Showing 33001 words to 36000 words out of 147628 words

Chapter 12 - A Duniyata Boon 2 Complete Hausa Novel

fito sanda maamah ta cire wani rafas din ta bawa nadra da zummar ta qara a ciki.



"To kuje ku gaisa" Maamah ta basu umarni sanda ta fara zube nata kudaden da suka ja hankalin mutane da dama.



"Waye ya kawoku?, yaushe kukazo?,ina momma?" Ta damqe hannun nadra da tafi kusa da ita tana jera musu tambayar a gaggauce daya bayan daya.



"Momma ta tafi yau....tun da safen mukazo,mun dawo gidan maamah......"



"Tana da kirki adda.....kuma tace kema kina nan,zamuci gaba da ganinki.....kayanmu ma tace basai mun taho dasu ba......kawu yace muyi zamanmu zamufi samun kulawa".



"Baki da hankali huda?" Ta fada da sauti me qarfi tana qoqarin janye lullubinta don ta samu damar saka idanunta cikin na huda.



"Yi a hankali......idanun jamaa suna kanki" Maamah data sunkuya saman kanta tana maida mata lullubinta ta fada da murmushi akan fuskarta kamar wani abun arziqi take gaya mata.



"Ku tafi mu zauna daughters" Ta fada da kulawa sosai a muryarta da cikakkiyar fara'a.



Tana jin takunsu sanda suke sauka a wajen,ba damuwa ko wani abu cikin muryoyinsu,tana jin tafiyar nasu na buga zuciyarta sosai,tanaso qwalla ta fita daga idanunta komai qanqantarta ko zataji sanyi,amma ko daya bata samu wannan damar ba.



Koda aka kirayi anni saita aike amna da wani qaramin akwati da ba wanda yasan meye a ciki aka ajiye cikin wani salo na siyan girma.





*DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK)*

08187255862



5�� 5�� 5�
� 5�� 5�� 5�� 5�� 5��

_ZAFAFABIYAR_



6B6O6O6K 62



g,D� D� �



5�K�5�<�5�B�5�@� 22





22





Kafin a tashi tsaf ta rasa sauran nutsuwarta,wani irin tashin hankali takeji maras misali daga kowanne lungu da sashe na zuciyarta. Ba abinda ke gilmawa ta idanu da zuciyarta sai huda nadra da haneefa......ina momma bahijja?.....ina momma bahijja?,.....da gaske ne sun bawa maamah yaran?,ya akayi haka ta kasance?,ya akayi ta tafi ba tare da sunyi sallama?,ya akayi ta tafi ta barsu bata cika mata alqawarin data dauka akan 'yan uwanta ba?......zata sakene ta kalli rayuwarsu ta balbalce?,ko xatayi dukkan abinda ya kama tayi don ta tseratar da rayuwar yaran?. Wadannan sune tambayoyin da ta dinga yiwa kanta har a sanda take cikin kebantaccen qaramin parlor din da amna ta kawota bayan tashi daga taron,tace ta zauna zasu gana da anni.



Dogayen yatsunta da suka sha lalle kawai take murzawa kanta a qasa,zuciyarta na wani irin zafi tare da jin qaguwar su koma gida ta lalubi maamah suyi magana ta sosai da ita.....koda tana jin kamar ta samu ikon sarrafa zuciyarta da bin umarninta cikin wani irin takura da takeji ana yiwa zuciyarta,.....to amma sam bata samu lago akan abinda takeji a zuciyarta game da 'yan uwanta. Qaunarsu darajarsu martabarsu da kuma soyayya da shaquwar data ginu tsakaninsu ba abinda ya sauya.



"Assalamu alaikum" Muryar anni ta ratsa falon tana murza qofar ta shigo



"Wa'alaikumussalam" Tada daga kanta kadan tana duban qofar gami da amsa sallamar. Kallon kallo suka yiwa junansu,kowanne a cikin su yanason tuna inda yasan fuskar dan uwansa. Sabreen ce tayi saurin watsar da qoqarin lalubo inda tasan fuskar annin,saboda gaba daya hankalinta ba'a nan yake ba,sai ta samu kanta kawai da zamewa daga saman kujerar tana gaidata,wata dabi'a data manta rabon data aikatata,amma a yau ta samu kanta da yin saboda wani kwarjini da taji matar tayi mata.



"Koma ki zauna abinki daughter" Ta fada da kulawa amma saita kasa hakan,saita samu kanta da zama sosai tana tanqwashe qafafunta.



"Na tsaidaki ko?,ga dare yana qara yi,duk da me babban sunan bai qaraso ba,uzuri ya taso masa daya saka dole ya fita" Kai ta sakeyin qasa dashi ba tare da tace mata komai ba,batasan me yasa matar take mata kwarjini haka sosai ba.



"Bari muyi magana a taqaice a gaggauce......da farko ina miki maraba da shigowa cikinmu da kikayi,ina fatan Allah yasa ku zama abokan arziqin junanku.....Allah ya hada hankalinku waje daya......bani bace mahaifiyar fuad,amma idan na kira kaina uwa a gareshi nasan banyi laifi ba,ni din uwar riqonsa ce tun daga quruciyarsa har kawo yau.....hajiya mariya wato maamah itace mahaifiyarsa". Dole bata shirya ba maganar ta sakata daga kai da hanzari ta dubi anni,sai kuma ta maida ta sunkuyar



"Baiyi sa'ar uwa ba.....ke kuma bakiyi sa'ar d'an riqo ba" Abinda ta fadi kenan qasan zuciyarta tana jin kamar a tsakaninsu annin ta fita daban. Anya ba halinsa Allah ya duba ba ya hadashi da uwa daidai da halinsa?. Zaren tunaninta ya katse sanda anni ke magana



"Yana da kirki.....yana karamci,yana da tausayi yana da tausasawa amma fa.......ga mutumin daya fahimceshi. Bashi da sauqi ya fiya tsauri,bashi da tausayi ga wanda bai fahimci shi waye ba,bayason qarya.....bayason saba alqawari,bayason yaudara baya son ha'inci......sannan uwa uba baya daukar raini. Abu na gaba muddin zakayi wasa da addini taku ba zata taba zuwa daya ba.....muddin ba zaka kasance karimi kamar yadda yake ba ba zasu taba daina sabani ba,wadannan sune kadan daga halayensa.......ameenatu" Ta kirata da sunanta na ainihi,abinda ya motsa zuciyar sabreen kenan sosai



"Ban gaya miki duka halayensa ba don na tursasaki kula da yarona.....na gaya miki ne don na sauqaqa miki qofofin zama dashi....na gaya miki ne don kiyi hanzarin mamaye zuciyarsa......na kuma gaya miki ne don na rage miki wahalar fuskantarsa......naso ace na samu zama da wasu mutane mafi kusanci dake don na tambayi naki halayyar na isar masa dasu a shimfide.....domin cikar mafarkina shine......gidan muhammadu yafi gidan dukkanin wani magidance zama aljannar DUNIYA......gidansa ya zame masa kaffara akan kowanne abu daya fuskanta a rayuwarsa a baya" Anni ta qarashe maganar har tsakiyar zuciyarta tana fatan mafarkinta ya tabbata. Miqa hannu tayi a nutse ta kamo hannun sabreen ta sanya cikin nata



"Idan har zaki bashi dukkanin kulawa......idan har xaki nuna masa zallar soyayya irin soyayyar da uwar kewa danta.....idan har zaki kasance me addini tsafta da kwalliya.....xaki kula da abincin muhammadu tabbas kin gama samunsa a tafin hannunki......yana cikin yunwar soyayya da kulawa.....muddin ya samu isashiya da zata qosar dashi babu ko haufi kin gama mallakar zuciyarsa dama rayuwarsa gaba daya".



Ta saurara ta kuma fahimci duka zantukan annin,saidai cikin nata zuciyar wani magana takeyi na daban



"Inama ace zaki fahimci waye danki sani na zahiri ba fuska biyunsa ba......inama wata daban kike budewa sirrikansa wadda ta shirya xama dashi ba SABREEN me zaman wucin gadi ba".



Dole ta sanyashi kashe duka wayoyinsa tun a hanya a sanda abdussabur yake tuqashi zuwa gidan anni.



A cikin jikinsa da zuciyarsa yakejin wata irin galabaita da bai taba jin irinta ba saboda zurfafa da tunanin da yayi. Yana da kyau yaci gaba da tafiya a gabar da yake na sanya idanu akan kowanne motsi da abinda dukka yake da alaqa da maamah. A zarginsa me girma da qarfi ya sake hawa kan yarinyar.......ya sake samun gamsuwa da cewa akwai shirin daya shigo da ita gidan,tunda har qarfin alaqarsu yakai girman da zata kebanceta da wata number wayar ta daban wadda shi kansa baisan da ita ba. Wunin yau gaba daya fiye da rabin tunaninsa yau duka ya tafi ne akan hakan.



Bazaice maamah maqiyayarsa ce ba.....hakanan bazaice bata sonshi ba,amma ta fifita kudi dukiya da abun duniya sama da tasu soyayyar.......kusan yayi mata fari kuma cikakken sanin da dan adam kan iya yiwa zanen tafin hannunsa koma fuskarsa......bazaiyi wasa da rayuwarsa ba.....hakanan bazai barwa maamah kowacce irin dama ba.....hakanan zai saka yarinyar a wasan da zata qara fahimtar batasan komai ba cikin duniya.....zai dafata da ruwa da kuma jinin jikinta.



Yayi sallama ya shiga parlor dinne a sanda anni ke miqa mata wata irin takarda me daukan idanu dake qunshe da littatafai na addu'o'i



"Akwai tsaftatattun addu'o'in mallakar miji a ciki,wadanda basu da wani aibu illa ko shirka a ciki,saidai suna matuqar tasiri wajen kama miki zuciyar mijinki a gareki" Ko alamun fa'ida bataji cikin bayanin anni ba......wannan mallkar da take fadi inda zata yiwu ta bawa maamah ita ta mallaki dan nata kamar yadda tace,ita kuma ta sakar mata 'yan uwa tabbas shine zatafi farinciki.



Yana zaune yana sauraren anni tana jaddada mata



"Ki raqe addu'a da kyau.....a yanzun kece garkuwan mijinki,garkuwar gidanki ma gaba daya" Baki ya tabe yana siririn tsaki qasan ransa. Inda anni tasan wacece ita tabbas da bata wahalar da kanta wajen mata wannan dogon jawabin ba,da tayi saving energy dinta kawai saboda gaba,a sanda zata fahimci wala'alla ko haruffan baqin dake cikin littafin ba zata iya hadawa ba ballantana ta karanta,don shi kam daidai da karatun sallarta bashi da tabbaci akai,don ya sani cewa Allah ya fada cikin qur'ani me girma



_haqiqa sallah tana hana alfasha da duk wani nau'in abunqi_. Ya tabbatar da nutsatsiya kuma cikkiyar sallah takeyi bata yadda za'ayi ta kasa rabuwa da dabi'ar karuwanci da bin maza.



Ko a motar kamar ba wanda yasan da zaman juna. Kusan nasa tunanin ma na tafiyar dake gabansa ne daga yanzu zuwa kowanne lokaci,yayin da nata tunanin ya.lula duniyar yadda zata fidda 'yan uwanta daga wannan wasan da bata shirya shigarsu ciki ba.



Sanda suka isa gidan sam bata wani jira guard sun bude mata qofa ba,gurds din da take mutuwar jin haushinsu tun daga sanda suka hanata rawar gaban hantsi a gidansu. A yanzu kuma a wannan gidan ta fahimci dasu ake kowanne motsi,wannan wacce irin masifa ce kamar raqibu da atidu da buwayin sarki ya saukar maka da suka zama lallai ka rayu dasu don su dauki dukkan ayyukanka,masu kyau ko akasin haka.



A gaggauce ta wuce duka falukan ta zarce hallway zuwa bedroom din,burinta kawai ta isa ga gallababbiyar wayar ta hadu da maamah.



Da zafin nama ta birkita inda ta aje wayar kafin su fita,saidai kuma sama ko qasa ba wayar ba dalilinta. Cak ta tsaya tana gwama numfashi,sai kawai ta bude jakar data dawo da ita ta fidda asalin wayarta da take kiran kowa da kowa da ita.



Asalin layin maamah din ta kira,wanda bugu biyu ta daga,saidai bata jiyo komai ba sai muryar haneefa daga gefe da alama hira take mata ita kuma tana fadin



"Allah auta?" Idanu ta runtse,ta lura da gaske ta shiryawa wasan...... Ta ruwan sanyi takeso ta cutar da rayukan da basuji ba basu gani ba.



"Me kikeso?,me kike buqata?" Ta tambayeta kai tsaye ba tare data damu ta amsa sallamar data mata ba. Wani shu'umin murmushi ta aje,sannan ta jita tana cewa



"Haneefa jeki kwanta kema,idan na gama zanzo na daukeki mu wuce daki tare"



"Tom" Ta amsa mata kamar yadda yawanci haka maganarta take,abun kuma daya sake sokar zuciyar sabreen kenan.



"Mallakamin d'ana nakeso kiyi.....ni kuma zan mallaka miki 'yan uwanki ta ruwan sanyi,dama naki ne". Tayi mata bayanin hankali kwance. Suya sosai taji zuciyarta tanayi,tanason fadin maganganu da dama......tanason tayi abubuwa da dama amma kaman an danne harshensa sai zallar bacin ran dake mata zullo



"Why ni?,me yasa saini ne?" Ta fusgi kalmar daga harshenta ta watsawa maamah ita.



"Saboda ni a wajenki kawai na hango irin zarrar da nake buqata......a aikinki na gano abinda zaisa aikina ya cimma gaci.....uwa uba kina da wani irin kyau da zai iya saurin rusunar da zuciya ya kuma narka zuciyar kowanne d'a namiji". Qit kawai ta kashe wayar tana jifa da ita gami da cusa dukka yatsunta goma cikin sumarta.



Maganganun maman sun isheta haka,a yanzu basu take da buqatar ji ba. Kowacce tsiga ta jikinta ta miqe,taji wani irin matsuwa da fatan isowar kayan aikin maamah din hannunta. Inama ace zai yuwu ta danneshi tayita dura.masa abincin?,daga safe zuwa yamma ya zame mata mallakakke kaman yadda takeso ita kuma ta samu yancin 'yan uwanta. Tabbas! Inda babu 'yan uwanta da maamah din tayi garkuwa dasu,babu abinda zai hanata nuna mata ainihin kalarta da kuma ainihin yadda wasan zai gudana.





*DUNIYATA LITTAFI KUDI NE(PAID BOOK)*

08187255862



5�� 5�� 5�
� 5�� 5�� 5�� 5�� 5��

_ZAFAFABIYAR_



6B6O6O6K 62



g,D� D� �



5�K�5�<�5�B�5�@� 23







23





Har wani nauyi idanunshi ke masa saboda tsohuwar gajiya da sabuwar gajiya dake a jikinsa,ga kuma wadda ke jiransa a gaba. Wanka ya fara yi,sai kawai ya sauya pyjamas dinsa ba tare da yabi takan abinci ba don baijin gajiya zata barshi yayi hakan yabi lafiyar lallausan gadon nashi dake gewaye da kyawawan pillows daa luxury bedsheet din dake qarawa bed din zama wani na musamman me cike da alfarma da wata nutsuwar samun lafiyayyen bacci.



Numfashi biyu kacal ya sauke wani lallausan ringtone ya katse masa relaxing din da yayi. Duk kiran da zai shigo wayar yasan na wani makusancinsa ne,hakanan a baya so din ya miqa hannu ya dauko shafaffiyar wayar me wani irin kyan daukan hankali.



Sunanta da ya gani ya sanyashi miqewa daga kwanciya zuwa kashingida zuciyarsa tana bugawa,ya lumshe idonsa yana budewa lokaci daya,can qasan ransa yana fatan Allah yasa ba wani jagwal dinne ya taso ba ko zai sameshi.



Cikakkiyar sallama yayi mata,ta amsa da wani irin yanayi na karsashi da kulawa.



"Akwai baqi a qofar gida,sun gaya min securities na gidan sun hanasu shigowa" Har ya sauke qafafunsa qasan gadon da zummar yaje ya duba ta na'urar tsaronsa,sai ya tuna ashe ba'a gida yake ba nan wani sabon muhalli ne,baida tabbacin an gama installing nasu,dole ya koma ya zauna gefan gadon a nutse yace



"Baqi kuma maamah?....at these late hours?"



"Eh......ba wasu baqi bane......me aiki ce nace tazo don ta tayata zama,da kuma yanayin gidan naku dole saida mataimaki daban". Numfashi sosai ya zuqa yana fesarwa,kowanne taqi kuma kowanne taku da motsi na maamah magana ce me zaman kanta.....wanzuwar aiki ne da sai ka saka hasashenka da kyau zaka iya cimmasa.



"Amma maamah ina tunanin tafiya zamuyi.....dani da itan gaba daya jibi idan Allah ya kaimu....so koda tazo dinma zata zauna a gidan ne ita kadai.....nace if possible ta bari idan mun dawo....i will call you saiki turota" Har tsakiyar kanta taji wani abu ya tsarta mata,hakan kuma ya bayyana har cikin sautinta daya canza nan da nan,abinda ya sake bashi wani haske.



"Har zuwa yaushe zaku dawo?".



"2to 3days ne.....just bude kamfani kawai zanyi na dawo" Ya bata amsa bawai yana nufin dukkan maganganun daya fada haka suke ba. Duk da bai iya qarya ba......amma a wannan muhallin ya samu fatawar qarya a kansa a yanzu halastacciya ce.



Adadin kwanakin da taji basu da yawa sai taji damuwarta taqaitacciya ce........ta cika da fatan tafiyar ta sake basu kusancin da zai damqa mata dukka amanarsa a hannunta,yadda suna dawowa komai zai fara cikin sauqi aminci da kuma nasara



"To yayi baida damuwa.....ammmm amma ba....kace su barta ta shigo na bada saqo ta bawa d'iyata". Kai ya jinjina yana cewa



"Alright" Sai ya gintse kiran. Wadanda suke on duty ya duba sannan kai tsaye ya kira daya daga cikinsu. Saidai kafin basu damar bata damar shigowa sai daya basu dan qaramin aikin da tun kafin zuwaira ta qarasa ciki suka gama aiwatarwa suka tura masa.



Bawai bayan ta shigo cikin gidan ba......tun daga farkon layin daya amsa sunan MUHAMMAD JADDA STREET ta gama raina kanta dama komai nata,bata sake tsinkewa ba sai da suka iso qofar gate gate guda biyu da fuskar gidan ke dashi daban daban......ta gama kuma narkewa gaba daya tun daga harabar gidan har zuwa falon farko da suka zauna suna dakon sabreen.



Kowanne motsi da yadda laila ta gaza sukuni,ta kasa danne zallar zalamarta da kuma dimuwa da yadda gidan yake duka kan idanun zuwaira take yinsu,zuwairan da tayi banza da ranta tamkar ma batasan tanayi ba. Mummunar qullaci ta samu zuciyarta dayi akan hajja harira.....ko maamah bata fuskanci manufar harira na hadota da ita ba ta gama karantar komai.....baqinciki qyashi da hassadar ta zauna ita daya a gidan take mata......to itama ta lashi takobin zata gara nata wasan akan laila da hajja,zata kuma murza musu kalar nata zaren.



Karo na biyu kiran daya shigo mata yadan darsa mamaki a ranta,saidai a yanzun da 'yan uwanta ke tare da ita,bata jin zata iya tsallakewa kowanne kira da zatayi mata.....don tana cike da tsoro da fargabar shudewar kowanne minti a sanda suke tare da ita.



"Ki sauka zuwa falonki kina da baqi.....saqon farko kawai naci su baki.....kiyi qoqarin fara amfani dashi daga gobe zuwa jibi". Bata jira cewarta ba ta katse kiran,saita sauke wayar daga kunnenta tana binta da kallo kamar bata gane yaren da maamah tayi magana dashi ba.





5� �5�"�5�'�5�-�5�.�5�'�5�� 5�-�5��5�%�5��5�-�5�"�5�'� 5��5��5�2�5�� 5��5�� 5�,�5�.�5�$�5�� 5�,�5�!�5�.�5��5��





Daidai sanda jerin motocinsa ke fita daga gidan don komawa nasu gidan,tana zaune daga gefe zuciyarta tayi wani irin nauyi dauke da tarin kalamai da al'amura da tayo tsarabarsu cikin gidan.



Tasan tayi qasa d window din motar sanda amna tayo mata rakiya tana mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login