Showing 66001 words to 69000 words out of 104658 words
Chapter 23 - Kwai Cikin Kaya Book 1 Hausa Novel Complete
abinda yaga yanayi da ƴar mutane.
Sai faman sinne kai yake yazo ya zauna a mazauninsa yanama Jawaad ɗin barka da zuwa.
Jawaad da bai tankashiba ya jeho masa tambaya mai rikitarwa,
“Wannan shine abinda kakeyi da ƴaƴan al'umma shiyyasa ka salwantar min da ciki?!!”.
Yanda Jawaad yay maganar a matuƙar kausashe ya saka jikin Doctor Tayyeb ɓari, bakinsa na rawa yace, “Yal...Yallaɓai wl... Wlhy kaji na rantse ban san komai akan maganar nanba, matarka ba zubar da cikinta taib.....”
Da ƙarfi Jawaad ya buga tebir ɗin gaban Doctor, wasu abubuwan suka zube, wasuko tsalle sukai suka canjama kansu muhallin zama.
“Mara mutunci, zaka cigaba damin wasan kwaikwayone kokuwa zaka sanarmin gaskiyar batu kafin na fasa ƙwalwarka da bindiga?!”.
Doctor Tayyeb daya manne da bayan kujera zufa na karyo masa ya share gumin goshinsa, “Yallaɓai please Calm dawn, wlhy bansan komaiba, yanda na musu bayani shine gaskiyar magana, mahaifartace bata da ƙwarin riƙe ciki.....”
Miƙewa Jawaad yayi yana wata ƴar dariya da tafa hannayensa, ya tako zuwa gaban kujerar da Dr Tayyeb yake, a saman tebir ɗin ya zauna suna fuskantar juna, ya ajiye ƴar ƙaramar bindigarsa daya ciro a aljihu ya ajiye gefrnsa.
Wani mugun yawu Dr Tayeeb ya haɗiya idonsa akan bindigar, Jawaad ya katsesa da faɗin, “Wannan itace tambayar ƙarshe dazan maka, ya rage naka ka bani amsa dai-dai kokuma ka sakemin ƙarya. Miyasa kabi ra'ayinta ka zubarmin da ciki?”.
Doctor dake lafe jikin kujera tamkar magen datai karo da kura a daji ya haɗiye wani yawu mai kauri idonsa akan bindigar Jawaad daya ɗauka yake jujjuyata a hannu, tabbas yasan Jawaad zai iya aikata komai, shiko da baida laifi gara ya fidda kansa a cikin wannan bala'in tunkan kwaɓarsa tai ruwa, saboda kuɗin Aamilah bazai halaka kansa ba a wofi.
“Yallaɓai kayi haƙuri ka ajiye bindugar na rantse duk abinda kake buƙata zan sanar maka shi”.
Cikin wani salo da murmushin mugunta Jawaad yasa ɗanyatsa ya tura eyeglasess ɗinsa sosai yana faɗin, “Good boy, ashe kasan dokar”.
“Sosaima kuwa yallaɓai” Dr Tayyeb ya faɗa yana jinjina kai tamkar ƙadangaren jangwala gwaja yaga shinkafar manja🤪.
Ajiye bindigar Jawaad yay yana ranƙwafowa kaɗan hannayensa harɗe a cinyarsa da yake zaune da ita a tebir ɗin, ɗayar kuwa tana ƙasane a jiye, “Ina saurarenka”.
Nanma kai Doctor ya jinjina masa, “Maganar gaskiya yallaɓai lafiyar mahaifarta ƙalau, zubar da cikin akai, sai dai wlhy kaji na rantse maka bani nai mata aikinba, andai kiranine kawai na ceto rayuwarta”.
Sosai zuciyar Jawaad ke tsitstsinkewa, ya zare glasess din idonsa yana zuba ma Doctor wani hargitsatstsen kalo, “Uhmyim, wato zubarwa akai? Amma miyasa ka zaɓi faɗar abinda ba haka yakeba? Haka aikinka ya koya maka?”.
“Wlhy A'a yallaɓai, kuskurene ka gafarceni”.
Sauka Jawaad yay daga saman tebir ɗin yana taku a hankali yana faɗin, “Maybe na iya yin hakan idan na tabbatar babu saka hannunka a ciki”.
“Wlhy da gaske nake babu hannuna, bankuma san komai a kaiba”.
Komawa Jawaad yay ainahin kujerar daya fara zama ya zauna, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana aza hannunsa ɗaya a tebir ɗin yace, “Doctor Tayyeb ka sanni na sanka tun lokacin daka fara aiki gidan Alhaji Ali, karka kuskura a wannan karon ka tsinci kanka a harƙallata, dan wlhy bazan maka ragiba, na kamaka da ƙaryar farko ta faɗar sakamakon abinda ba haka yakeba, kasa a ranka ba'a min ƙarya a shani a banza, yanzu zan tafi, a koda yaushe kuma zan iya nemanka a office ɗina, zaɓin kane kazo akan lokaci koka ɓatamin lokacin”.
“Insha ALLAH zanzo yallaɓai, kuma bazan sake kuskuren maka ƙaryaba akan duk abinda zaka tuhumeni a kansa”.
“Good” Jawaad ya faɗa yana miƙewa da ƙoƙarin tura bindigarsa ta baya, bai kuma tankama Doctor Tayyeb ba ya fice a office ɗin.
Bai cema su Gimba komaiba yay gaba suka sake rufa masa baya har inda suka ajiye motocinsu, buɗe masa akai yanzunma ya shiga ya zauna sannan suma duk suka shiga suka bar asibitin a sukwane.
Haɗiyar zuciya kawai Jawaad keta faman yi, shi kaɗai yasan mi yakeji da yanda ƙirjinsa ke zaɓalɓalar azabar kunar zuciya, shi Shahudah ta zubarma ciki dukda gargaɗin ta da yay akan karta aikata hakan?.
Doctor dai tunda Jawaad ya fice saiya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana share gumi, mikewa yay yaɗan leƙa kansa ta ƙofar da Jawaad bai rufe da ƙyauba, sai da ya hango sun fice sannan ya sauke numfashi yana tura ƙofar ya murza key ya koma jikinta ya lafe yana rumtse ido hannunsa dafe da ƙirjinsa.
A ransa yana ayyana tsaurin ido da tsantsar kwarjinin Jawaad, a fili ya furta, “Tabɗi, waɗannan ai sune mazajen gaskiya”.
😂🤣Su Doctor Tayyeb ashe mata mazane bamu da labari😝.
★★★★★
Ko a Office ma da suka isa kowa yau a miskile yaga Jawaad, duk da babu wani ɓacin rai a fuskarsa ko nuna damuwa.
Ya shige Office abinsa, kusan mintuna biyar ya aiko ai masa kiran Aliyu.
Babu ɓata lokaci Aliyu ya amsa kiransa da gaggawa, bayan sun gaisa cikin musabaha Jawaad ya miƙama Aliyu ledar daya ɗakko sirinjin jiya a gidansu Shahudah yana faɗin, “Inason nasan hoton yatsun wanene a jikin Syringe ɗinnan Aliyu yanzun nan”.
Cikin girmamawa Aliyu ya amsa yana faɗin, “Okey Boss, ka bani nanda mintuna Arba'in koma ƙasa da haka”.
Hannu kawai Jawaad ya ɗaga masa ba tare da yace komaiba, Aliyu ya fice shikuma ya shiga wata sabgar daban.
Kusan awa ɗaya sai ga Aliyu ya dawo, sai da ya nema afuwar Jawaad na daɗewar da yayi sannan ya zauna yana miƙa masa ledan da syringe ɗin yake ciki da sakamakon binciken, amsa Jawaad ɗin yayi da faɗin, “Thanks my Dude”.
“Babu godiya a tsakaninmu, amma akan case ɗin miye?”.
Murmushi Jawaad yay masa yana cigaba da duba takardun gabansa, yace, “Share kawai Aliy gadanga ƙusar yaƙi, su Hafiz fa?”.
Kaɗa kai kawai Aliyun yayi, bai matsa akan sai yaji ba, yace, “Hafeez da Rose inaga suna kan aikin nan, Jabeer kuma yana Office”.
“Okey, nima kam inaga zuwa yamma zan ziyarci anguwar can, dan yakamata muɗan fara motsi akan case ɗin nan, tunda ALLAH yasa munga ƙarshen wannan, saura shiga Court kawai ya rage”.
“Okey to ALLAH ya bamu nasara shima, amma wannan aikin na lura kamar zai zama na basaja ne shi?”.
Idanu Jawaad ya ɗago yana kallon Aliyu sosai, ya lashi leɓensa na ƙasa daya bushe sannan ya turasa cikin baki sai kuma ya biddosa yana janye idanunsa daga kan Aliyun murmushi kwance a fuskarsa yana faɗin, “Wani zai zama mai sana'ar kifi kenan”.
Dariya Aliyu yayi, “Kai haba boss? Wannan lokacin kuma tanan ka ɓillo?”.
Cikin taɓe baki Jawaad yace, “Mutanen duniyarne sai ka musu duniyanci kuke zama ku mori duniyar tare”.
“Hakane kam boss, kenan yau akwai zama?”.
“Eto bance a'a ba, amma da kamar wuya, dan akwai wani rami na cikin gida da nima nakeson cikewa, maybe zaku bani yau kawai na ƙarasa”.
“Ai ya zama dole Boss, ALLAH ya bada sa'ar cikosa da alkairi to”.
“Amin” kawai Jay ya faɗa yana haɗiye ɗacin daya riƙe masa maƙoshi.
Daga nan Aliyu yay masa sallama ya fita.
Kusan mintuna ashirin da fitarsa Jawaad ya ɗau ƙaramar wayarsa yay kiran Doctor Tayyeb, yana ɗagawa yace yazo ya samesa a Office.
Bai bashi damar faɗar komaiba ya yanke wayar.
Kamar yanda Jawaad yay Warning ɗinsa bai ɓata lokaciba ya iso kuwa, Gimba ne ya kawosa har Office ɗin, Jawaad daketa faman aiki da Computer baiko motsaba balle ya kallesu har Doctor Tayyeb ya zauna.
Sai da kusan mintuna biyu suka shuɗene ya fara magana ba tare da yabar aikin da yakeyiba.
“Kasan wane aiki zakai min?”.
“A'a yallaɓai sai ka faɗa”.
Jawaad yaɗan kallesa sai kuma ya maida kansa ga aikinsa yana cigaba da faɗin, “Yatsun hannun duk jama'ar gidan Alhaji Ali nake buƙata amma banda Qaseem da shi Alhaji Alin, ya rage naka kabi ta hanyar da ya dace ka aikata, kokuma kayi rawar kai ni kuma na ragargaza maka kwanya babu ruwana”.
Cikin haɗiye yawu Doctor yace, “Wannan mai sauƙine mai gida”.
“Na fika sanin sauƙinsa, dan danaso zanje kai tsayene na nema basai nabi ta hanyar kowaba, inada nawa dalilin sakoka cikin aikinne kawai”.
Ba ƙaramin faɗuwar gaba Doctor yajiba, ya hadiye yawu daƙyar yana fiddo idanu kamar kwarton da mai gida ya kama da farar magriba😑.
Jawaad yace, “Karka tsaya kallona, lokacinka ya fara daga yanzun”.
Mikewa Doctor Tayyeb yayi yay masa sallama ya fice........
_______________________________
Idan nace muku ban fara ganin canji a rayuwata ba nayi ƙarya, dan kuwa ilimi tubaline mai ɗaga darajar kowanne mai fafutukar nemansa, idan kaga saɓanin cikagabanka a cikinsa to lallai bakabi hanyar data daceba wajen samunsa.
Kasancewar su Ummie manyan yarane wayayyu, wayewa kuma mai tsafta tuni sun fara dorani bisa layi, musamman salo-salo na tsaftace jiki dana tsara rayuwa inhar kanada ikon ribantar gobenka.
Tabbas ni baƙace, amma na yarda jin daɗi kan saka koda kai bakine baƙin ya kasance na musamman mai ɗaukar hankalin idanun mai kallonka.
A yanayin da nake ciki da sauyin iska dana fara samu tun a gidan Dad sai suka sake tasiri a yanzu a gareni, gashi dai makaranta muke, makarantarma Boarding skull, sai dai ta kasance ta musamman, dan banbancinta da rayuwar gidanma ƙalilance, anan kawai dai baka ganin iyayenka ne bakuma a ganin gari da jama'a, tunda a killace muke.
A hankali aka fara sanina saboda su Ummie ƴan babu sauƙine, guruf ɗinsu sanannen guruf ne ko a cikin ƴan mate ɗinsu, musamman saboda ƙokarinsu da kwazo da ALLAH ya basu, kowanne zakaga gwarzone a wani subject, hakan yasa har malam ma ji suke dasu ainun.
To sai shigata cikinsu nima ta kuma ƙarfafa fahimtata da tun a baya rashin gatan samun gurbin karatu mai ƙyau ya raunanashi.
Ba karatu kaɗai ba, dai-dai da yanda ake tafiya, saka sutura zuwa magana babu abinda su Ummie basa koyamin, ni wani lokacin ma har mamaki sukeba su a ina suka koyo?.
Sam bana nuna wani girmankai a garesu balle turjiya, komai sukace nayi inhar nasan bai saɓa shari'a ba ko taɓa tarbiyyar al'adata nakan amshesa hannu biyu na riƙe na kuma bada himma wajen fahimtarsa.
A hankali komaina ya cigaba da canjawa ga jarabawa nata gabatomu wadda zuwa yanzu ko fargaba banaji akan zuwanta, dan inada yakinin insha ALLAHU nima za'a goga dani a filin dagar.
Turanci kam yanda yake zama min akan harshe zakasha matuƙar mamaki da tunanin tun inada ƙuruciya dashi na tashi a baki, tsoron mutane da kuka sanni dashi zuwa yanzunkam ya fara guduwa, dan jina nake a gaban kowa zan iya fita a dama dani akan abinda ya kamata.
Sai dai kunya dake ƙara martaba kimar mace a koda yaushe tana nan daram a jikina da ayyukana bata fitaba, hatta wani abun idan su Ummie sukai nakanji nauyinsa harma na kasa saka baki ko kaina a ciki, sukan tasani da dariya sosai harsu koma tsokanata.
Bazance har yanzu Nazifa ta saki jiki daniba, amma dai bata ɗaukata da zafi kamar da.
Akwai malami da Dadyn Ummie ya ajiye mana yake zuwa duk yamma ta fannin ilimin addini, hakanne ya sakani fahimtar abinda ya zaunar da tarbiyyar su Ummie akan tsari ba tare da wayewarsu ta zarce ƙa'idar da addini ya shinfiɗaba.
Lallai ako ina inhar kanason ribantar ilimi toka ɗauki duka biyu ka riƙe, inhar da ililin addini to babu yanda za'ai ilimin boko ya dilmiyaka koyi da nasara kamar yanda naga su Aunty Shahudah sun zarma.
Wayewar mai riƙe da ilimin addini dana zamani a duk inda take dolene ta burgeka, dan zaka ganta cike da tsafta da nutsuwa babu shirme ko rawar kai a ciki.
ALLAH ka bamu ikon cin ribar ilimi a duniya da kuma lahira ba mucinye rabonmu anan duniya ba.
Zuwa yanzun kam inajin kewar gida, a duk lokacin kuma da sabbin ƙawayena suke bada labarin ahalinsu nima nakan bada labarin rayuwatane da iyayena ta gidan haya.
Sukanyi mamaki sosai, dansu sam basu taɓa tunanin ana samun makamanciyar wannan rayuwarba.
Nakanyi murmushi dan bana ganin laifinsu sam, a yanda rayuwa da duniya suka rainesu bazama su kawoma kansu tunanin akwai masu bukatar koda kwatankwacin irin tasu rayuwarba.
A koda yaushe sukan shiga damuwa da tsantsar tausayina harma da waɗanda suke da irin tawa rayuwar koma wadda ta fita, har zumuɗi suke na basu labari, sannan suna kuma ɗaukama kansu alƙawarin zamu zama masu taimakon wasunmu muma anan gaba da izinin ALLAH.
Gaskiya rayuwarsu na birgeni, dukda kasancewarsu ƴan gata iyayensu sunyi ƙoƙarin tsayawa tarbiyyarsu, ta waɗanda keda rauni a cikinsu kuma sun hadu sun daidaitata akan ƙyaƙyƙyawan bigire da shima zai amfana tun ba yanzuba, dan sun tabbatarmin tun daga js1 suke tare a makarantar, hakannema ya dasa shaƙuwa mai yawa a tsakaninsu harma da ƙulluwar zumin iyayensu, ƴar uwar Ummie data rasu na maye gurbin data bari sam basa iya mantata, kullum cikin bani labarinta da ƙyawawan dabi'unta suke, hakanne yasani fahimtarma dukta fisu zurfin ilimin addini da ƙulafucin kulawa dashi.
Wannan itace matakin na sara ta farko da ni BILKEESU ADAM MAKAHO na fara tsinta a duniyar da a baya nake kallon bata bukatar bani filin dazan zuƙi iskar cikinta a baya.............🤩✍🏻
Page 26
............Shahudah taɗan samu sauƙi, sai dai fargabar Jawaad ta hanata sukuni sam, gashi a yau ko ƙeyarsa basu ganiba a gidan, tanason kiransa a waya tanajin tsoro.
Kusan ƙarfe uku na rana sai ga Doctor Tayyeb yazo gidan, lokacin duk suna falo, Qaseem ne kawai babu a gidan dan yana Office wajen aiki.
Shahudah na kwance ne a kujera doguwa kanta a kan cinyar Mummy, karenta na kwance daga ƙasa kusa da ita, sai Aamilah da Jack da Salma waɗanda shigowarsu gidan kenan.
Sai da Dr Tayyeb ya bama su Salman hannu suka gaisa sannan ya zauna yana gaida Mummy idonsa akan Shahudah da keta ɓata rai, dan tasan allura yazo yay mata ita kuma batason ta.
“My patient yaya jiki?” ‘Ya faɗa yana mata murmushin yaƙe’.
“Fine” kawai tace masa ta ɗauke kanta.
Bai damu ba yace, “Alhmdllh, yanzu dai babu ciwon marar ko?”.
Kanta kawai ta ɗaga masa.
Shima bai sake cewa komaiba ya shiga haɗa allurar da zai mata, ƙasan zuciyarsa yana tunanin ta yanda zai ɓilloma aikin Jawaad.
Da ƙyar Shahudah ta tsaya akai mata wannan allura, saboda tsabar taɓara harda kukanta.
Sai da ta koma dai-dai ne ya gyara zama yana mata bayanin yanda zata kula da kanta, ya fiddo wasu ƴan kwalaben magani, ɗaya ya miƙama Salman dake kusa dashi yana faɗin, “Salman ko kasan wannan maganin?”.
Karɓa Salman yayi yana dubawa, Dr Tayyeb ya sake ɗibar biyu ya mikama Aamilah da Jack suma, “Kuma ku duba kuga ko kun sanshi”.
Suma basu musaba suka amsa, itama Mummy da Shahudah duk ya miƙa musu, da farko dai Shahudah kam taƙi amsa, a cewarta karya isheta.
Mi kuma ta tuna oho mata, sai ta miƙo hannu ta amsa.
Salman da Aamilah suka fara maido masa da kwalaben suna faɗin sudai bama su gane kan maganinba, kwalayen kwalaben ya miƙa musu duk suka saka da kansu sannan ya amsa ya maida ajikka.
Jack ya kalli Dr Tayyeb cikin nuna shiɗin ƙwararrene yace, “Wannan ai maganin hana ɗaukar cikine, macen da bata haihuwama akan bata ta gwada shi kamar na wasu wattani kafin ta dakata”.
Murmushi Dr Tayyeb yayi yana jin jina kai alamar gamsuwa da bayanin jack, ya miƙa masa kwalin shima ya saka yana faɗin, “A lallai kasan magani kam sosai”.
Jack yaji daɗin yabon da ake masa ya miƙama Doctor bayan ya saka a kwalin yana sake bajewa a kujera, suma su Shahudah duk basu yay suka saka ita da Mummy ya amshe abunsa ya maida duka a jaka, ba tare daya yi musu wani ƙarin bayani ba yay musu sallama ya tafi.
Kaf ɗinsu babu wanda ya kawo wani abu a ransa game da maganin da Doctor Tayyeb ya nuna musu, garama Mummy taji haushinsa sosai, dan ita gani take kawai Doctor ɗin nasu yayi hakanne danya nunama Shahudah hanyar ɗaukar mataki a gaba, itako yanda suka tsara yanzu nanda kwanaki kaɗan Shahudah zata koma ɗakinta ko ALLAH zaisa a dace wani cikin ya shiga.
Dan jiya dai ta daure taje gida tama Mama Atika da ƴan uwanta bayani akan matsalar Shahudah ɗin.
Dukansu sun nuna rashin jin daɗinsu da tausayin Shahudah, sai dai kuma hankalinsu ya tashi, dan a ganinsu inhar Shahudah nada wannan matsalar to kenan yaushene ciki zai fara zaman da zasu sami cikar burinsu?.
Uncle Uwaisu daya kasa haƙuri sai cewa yay, “Anya kuwa kuna ganin bazamu ɗauki matakiba? Indai hakanefa zaman Shahudah da Jawaad bazai mana wani amfaniba kenan? Ko dai mu sake dubawa cikin yaran nan saimu aura masa wata?”.
Tsitt falon yayi kowa ya kasa magana, sai dai fuskar Mummy ta nuna alamun ɓacin rai.
Mama