Showing 90001 words to 93000 words out of 104658 words

Chapter 31 - Kwai Cikin Kaya Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

206

a hannun mahaliccina, domin yafi kowa sanin mike raina .
      Nakuma cigaba da miƙa kukana a garesa da fatan dacewa idan har aikin alkairine a garemu, idan ba alkairi bane ALLAH ya canjamana da wanda zai zama alkairi.
         kusan wata guda babu wani bayani daga Dad ko dadyn Ummie, dan dad ma har yayi tafiyar sati uku yaje ya dawo.
     Sai ranar kwatsam na dawo islamiyya na iske Dadyn Ummie da Ummien kanta a gidanmu. Muka rungume juna muna farin ciki, sannan naja hannunta muka shige ɗakina.
        Itace ta fara gumtsamin abinda ya kawosu gidan, tuni farin ciki ya mamaye min zuciya, muka sake rungume juna, kiran Dad ya sakani sakinta muka tafi falonsa tare.
      Na gaida Dadyn Ummie bayan mun zauna, Dad ya miƙomin takardun hannunsa dake tabbatar da an ɗaukemu zamuje training, harda ƴar ƙwallata ta murna tamkarma ance mun zama ƴan sandan.
       Su dad nata min dariya, duk da dai ba ɗan sandan danai fatar zama bane wannan ma nayi farin ciki dashi, naji a jikina shine alkairi a gareni shiyyasa ALLAH yay min canji dashi.
      Mun taso zamu fita naji Dadyn Ummie na faɗin, “Wlhy nayi mamakin hakan Alhaji, dan ban taɓa zaton Jawaad zai iya aikatawaba, kamar yanda na faɗa maka shine yayta ƙoƙarin ganin takardun yarannan sun shiga duka wlhy, musamman dayaji nace saƙon nakane.....”
     Banji amsar da Dad ya bashiba muka ida ficewa, ina mamakin wanene wannan Jawaad da ake yawan faɗar sunansa a gidannan? Sai kuma labarin da Amina ta bani akan Aunty Shahudah da mijinta ya faɗomin a rai, to kodai mijin aunty Shahudah ne? To amma miyasa Yah Qaseem ya tsanesa matuƙa? Bani da mai bani amsa dan haka na kauda zancen a raina kawai muka cigaba da hirarmu da Ummie.


*_INDA RAI! DA RABO_*

         Lallaikam inda rai da rabo inji masu iya magana, to nima dai Bilkisu yanzu na shaida hakan, dan kuwa yau gani cikin jerin waɗanda ake horaswa na hukumar ƴan sandan farin kaya a cikin (Training center) ɗinsu, tare da ƙawayena huɗu a karo na  uku.
         Duk yanda zan fasalta abun ba lallai ku fahimta ba, amma al'amarin ɗanba sauƙine, anji jiki kafin ƙashi da tsoka su saba, yayin da ƙarfin jini da karsashin zuciya ke ƙara yawaita, babu babban maicin ribar abu irin maiyinsa da yaƙini ko fushin son maida murtani.
     Nayi imani da hakan ya taimakama ƙwazonmu sosai ni da ƴan uwana, dan kuwa matakin farko na nasara damu aka shallakesa, kamar wasa sai gamu a mataki na biyu, inda mataki na uku ya kasance na masu babbar nasara, dan kuwa a cikin waɗanda muka shigo wajen mu sama da dubu biyu bamu wuce mutum dubu ɗaya da ɗari uku muka shallakeba, a kuma cikin dubun muka kasance mafiya ƙwazo mu ɗari uku da ashirin, cikin 300 ɗinan aka kuma rairayemu mu saba'in, mu goma sha uku ne kawai mata a cikin saba'in ɗinan, sauran duk sun kasance mazane, cikin amincin ALLAH kuma ko ina ina tare da ƙawayena.
         Mu 70 ɗinnan an waremu domin samun horo na musamman fiye da sauran ƴan uwanmu, ƙwazon da muke nunawa da juriya ya samu fita cikin ƴan rukunin farko kenan.
      
        A haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa har suka rikiɗe zuwa watanni, inda cikin amincin UBANGIJI muka cika dikkan shariɗɗan zamowa cikakkun ma'aikata abin alfahari.
      Tabbas wannan nasara da muka samu munyi matuƙar farin ciki da ita, ranar kuma nasha kuka saboda tunowa da iyayena da siraɗin rayuwa dana tsallake batare da hasashen kaiwa wannan matsayinba na yanzu.
      Shiyyasa akace babu maraya sai rago, wannan magana tabbas haka take.

★★★★★★

         Ranar data kasance ranar yayemu ta zamto rana mai daraja da zuciya bazata iya mantawaba, dukanmu muna cikin Uniform da suka ƙara mana kwarjini da cikar kamala, inda manyan baƙi da manyan wannan hukuma sukai jawabai masu nuna ƙwarin gwiwa a garemu da fatan alkairi, sai ƙyaututtukan karramawa da suka biyo baya na ɗalibai mafiya ƙwazo a cikinmu inda sunana ya fito a bazata.
       Wannan abu ya sakani ɗunbin mamaki da al'ajabi, dan ban taɓa kawo hakan a rainaba koda a mafarkina, dan ni kaɗaice mace a cikin waɗanda suka samu wannan karramawa.
          Dad yaji daɗi sosai, hakama Yah Qaseem, su Mummy ma dai dayake duk hardasu akazo sun tayani murna koda bata kai har cikin zukatansuba.
         Daga ƙarshe kowannenmu ya samu takardar tabbatuwarsa ma'aikaci tare da inda aka turaka, matakin karatu ya matuƙar taimaka mana wajen tsintar kai ba'a matsayi mafi ƙaranci ba, dan kuwa bamu kasance matakin ƙarsheba.
      Mun rungume juna mu dasu Zuhrah muna kuka, dan kuwa dai an samu matsala wajen rarrabamu bazamu kasance a waje ɗayaba, kowanne da inda aka cillashi, ni da Ummie ne kawai a waje ɗaya.
      Sosai hakan ya taɓa zukatanmu, har sai da iyayenmu suka koma lallashi da nuna mana ai dama aikin kenan, wannan ba makaranta bace balle muce tilas mu kasance a zaɓinmu.

★★★★★★★

         Sati guda cif da gudanar da bikin yayemu muka shiga filin daga, yau sai ga Bilkisu Adam makaho matsayin ƴar sanda ta hukumar DSS, Yah Qaseem shine ya zamemana fitila a komanmu ni da Ummie, duk da kasancewarsa babba a wannan hukuma.
      Aikin farko da muka fita Ummie tayisa cike da tsoro, ni naita ƙarfafa mata Gwiwa har itama ta samu ƙarfin zuciya, a cikin kwanakin da basu gaza sittin ba, waɗanda a jimlace zasu baka wata biyu mun gama gogewa, muma munaji a ranmu mun isa karanmu yakai tsaiko.............✍🏻


Akwai sauran pages 6 a ƙasa, nima sai naga ana zabga mana ruwan subscribing sannan zan sakesu🙄😂, waɗanda sukai mana sub... Muna godiya, ALLAH yabar zuminci, kuma nayi farin ciki dan duk wanda yayi na gashi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Page 35

............Yau safiyar Laraba muka tashi da labarin dawowar wasu manyan jami'ai na wannan hukuma tamu kamar yanda manyanmu suka sanar.
       Na kasance a cikin tawagar masu zuwa tarbarsu da aka ɗiba a cikin mu ƙananun ma'aikata, akwai kuma manyanma.
     Hakanne ya tabbatar mana lallai waɗanda zamuje tarar sunada muhimmanci a wannan hukuma. Haka kawai na tsinci kaina da faɗuwar gaba, zuciyata sai wani irin zallo take kamar zata faɗo ƙasa.
      Ƙirjina na dafe ina lumshe idanu, dama tun jiya nakejin tamkar wani gagarumin abu na kusanto rayuwata, sai dai bansan minene ɗinba.
       Mun iso airport ɗin akan lokaci, dan jirginma bai kai ga saukaba sai nan da minti arba'in kamar yanda aka sanar damu.
         A yanda mutane suke kallonmu musamman ma mu matan da muka kasance mu biyu kacal yasa duk na takura, sanye muke da Uniform wanda ni kaina nasan sunma surata matuƙar ƙyau, tabbas bani da ƙyawu mai tsanani amma ALLAH ya azurtani da ƙyaƙyƙyawar  surar dake da wahalar samu ko a cikin matanma, wadda itace ke fisgar maza da yawa a gareni, akwai baby hijjab dana saka kafin na ɗora hular Uniform ɗin a saman kaina, hakan ne zai baka amsar kasancewata musulma kai tsaye.
       Addu'a na rinƙayi a zuciyata, saima na saka eyeglasess a idona saboda kallon ya gundunreni.
           Adadin mintuna na cika jirgin da muke tabbacin jira ya iso, saida  ya gama shawagi a sama kafin ya sauka a inda ya dace, wannan shine karon farko da nazo airport a rayuwata, hakan ya sakani tsarkake sunan UBANGIJI daya sanya fasaha ga zukatan waɗanda suka ƙera jirgi, sannan ya bashi ikon tashi sama duk da girman da yake dashi.
        Bugun zuciyata ya sake sauya salon bugawa da sauri-sauri, hakan ya sakani rumtse idanu dukkan jikina na wata irin tsuma, haka kawai sai nakejin kamar na kama kuka.
         Taɓanin da akaine ya sakani buɗe ido da sauri, ɗaya daga cikin ma'aikacinmu ne da yake nema takurama rayuwata, na kallesa ina ɗauke kaina dan haushi yake bani, shi a dole wai sona yake, tun a wajen training ya maƙalemin, sai kuma akai rashin sa'a muka tsinci kanmu a waje guda.
        Ganin ya gyara tsayuwa zai fara magana nai gaba abuna. Dai-dai fasinjojin jirgin sun fara fitowa.
     Duk wanda ya fito a jirgin idonmu a kansane, sai dai ganin babu wanda ya motsa daga jami'anmu ya tabbatarmin namu tawagar basu fitoba har lokacin.
      Sai da kowa ya gama fitowa har babu alamar sauran mutane kafin wata mata da yara biyu ta fito, sai wata kuma a bayanta ita riƙe da hannun yaro namiji, sai wata na biye musu baya itama.
        Suma sai da suka sauka duka sannan sannan fitowar wani sadauki da tai daidai da tsananta bugun ƙirjina ya fito.
     Zaratan mazaje uku da doguwa budurwa na biye dashi a baya.
       Jinai ƙafafuna na neman gaza ɗaukata, hakan yasani saurin jingina da ɗaya a cikin motocinmu gudun karna faɗi.

       Jawaad dake fitowa ya sauke idanunsa akan sir Ahmad barewa, kafin yaci gaba da bin ma'aikatan tadabbaci ke nuna sunzo tarbarsu ne.
     Kansa tsaye inda su sir Ahmad da wasu manya suke suka nufa, inda shima Sir Ahmad ɗin ya nufesu fuskarsa cike da fara'a da farin cikin ganinsu.
        Gaba ɗaya sauran ma'aikatan sukaja layi alamar girmamawa, miƙewa nai ina sauke numfashi tamkar wadda tai gudun fanfalaƙe.
      Sai da ya gama gaisawa da manyansa kafin su nufomu su dukasu.
      A tare muka buga ƙafafu tare da yin salute nasu cikin nuna tsantsar girmamawa.
    
      Jawaad dake tsaye yana ƙare musu kallo idonsa ya sauka kan matashiyar budurwa mai hijjab.
     Ganin ya tsura mata idanu Jabeer da suke bayansa yay mata umarni data cire glasses ɗin idonta a ɗan kausashe.
         Kawai jinai idanuna sun cika da ƙwallan da bansan dalilinsu ba, na zare eyeglasess ɗin idona kamar yanda aka umarceni tsigar jikina na wani irin tashi tamkar nai gamo da halittar ban tsoro.
      Babu zato idanuna suka shige cikin nashi idanun masu wani sinadarin da baki bazai iya faɗaɗa bayani akaiba.
     Kasa jurewa nai na janye nawa ina rissinar da kaina tamkar zuciyata zata faɗo ƙasa.
       Shima cikin basarwa ya janye nasa idanun cikin wani salo na halin ko in kula.
      Sai da ya gama ƙare mana kallo mu duka kafin yay guntun murmushin daya saka kumatunsa loɓawa.
     Saitin inda nake yay mana nuni da hannu alamar mu bashi hanya, hakan ya sakamu darewa muka rabu biyu ya gittamu ya wuce, mayen ƙamshin turarensa na rige-rigen shiga ƙofofin hancinanmu.
       Da sauri wasu a cikinmu suka nufi motocin suka bubbuɗe musu har manyan mu da mukazo tare wajen, ni dai bamma iya koda motsiba daga inda nake, saboda bani da wani ƙarfi sam balle samun kuzarin yin abinda ya dace.
       Sai dai idona akan motar daya shiga shi kaɗai baya aka maida aka rufe masa, haka kawai naji tamkar ana kallona, kallo kuma irin na ƙurilla, sai dai iya dube-dubena banga alamun kowa da idonsa ke kainaba, saboda mutane sunata hada-hadarsu ne.
    Hannu na ɗora a hankali bisa ƙirjina dai-dai saitin zuciyata ina lumshe idanu, wasu ƙananun hawaye suka silalomin a kan kumatu, saurin jan hulata nai sosai yanda zata hana kowa kallon halin da nake ciki kafin nasa handkherchief na share cikin dabara ina nufar mota nima.
     
       Jawaad da tunda ya shiga mota idonsa ke akanta yana ƙare mata kallon da shima baisan dalilinsa ba ya lumshe idanu yana huro iska ta ƙofofin hancin, kuma buɗewa yay sai yaga wayam babu ita a wajen, cikin halin ko in kula yaɗan taɓe baki yana ɗauke idanunsa daga kallon wajen ma baki ɗaya ya maida ga wayarsa.

         Tanda muka fara tafiya nake jerama kaina tambayiyin da bansan amsarsu ba.
       “Miyasa nakejin tsoro? Miyasa yay min kwarjini fiye da kowa? Miya sakani kuka? Minene ma'anar halin dana shiga bayan banida wata alaƙa da wani abu daya taɓa shafar irin wannan yanayin dana tsinci kaina a ciki balle nace na tunashine?”.
      Waɗanan tambayoyi su naita jerama kaina har muka iso, tarbar da muka iske an shirya musu ananma ce ta sakani samun damar zare jiki na koma can gefe na zauna ina maida numfashi da addu'ar samun daidaituwar wannan baƙon yanayi nawa da baida alaƙa da komai.
       Dafanin da akayine ya sakani juyowa, Ummie ce, hakan yasa tana zama sai kawai na fashe mata da kuka.
       Ɗunbin mamaki ya bayyana a fuskar Ummie, tai kasaƙe tana kallona tamkar wata sokuwa,
      “Bily lafiyarki kuwa?”.
Ban bata amsaba, saima ƙarfin kukana dana ƙara, tai shiru kawai ta sakamin ido, saida nayi mai isata nai shiru dan kaina sannan ta sake jefamin tambaya.
       “Bilkisu mike faruwa ne wai? Ko an miki wani abune da kuka tafi?”.
      Kaina na girgiza mata alamar “A'a”.
    Tace, “To minene ya faru? Ko baki da lafiya ne?”.
       “Lafiyata ƙƙalau kawai na tuna su babane” na samu kaina da mata ƙarya batare danasan dalilin hakanba, dan nasan bama ɓoyema juna abu sam.
       Numfashi ta sauke tana dafani, cikin tausasa murya ta shiga lallashina damin nasihar addu'a su baba ke buƙata bawai kukana ba.
      Kaina na ɗaga mata kafin nace, “Nagode Ummie, insha ALLAH bazan sake yiba”.
     Tai murmushi tana canja akalar firar tamu zuwa wata,
       “Kutt Bily basawannan namu da kuka tarofa sunji gishiri da magi, musamman mai green ɗin Suit ɗinnan”.
       Gabana ya sake faɗuwa jin ta ambacesa, amma saina danne cikin ƙaƙaro murmushi nace, “Kingani ban wani tsaya ƙare musu kalloba, yanzu haka babu kamannin wanda zan iya kawowa a cikinsu”.
       Tace, “Tab, amma lallai kinyi gwari dan wlhy anci kasuwar sama babuke Babie, ai har sunan mai green suit ɗinma na riƙe”.
        Kallonta nayi da mamaki, tare da jin zuciyata tai zallo, kamar na tambayeta yaya sunan sai kuma na taɓe baki ina miƙewa, “Kinga dan ALLAH bar wannan shirmen tashi muje, yaushe kika fara lalacewa ne haka Ummie?”.
      Dariya ta tuntsire da ita tana dukan kafaɗata, tace, “K nakai aurefa, sannan dukkan burikanmu sun cika, miya rage mana kuma? Musamu mazajen aure kawai, kodan ke kin samu Yah Qaseem a hannune”.
       Kallonta nayi a wani irin yanayi jin ta ambaci yah Qaseem, sai ban iya furta komaiba nai gaba abina ina murmushin ƙarfin hali.
     Itama bata sake maganaba ta biyoni da hanzari muka dai-daita tafiyarmu.

           Da ɗan aiken Yah Qaseem mukai karo akan naje yanason ganina.
      Haka kawai sai naji kiran yaban haushi, amma bani da damar ƙin zuwa ɗin.
       Na kalli Ummie ina faɗin, “Dan ALLAH ki rakani tawan”.
      Baya tai tana zaro idanu, “Wa? Rufamin asiri hajiyata, wannan fagen na masoyane ai, aidai ƙone ƙaɗan babie kar ai ƙurmus dan ALLAH”.
         Harara na zuba mata kafin na wuce ina zare hular kaina na riƙe a hannu.
       Koda na isa Office ɗin nasa kaina tsaye na shiga, dan ya bada sharaɗin shigata babu shamaki.
         Kallo ɗaya naima fuskarsa na fahimci ransa a ɓace yake, na zauna ina gaidashi cikin girmamawa kamar yanda na saba.
        Bai amsaba sai numfashi daya sauke, ya taso daga kujerarsa ya dawo inda nake shima ya zauna a ɗayar kujerar dake kallon wadda nake kai.
      Idanu ya tsuramin kusan minti ɗaya, niko na gaza kallonsa saima takura da nayi, cikin son katseshi na shiga gaishesa.
      Nanma numfashin ya kuma saukewa yana janye idanunsa a kaina.
      Ba tare dana kallesanba nace, “Yah Qaseem lafiya dai ko?”.
     Siririn tsaki yaja yana haɗawa da ƙaramar ƙwafa, “inafa lafiya wannan banzan ya dawo”.
      Da mamaki nace, “Banza kuma? Wanene banza yah Qaseem?”.
     Tsakin ya kuma ja yana maido kallonsa kaina, “Bazaki taɓa ganewaba, dan haka share, ina kikaje ɗazun na aika kiranki akace kun fita?”.
        Zamana na gyara cikin rashin damuwa nace, “Ba inda naje, kawai tarbar waɗanan jami'an namu da suka dawone.........”
      “Kina nufin dama dake akaje?”
   Yay maganar cikin tare numfashina tamkar zai haɗiyi harshensa.
         Da mamakinsa na ɗaga kaina kawai.
      Sosai ɓacin rai ya kuma bayyana a kan fuskarsa, ya furzar da ɗacin da nakeda tabbacin yanaji tare da miƙewa.
     Nidai uffan bance dashiba saima kallo dana bisa dashi kawai.
     Bansan miya tunaba ya juyi yana faɗin in tashi muje muci abinci.
    Tashin kuwa nayi, ya fita ina biye dashi, koda muka fito a Office ɗin sai ya tsaya muna tafiya a tare.
           Bugawar da zuciyata tayine ya sakani komawa tafiya da sassarfa, ɗago idon da zanyi idona suka sauka akan mutumin ɗazun da mukaje tarba.
        Da ƙyar na iya haɗiye yawun daya tsinkemin a cikin baki saboda kallon ido cikin ido da mukaima juna, amma sai ya janye nashi tamkar bani yake kalloba ya shige motar da aka buɗe masa wadda alamomi suke nuna zai tafi gidane maybe.
         Nannauyan numfashi ya kufcemin wanda yay dai-dai da fitar sautin jan tsakin da Yah Qaseem yayi...........✍🏻

Page 36

.............Har muka isa wajen da kullum Yah Qaseem ke kaimu cin abinci anan kusa damu fuskarsa babu walwa, bama muba kusan duk anan manyan jami'an kecin abincin, dan wajene haɗaɗɗe da yasha gyara na musamman, sanan ake abinci mai tsafta da daɗi, sai dai kamarmu ƙananu da ƙarfinmu bai kaiba akwai wani gidan abincin daga ɗayan gefen mukanfi yawan zuwa acan muci.
To nidai bamma taɓa zuwa wancan ɗinba, dan kullum nan Yah Qaseem ke kawoni, idan kuma aiki yay masa yawa yakan saka akai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login