar razana na zabura, har taune harshe nake wajen ambaton “Fyaɗe fa kikace Zuhrah?”.
“Tabbas fyaɗe Bilkisu, ni Nazifa nida ita akaima Fyaɗe a cikin gidanmu sunje mini weekend ita da Ummie, amma abin mamaki da al'ajab sai aka rasa wanda ya aikata mana wannan ta'asa, dan kuwa kamar yanda kika bamu labarin nan sai da aka bugar da Amina muma haka akai mana wlhy. Babu kalar binciken da ba'ayiba amma har yanzu babu wani bayani, kwannamu uku a asibiti ƴar uwarmu ta rasu saboda yanayin jikinta bayason wahala, da kuma dai ƙarar kwana. Bilkisu wlhy ba ɗiyan talakawa kawai akema fyaɗe ba, sannan ba mata kawai ba, harma da maza, ƙanin Rebecca an masa fyaɗe ta hanyar luwaɗi shima kuma ya rasu”.
Kasa magana nai saboda kuka, jikina sai tsuma yake, hakan yasa na miƙe a fusace ina nunasu, “Amma duk da wannan abubuwan da suka faru da rayuwarku kuka ɓata lokacinku wajen tsara burinku akan business kawai? Rayuwa a hannun ALLAH take, amma baka yanke ƙauna daga rahamarsa, shiyyasa a kullum muke zama masu buri, kuyi haƙuri duk da ni ɗiyan talakawace, ban tashi gidanmu naga kuɗiba hakan bazaisa na cigaba da zama a cikin burinku ba gaskiya”.
Dukansu kallona sukai, bance musu komaiba naja takarda da biro nai rubutu na tura a tsakkiyarsu.
Dukansu kallon takardar sukayi, kafin su maido kallonsu gareni.
“Wannan daga yau ni Bilkisu Adam makaho shine burina, ban isa canjawa gaba ɗaya ba, amma ko alwashin dana ɗauka akan Amina da Nazifa da ƙanin Rebecca da ƴar uwarmu data rasu suka cika naci riba”.
Rebecca ta kamo hannuna ta ɗora nata, itama tace, “Daya yau nima Rebecca ina tare fake Bilkisu”.
“Nima ina tare daku” cewar Nazifa tana aza hannunta akan na Rebecca, Ummie da Zuhrah ma duk suka ɗora tare da bamu goyon baya.
Wannan shine sanadin burinmu, a haka muka ƙarasa jarabawar data rage tare da bikin karramawa da aka gudanar.
Ranar Dad da kansa yazo ɗaukata shi da Yah Qaseem.
Nayi farin cikin ganinsu, haka suma sun tayani farin ciki.
A gidanma nayi mamakin tarbar dana samu daga Mummy.
*_RAYUWA SABON TAKU!_*
.............Dole na kira yanayina na yanzu da suna rayuwa sabon taku, dan kuwa nazo da sabbin salon taka tsantsan a gidan, na sake komawa islamiyya, inda a kullum nake samu na leƙa Amina, duk da yanzu dai ta warke a jiki, sai dai ciwo a zuciya da kuma firgita da takeyi musamman idan taga maza kusa da ita dab. Ina tausaya mata, shiyyasa a kullum bana mantawa da ita a cikin addu'ata.
Ina fuskantar sabuwar tsangwama daga Mummy da Aamilah akan son da Yah Qaseem ke iƙirarin yanamin, wanda ni banma ɗaukesa a komaiba duk da naji zan iya zama dashi matsayin miji inhar da gaske auren nawa zaiyi, kuma bazance bana sonsaba, sai dai ban ƙwallafa rai ba, idan na samu zan amsa, idan saɓanin haka yazo zan zamto mai haƙuri.
Rashin Amina ya saka ayyuka da yawa na gidan dawowa a kaina, musamman gyaran sama ɗakin Mummy da Dad da falon saman, sai ko ɗakin Yah Qaseem daya wajabta min shima, da farko har Aamilah da Salman suma sun fara sani, amma sai Yah Qaseem yay magana akan karsu ƙara, matarsa ba ƴar aiki bace.
Harga ALLAH yaban dariyar wannan furuci, yayinda ya ƙona zuciyar Mummy harta yini bata amsa maganata tana fushi dani, Aamilah kam harda cewa wai Mummy ta bincikeni ina niyyar cinye mata kurwar ɗa, dama ta daɗe da zargin ni mayyace.
Ban damuba, danni yanzu a rayuwa mukuma ya rage ban ganiba? Sai dai zaman takewar aure da nakeji jama'a na kira da zaman haƙuri shima.
Kamar kullum yauma na tashi da wuri na kimtsa ɗakina nai wanka, na fito cikin doguwar baƙar riga zuwa kicin, kuku ne kawai keta kiciniyar ɗora breakfast, mun gaisa cikin mutuntawa na haɗa tea na fito falo.
Shi kaɗai nasha saboda sabon makaranta, yanzunma sai ban iya daurewa saina sha ɗin, dan breakfast ma saina ka sha biyu banyiba ko ƙarfe ɗaya.
Sallamar Yah Qaseem ce ta sakani ɗago idanu na, na kallesa ina amsa shi.
Yayi ƙyau cikin suit ɗin sosai, duk da baisa rigar saman ba tana riƙene a hannunsa.
Fuskarsa ɗauke da murmushi ya zauna a gefena dab, hakan ya sakani matsawa nikuma ina gaidashi.
Bai amsaba, sai tambaya daya jeho mani,
“K wai yaushe zakibar gidadanci ne? A zahiri dai ba Bilkisun da bace bagidajiya, amma a baɗini babu abinda ya canja na ƙauyancinta”.
Duk da maganarsa tamin zafi sai nai murmushi kawai, na cigaba da juya cokalin dake a kofin shayin ba tare dana bashi amsaba.
“Baki jinane?” ya sake min tambaya?.
Haɗiye takaicin daya tsayan a maƙoshi nayi naɗan kallesa na ɗauke ido lokaci guda saboda tsareni da yay da kallo, “Naji Yaya, sai dai kasani ni abinda nakeyi ba ƙauyanci bane ko gidadanci, hakan koyarwar addininmu ce, niba muharammarka bace, bamuda hurumin haɗuwar jikin juna a halin yanzu, kodan gujema sharrin shaiɗan mai saka wasuwasi a zukatan bayin ALLAH”.
Jikinsa ya kwantar a kujerar yana ɗan taɓe baki, yace, “Da haka ake cutarku ai dama ku kullum, shiyyasa hausawanmu sunfi kowa rashin wayewar kai, shikenan sai akace dan namiji ya zauna kusa da mace, koya kama hannunta, koya rungumeta wani abu zai faru?”.
Mamaki ya kamani jin furucinsa, sai bance komaiba na cigaba da juya cokalin a cikin shayina nidai.
Babu zato naji ya ɗora hannunsa a saman nawa yana faɗin, “Bani nasha ni”.
Ban sakar masaba, duk da jinake kamar na make hannunsa daya ɗoramin, nace, “Bari na haɗo maka wani to”.
“No barsa, wannanma ya wadatar, sai dai idan bakiso nashanye miki” Ya faɗa yana sake matsowa jikina.
Sakar masa kofin nai kawai na miƙe nabar masa kujerar, domin neman hanyar kuɓuta, ya bini da kallo harna shige kicin.
A ɗan lingun da zai sadani da kicin ɗin na tsaya ina roƙon UBANGIJI akan wannan rayuwar yahudanci, “Ya ALLAH ka kareni ka karemin martabata da mutuncina harna bar gidannan zuwa gidan aure na, ya rabbi ka hananeni saɓa maka bisa ganganci komin farin cikin da hakan zai sakani”.
Na haɗiye hawayen dake neman zubomin kafin na ida shiga kicin ɗin, na tarar kuku harya shirya masa abinci saboda shi yake fara fita a gidan kafin kowa.
Ɗauka kawai nai na kawo masa falon, na iske yana wayane yana shan tea ɗin daya amsa a hannuna.
Yanda yake wayar a zafafe yana ambatar sunan wani Jawaad ya sakani kallonsa, fuskarsa harta koma jaa saboda bala'i kasancewarsa farin mutum sosai.
Koda ya gama wayar tsaki yayta ja da ambaton sai ya kawo ƙarshen iskancin Jawaad ɗin.
Nidai bance dashi uffanba, na haɗa masa abincin na canza kujera can nesa dashi.
Bala'i na cin ransa bai wani ci abincin kirkiba ya tashi zai fice, gabana yazo ya ranƙwafo wai zaimin kiss, nai saurin kaucewa jikina har rawa yakeyi.
Wata banzar harara ya watsamin yana jan tsaki.
“K baƙauya karki ƙaramin ɓacin rai mana”.
Fuska na ɓata nima, nace, “ALLAH ya baka haƙuri Yaya, sai dai ina sake tuna maka bai daceba, kabari sai munyi aure”.
Bai tanka maniba ya fice abinsa yana sake jan wani wawan tsaki.
Nannauyar ajiyar zuciya na sauke ina harar bayansa, kai wlhy da sake, dolene nasan maiyuwa da wuri kafin wankin hula ya kaini dare a gidan nan.
Kayan da yaci abincin na tattare na gyara falon, na hau sama canma na gyara da ɗakin Mummy, dan tana ɗakin Dad tunda yana gari.
Sai da komai naga yamin fes sannan na fito harabar gidan tacan baya na zauna ina wani bincike ta waya.
Naja dogon lokaci a wajen kafin na shiga cikin gida saboda kiran Dad daya shigo min a waya.
A d/table na iskesu su duka, dan haka na fahimci dalilin kiran Dad.
Sai da na duƙa har ƙasa na gaishesu shi da Mummy sannan na gaida Aamilah da Salman lokacin da nake zama.
Anacin abincin ana hira, duk da dai babu bakina a ciki sai lokaci-lokaci, shima Dad ke sakoni a maganar na bashi amsa.
Bayan mun kammala ne Dad yace na sameshi sama zamuyi magana.
Duk da inata tunani akan wace magana haka na miƙe nabi bayansa.
Sai da ya zauna a kujera sannan nima na zauna a ƙasa, yace na koma kujera nima, amma saina bashi haƙuri akan nanma ya isa.
Murmushi kawai yayi yana gyara zamansa, idonsa a kaina yace, “Bilkisu nasan zakita mamakin wannan kira ko?”.
Kaina na jinjina masa ina bashi amsa da “Eh wlhy Dad, ALLAH dai yasa banyi laifi bane”.
“A'a bakiyi laifin komaiba mai gadon zinari, akan karatune dama, mizai hana da wannan zaman ki sake komawa makaranta kawai? Kinga saina turaki wajen yayarki Shahudah ko?”.
A zuciyata mamakin rayuwa irin ta Dad nake, maimakon yamin zancen aure amma kunji zancen cigaban karatu yakemin, duk da a yanzu ina cikin shekara ta ashirin da huɗu ne.......
Katsemin tunani yay da faɗin, “Karki ce zaki sakama ranki wata sakarar soyayyar Qaseem kinji, ki tsaya kiyi karatun da zaki tallafi rayuwarki koda bana raye, shi kansa zaifi ganin mutunci da kimarki, duka shekararkima nawa da har zaki sakama kanki maganar aure? Bakiga sakamakon da aure ya bama yayarki Shahudah ba, Rayuwar yau data jiya da mu mukai akwai banbanci kinji”.
Kaina na ɗaga masa ina murmushi, nace, “Dad dama ba aure nakeso ba, sai dai akwai wani buri a raina”.
Da sauri yace, “Wane burine haka ɗiyata?”............✍🏻
Page 34
...............Murmushi na sakeyi saboda yanda yaymin tambayar cikin zumuɗi, duk yanda zaiyi ka sake dashi dad ya sani, shiyyasa akwai shaƙuwa mai ƙarfi tsakaninsa da yaransa, kawai sakacine dai dashi wanda yake kallon hakan matsayin ƴancin kai.
“Dad bansan yaya zaka ɗauki zancenba, dan mutanenmu da yawa sukan ɗauki aikin matsayin bai dace da mace ba, sai dai ƙabilun nan suna shigasu, mune dai gaskiya akan daɗe babu ɗiyan bahaushe a ciki....”
“Kinga faɗamin kawai kanki tsaye, wane aikine?”.
“Dad aikin ƴan sanda, sonake na zama ƴar sanda inhar kana ganin ya dace nayi?”.
Kansa yaketa kaɗawa cikin murmushi, ya dafa kaina yana faɗin, “ALLAH yay miki albarka Bilkisu, wannan tunanine mai ƙyau kuwa, wanda ya kamata ace yaranmu mata suna irinsa koda cigabanmu, ina goyon bayanki ɗari bisa ɗari, sai dai kibari zan zaɓa miki wanda zaifi dacewa dake kinji ko?”.
Kaina na ɗaga masa ina jero masa godiya ta musamman, dan ina ganin fatana na zama ƴar sanda maisa kaki zai cika.
Ƴan sanda masu saka kaki yafi birgeni, aikin su Yah Qaseem bai cika birgeniba, dukda su ƴan sandane sunfi yin manyan ayyuka ba irin na ƴan sandan dana saniba masu fuskantar kowacce matsala musamman ma irin tamu ta cikin gidaje, to amma babu yanda zanyi, dan kimar Dad ta wuce nai masa musu koda a mafarkine, bazan dai taɓa masa biyayya akan abinda ya kauce shari'a ba, amma duk wanda ya zaɓamin zan amshesa matsayin zaɓin UBANGIJI na.
Ina dawowa ɗaki Number Ummie na kira na sanar mata yanda mukai da Dad, taji daɗi sosai, dan haka tace zata sanarma Dadyn ta dan yazo ya samu Dad akan batun, dan suma duk sun sanar a gida kuma an barsu, Zuhrah ce kawai aka hana itama tana kan lallaɓawa.
*_KANA NAKA ALLAH NA NASHI_*
Tabbas haka wannan batu yake, sanda kake tsara wancan sai kaga ba shine a kundin ƙaddararka ba, tunda tun farko bakai ka rubuta littafinba balle kai tunanin bin tsarin daka shirya ko zuciyarka tafi so.
Kwanaki uku dayin wannan magana da Dad sai ga Dadyn Ummie yazo gidan, wanda na lura dai yaron Dad ne, dan abubuwa da dama daya shafi karatun yaran gidan shine tsaye a kansa, hatta da aiki ko wani abu shi dad ke ɗorawa akan nemawa wanda duk yaso.
Bansan mi suka tattaunaba, na dai je mun gaisa, inda kamar yanda ya saba ya sakemin nasiha akan na kula da komai karna bari nai zirmawar da zanyi dana sani anan gaba.
Na riga na gahimci hannunka mai sandarsa, dan yasha faɗamin karna yarda nai koyi da tarbiyyar gidanmu, ba ƙaramin daɗi nakejiba kuwa da wannan kulawar tasa, shiyyasa a kullum nake sake ganin kimarsa da mutunci.
Nayi zaton ko Yah Qaseem zaice shi aure yakeso muyi baison na tafi wannan aikin, amma sai naji tsitt baice komaiba, sai dama akai kusan sati sannan yakemin tambaya akan maganar.
Koda na bashi amsa murna kawai ya tayani muka cigaba da wata hirar kuma.
Hakan sai ya bani mamaki, a shekarun Yah Qaseem ya cancanci buƙatar mace a kusa da shi, kumani ban taɓa kamashi da wata maceba ko ganin wani abu daya danganci mace a ɗakinsa balle nace yana neman mata, to minene matsalarsa? Dan a yanda yake nunamin dai ai yana buƙatar jin ɗumin macen.
Na kauda wannan tunanin a raina dan bashi da wani muhimmin amfanin da zai mini.
Su Aamilah kam dariya sukaita min, inajinta har aunty Shahudah ta kira ta sanarmawa itama tana tayasu.
Mummy dai batace komai akan batunba, amma naji wani furuci nata daya tsayamin a ƙahon zuciya, wanda na lura ita gani take kamar dan neman kusanci da yah Qaseem ne ya sakani son aikin.
Ni dai na tattara dukkan lamarina