Showing 57001 words to 60000 words out of 147628 words

Chapter 20 - A Duniyata Boon 2 Complete Hausa Novel

bawai maganganunsa ba......if kikayi abinda zai sake sanya masa shakkan sakewa da gidan dukka ayyukanki zasu koma baya.... Sisters dinki zasu ci gaba da zama qarqashin hadari" Maganganun da suka fito daga qasan zuciyarta kenan,suka kuma sanyata tsaiwa cak daga takun data fara don matsawa zuwa gareshi.



Remote din ya dauka ya bude mata qofar yana ci gaba da abinda yakeyi



"Hey" Taji ya sake fada sanda ta sanya qafarta daya a waje,saita dakata ba tare data waiwayo ba



"Mind you....banason qazanta,i don't want it,ki kiyaye". Da sassarfa da kuma hanzari ta soma sauka saga stairs din har kamar zata fadi. Kuka ne yakeson qwace mata amma bataso yaji ko ya gani,don ta yiwa kanta alqawari ba zata taba bari yasan lagonta ba.



Baqincikinta yadda ya fadi mata dukka maganar da ke ransa,nata zuciyar da ruhi cike maqil da maganganu amma TARKON da take ciki yasa bazaiyuwu ta fiddasu ba.





*_Washegari_*





Tun shida na safe zuwaira ke kai kawo tsakanin shiyyarsu zuwa ainihin falon da kuma kitchen din. Jin shuru ba alamun tashi sai ta fara aikin gyaran dukka falukan da kuma kitchen din. Duk wani motsi da zataji hankalinta yana kai,tanaso ta samu cikakken bayani akan komai yadda zata zama cikakkiyar informer na maamah. Tanason bata duk kalar bayanan da takeso don tana son ta doke matsayin hajja harira wajen maamah. Ta kowacce fuska da kuma yanayi tanason ta taka matsayin da zata zama aljihun daman maamah a sanda burin maamah ya cika din. Itama tata zuciyar da ruhin cike suke da nata kalar burin da take fatan zuwan ranar wanzuwarsa.



Wani irin qarfi ta sanya ta danne zuciyarta ta fito shirya masa breakfast,duk da asara akayi daren jiya na dukka girkin da sukayi,sai tashi tayi tsakiyan dare ta kwashesu ta zuba a inda ta saba zubawa.



Yau din cikakkiyar shiga tayi,ta rufe jikinta sosai tunda ta fahimci ba ita kadai bace cikin gidan. Idanunta duka sunyi nauyi saboda kuka da rashin cikakken bacci. A hankali take ratsa falon hankalinta yana qofar kitchen din.



"Barka da fitowa ranki shi dade" Taso ta tsorata kadan,don gaba daya ta manta da wata baba zuwaira a gidan. Ta sauke dubanta a kanta sanda zuwaira ke qare mata kallon qwaqwaf. A jiya batayi cikakken bacci ba sai data gama fahimtar inda kowannensu yake kwana ita dashi. A gaban idanunta ta sauko daga samanshi a gaggauce cikin bacin rai ta fada dakinta,abincin dataxo ta kwashe kuma baici ba,a daren itama bata kwanta ba ta sharhantawa maamah komai.



"Ya zama dole na matsa mata lamba ta yaudaroshi ya zama a tafin hannunta" Abinda maamah ta furta kenan,tsoron taurin kai irin nasa yana damunta. Tasan halinsa da kafiya akan abinda baida niyya baiyi masa ba......amma zata sake yin amfani da qarfinta a matsayinta na uwa karo na biyu.



"Barka kade" Ta amsa mata a taqaice ba tare data sake dubanta ba tayi kitchen



"Nace ba,ba abinda za'ayi kuma?"



"Babu....kije saina nemeki" Ta amsa mata a taqaice,don kwata kwata batason doguwar magana gaba daya. Da kallo zuwaira ta bita har ta shige kitchen din,sai ta saki murmushi tana ji a ranta ya kamata taci tudu biyu fa......bangaren maamah din da bangaren yarinyar.....abinda ta kwana kenan tana tunani akai,gwara tayi amfani da damarta,ta yadda koda gaba kome ya faru zai zame mata ribar qafa,salon maganar nan da hausawa kance idan tayi ruwa rijiya,idan kuma batayi ba masai.



Dukka 4glass stove gas din ta kunna kowanne ta dora abu akai. Da zafi zafinta ta saka 'yar basirarta ta kammale breakfast din cikin taqaitaccen lokaci,ta gyara inda zata gyara ta fara daukan luxury Warmers din tana jerasu saman dining.



Cikin ginshira da wani irin tsanaki gami da nutsuwa yake saukowa daga saman stairs din,kunnensa manne da Bluetooth yana amsa waya,lokaci guda kuma yana qoqarin gyara tie dinsa.



Hankalinta yayi nisa sosai cikin duniyar tunani,fargaba kuma na sake cikata kamar kullum na kada a sake tafka asara yaqi cin komai kamar kullum,asarar da take sake kusantata da faduwarta da samun matsala a rayuwarta.



Tun daga nesan idanunshi suna kanta,duk da baiga fuskarta ba amma ya gane itace. Sai ya dauke dubansa yana haurawa zuwa steps din ya wuce zuwa kitchen. Qamshinsa kadai shi ya ankarar da ita,ta daga kanta tana bin bayansa da kallo gabanta yana wani irin faduwa,cikin mutuwar jiki ta ajjiye spoons din hannunta taja kujera daya tana jiran fitowarsa cike da hope.





*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*

08187255862



5�� 5�� 5�
� 5�� 5�� 5�� 5�� 5��

_Zafafabiyar_



6B6O6O6K 62



g,D� D� �



5�K�5�<�5�B�5�@� 35





_Daga abdullahi dan abbas R.A yace,Lokacin da aliyyu R.A ya auri nana fadima,sai manzon Allah S A W yace"ka bata wani abu(a matsayin sadakinta),sai sayyadina Aliyyu yace "ba komai a wajena" Sai manzan Allah S A W yace "ina sulkenka?"_







35





Coffee ya hadawa kansa,yayi tsaye jikin kitchen cabinet yana kurba a hankali. Kwanakin nan duka baici wani abincin arziqi ba,sai kame kame da cin abincin waje,wanda yasan totally isn't safe musamman ga mutum sannanne irinsa da ta kowacce fuska cikin barazana da qoqarin kawo musu hari ake ta duk wata siririyar kafa da za'a samu dama. Iya lamarin maamah da yarinyar ya isa zama izina a gareshi,abu a cikin gidan.... Amma kuma farautarka akeyi.



Sai yaji gaba daya coffee din ya fice masa a kai,yana qaramin tsaki ya ajiye cup din,ya ciri paper towel ya goge lips dinsa duk da ba baci sukayi ba ya fara takawa a nutse yana fita a kitchen din.



Sau daya tak ya kalleta ya dauke kansa,ya taka a nutse yana isa gabanta. Tsaiwarsa ta sanyata daga kanta,akwai inches tsakaninsu amma tana jin kamar ba wani gap daya rage musu. Idanunsa saman lips din nan nata da suke very smooth,ba digon komai akai sai ainihin color dinsa. Smart key na qofarsa ya dora saman table din,ya kuma harbasa gabanta. Ya motsa labbansa zaice wani abu wayarsa ta fara fidda wani tattausan ring me kama da sarewa,irin ring din da zai iya haifarwa da mutum karyewar zuciya musamman ga masu karyayyiyar zuciyar. Fareeda Khaleed mustapha sunan wanda ke yunqurin samun sadarwa dashi kenan aka sanar mishi. Maimaita kiran sunan me kiran wayar ta soma yi kamar ba zata dakata ba. Saman kunnuwanta sunan ya sauka,irin sunan da taji a wancan daren. Iska ya furzar daga bakinsa yana sauke numfashi,sannan yana qaramin tsaki gami da ciro wayar da wani dan zafin nama yana yanke kiran ya jefata aljihun yana sake sakin tsakin. Baki ta tabe qasa qasa tana kauda fuskarta wani sashen,can qasan zuciyarta kuwa gulma take,tasan za'a rina.....koda dukka jikinta kunnuwa ne ba zata taba yarda mutum kamar muhammad jadda bashi da kowa ba.....mutum kamar muhammad jadda baida ajiyayyun 'yammata da yake debe kewarsa dasu ba......ba zata yiwa kanta qarya ba,idan tace mummuna ne ko bai hadu ba tasan tabbas wannan din gundumemiyar qarya ce ta zabgawa kanta......to kuwa tasan zai wahala a rasashi da wasu halaye da sukayi kama da wannan. A iya rayuwarta.....a iya mazan data hadu dasu harda wadanda basu kaishi bama,masu kudi sosai matasa masu jini a jika,taga dabi'u kala daban daban da halayen da bata ma tsammaci ganinsu ba,yaga yadda matan aurensu suke ba komai ba a wajensu......taga irin qalubalen da shuke fuskanta a tattare dasu....matasan cikinsu harma da masu yawaitar shekaru,wannan abun ya sake cire mata sha'awar abubuwan nan guda biyu a ranta SOYAYYA da kuma AURE. Gadai guda daya nan ya cimmata,saidai tana da yaqinin ba zata bari yayi galaba a kanta ba,yayin da take bawa kanta tabbacin tafi qarfin wata soyayya taci galaba a kanta,don idan ka dauke soyayyar qannenta bata taba tsintar kanta cikin soyayyar komai ba,wannan shine yake sake bata yaqini tabbaci da nutsuwan ba zata taba yin soyayya ba....saidai ita a sota

(Nace uhmmm....maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta). Idanunsa ya maida saman fuskarta,a nutse ya fara magana kamar wanda ya hada jini da gidan sarauta.



"You can start your work today.......but......ya kamata ki sani,nasan komai da yake every single room......sannan nasan place dinshi,so do your own business......kiyi iya abinda akace kiyi" Daga haka sai ya juya a nutse don sauka a wajen,saidai kuma muryar da yaji tana gaidashi ya sanyashi tsaiwa yana juyawa wajen.



Zuwaira ce a durqushe a wajen,da yanayin da yake tabbatar masa ba yanzu yanzu ta shigo ba. Sunkuyar da kanta tayi sanda ya zube mata kaifafan idanun nan nasa,yayi mata wani irin kwarjini da bata taba ganinsa idanun kowanne mahaluki ba sai a kansa. Wannan kwarjinin nasa ya sanya suke qauracew waje duk sanda ya shigo gaida maamah. Sosai goshinta ya soma tsatstsafo da gumi,tana ganin kamar a iya kallonsa kadai zai iya bankado komai ya kuma fallasashi.



"Who are you?" Yayi tambayar kai tsaye ba wani wasa ko sassauci a muryarsa,abinda ya sanya zuwaira ta ida rudewa,ga turancin daya jefeta dashi wanda ya saka a duhu



"Eh....na'ammmm.....eh"



"Wacece ke?" Ya maida mata tambayar da hausa. Caraf ta kama maganar tasa



"Nice zuwaira.....zuwaira ce,me aikin da hajiya maamah ta aiko don taya uwargida sabgogi da hidimomin gida". Ta qarashe fada tana daddafe hannuwanta a qasa,saboda ji tayi kamar zata fadi daga tsugunnen.



Hannayensa kawai ya zube a aljihun wandonsa yana ci gaba da kallonta,yana kuma son ganin fuskarta sosai. Duk wani daya rabi maamah yana da nashi question mark din a wajensa.....duk wani wanda maamah zatayi qoqarin hada connection tsakaninsa dashi baida aminci ko nutsuwa kwata kwata dashi,don haka yake sake shawarwarin qarawa musaddiq kwanakin zamansa a qasar da ya aikeshi ba tare da wani qwaqwaran dalili ko kuma buqatar hakan ba.



Hannayensa nasa ya sauke ya soma takawa yana sauka daga wajen,zuwa sannan qiris ya ragewa zuwaira ta saki fitsari a wando.



"Kada na sake ganin gilmawarki cikin gidan nan indai ina nan......duk ranar kuma da kikayi sake hakan ya faru.....ki fara hada kayanki na barin gidan nan....basai nace ba"



"In sha Allahu ranka ya dade,tuba nake" Ta fada dukka jikinta yana rawa.



Daga ita har sabreen ba wanda yacewa da dan uwansa komai. Kusan minti biyar da fitarsa sannan ta tattara qarfinta ta miqe tana sake hawa steps din dining da sabreen ke zaune akai. Fuskarta qunshe da munafukin murmushin nan ta soma gaidata



"Barka da asuba ranki ya dade.....ashe har kin gama aikin?,ba zaki jira nazo ba?,hidimar ai sai tayi miki yawa,da sai na rage miki ai.....iyaka idan na gama abincin ki bada kalar maganin da za'a zuba a ciki......kedin abar tausayi ce ranki ya dade,kullum addu'ata da fatana ki kubuta daga hannun hajiya mariya lafiya" Zuwaira tayi maganar cikin matuqar sanyin muryar.....tsantsar alhini da kuma nuna damuwa.



Tunda zuwaira ke maganganun nan a jejjere sabreen bata daga kai ta kalleta ba sai da tazo gabar qarshen maganar tata. Kalmar tausayi data furta a maganar nata yaja hankalin sabreen ya kuma tsaye mata a rai. Sosai ta zubawa zuwaira idanu tana son tantance gaskiyar abinda ta fada,saidai kuma abun mamaki haka kawai sai taji ta kasa gamsuwa da ita.



Boyayyen numfashi ta sauke,sannan ta tattara hankalinta a kanta tana hade ranta tsaf



"Wannan duka ba huruminki bane.....kiyi abinda ya cancanci kiyi kawai" Sai ta miqe daga saman kujerar tana niyyar tafiya. Da sauri zuwairan ba tare da ta ji ciwon tsaidata a wata iyaka da tayi ba tace



"To ranki ya dade abincin fa?,yauma saidai a zubda?"



"Idan kina da buqatar ci kya iya ci ai" Ta amsa mata da gatse tana sauka daga step din idanunta yana sauka kan laila dake shigowa parlor din.



Sanye take da robber gown wadda tabi kowanne shape na jikinta ta lafe mata. Fuskar nan fes da kwalliya zaka rantse ba safiya bane ba. Ba komai a kanta sai wani qaramin bandana da bai rufe komai a gashin kanta ba. Wani mahaukacin tashin qamshi jikinta keyi,wanda turaren turare ne na musamman da aka tanada saboda wani mutum na daban.



Duk da fuska ko kuma jikinta ba wata kwalliya.....amma haka kawai ta fusgi hankalinta. Sassanyan kyan nan nata da baya buqatar kwalliya ko wani abu makamancin haka yana nan shimgide saman fuskarta. Haka kawai taji ta muzanta duk da kwalliyar dake jikinta,amma duk da haka sai taji ta raina kanta. Tashin farko wasu kalmomi na hajja suka dawo mata fes cikin kwanya suka qara mata azama da qwarin gwiwa. Muhammad jadda kawai take da buqatar gani,don haka taci gaba da shigowa falon tana jin izza tare da fatan ko yaya ta gwadawa sabreen wani abu da zai sosa ranta.



Kallo daya ta yiwa lailan ta watsar da ganinta a wajen,taci gaba da wucewa ciki ba tare data damu da kallon qurillar da laila ke mata ba. Ita sam bata ma dauketa a sunan damuwarta ba,damuwarta ta tsaya ne kan yadda yake neman maidata boyi boyin qarfi da yaji. Ta share masa sassa ta hada da wankin bandakinsa dama underwears dinsa,tana jin koda sama da qasa zasu hade ba zatayi wannan aikin ba. Lumshe idanunta tayi tana qara jin takaici yana cikata. Bashi da masaniyar hatta da girkin da take masa dole ce ta sanya take masa ba?,har wani qyashi da baqinciki ke rufeta gami da kasalar bacin rai duk sanda ta tsinci kanta dumu dumu a kitchen tana hidimar dafa masa abinci.



Dakinta kawai ta wuce bayan ta saqale masa key dinsa jikin qofarsa,tana fatan ya dawo ya samu sassansa da muqullansa a inda ya barsu.



Dining din laila ta wuce kai tsaye tana wani taku kai kace itace matar gidan,ranta ya cika maqil da kishi da hassadar sabreen din. Ko daga nesa ka hangosu sabreen din ta fita quruciya.......amma miskilancin yarinyar da shegen girman kanta mamaki yake bata. Bata taba mata kallo biyu ba....kai zata ma iya rantsewa sau daya ta mata nutsasten kallon cikin idanu Randa taso blocking mata hanya. So take ko yaya taga wutar kishinta a idanunta,to amma kullum suka hadu tana yin kamar babu aka kawo gidan aka ajiye ba dan adam ba.



"Ma aka dafa?" Ta tambayi zuwaira Kai tsaye tana latsa wayarta sanda zuwaira ta kusa gama kwashe warmers din.



"Sai yanzu Allah yayimin tashi,don haka saiki jira na gama da aikin matar gidan tukunna" Zuwaira ta gaya mata gatse gatse gami da satar idanunta ta gasa mata harara. Kullum ta tuna warning da kuma jan kunnenta akan ta yiwa yarinyar biyayya da hajiya mariya da hajja uwar yarinyar suka mata akan tabi yarinyar sau da qafa bama matar gidan ba.....sai taji kamar ta zabge yarinyar da mari.





*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*

08187255862



5�� 5�� 5�
� 5�� 5�� 5�� 5�� 5��

_Zafafabiyar_



6B6O6O6K 62



g,D� D� �



5�K�5�<�5�B�5�@� 36





_An karbo daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace,manzon Allah S A W yace,idan miji ya kira matarsa zuwa shimfida taqi zuwa,mala'iku zasuyita la'antarta har gari ya waye_



*_qarqashin wannan hadisin akwai qarin haske,idan a wannan qin da tayi kuma ta samu ciki koda ta rasu wajen haihuwa wasu malamai suna ganin bata samu wannan shahadar da mace me naquda ke samu ba idan ta rasu_*







36





"Ki gaggauta da Allah.... Am starving,ko ki bani wannan da kike debewa in fara dashi"



"Sannu akuya......" Zuwaira ta fada a ranta,amma a fili saita ajiye mata warmer din tana cewa



"Zaki iya ci mana.....amma kafin kicin ki fara sanarwa tsohuwarki gudun maida laifi a kaina" Ta fada dadan zafin rai. Haka kawai sai laila tasha jinin jikinta,don haka ta miqe tana sauka daga wajen



"Fresh nakeso.....kada ki wuce minti talatin" Bata ma iya amsa mata ba ta dauke ragowar warmer din tana wucewa kitchen din gami da jan tsaki qasa qasa.



Tafiyar minti arba'in da shida ta sadashi da mansion House din alhaji hamza kibiya. A qofar tafkeken gate din dake qara nuna alfarmar dake cikin gidan motocin suka tsaya bisa umarninsa,don yanaso ne ya gaida anni ya fito......ya kuma haida maamah din sannan ya wuce office din. Akwai cushewar ayyuka sosai yau din bisa schedule din da saddiq dinsa na yau da saddiq ya tura masa tun jiya da dare,wannan ya sanyashi fita da wuri. Wani irin qarin investors suketa samu a dukka kamfanoninsu,duk da yana yin komai bisa kula don ya tabbatar akwai mutanen dake bibiye dashi,kuma nasararsa a wancan lokacin yayi imanin ta tarwatsa musu dukka shirinsu..... Faduwarsu kuwa da shurunsu yayi amannar bawai suna nufin komai ya wuce bane.



Gidane dake cike da tsari,da kuma kusan duk wanda yake gidan bisa tsari da sanin ya kamata yake zaune. Kowa yasan aikinsa,tun daga kan security guards da sauran masu aiki na cikin gida dama farfajiyar gidan,hakanan bayin Allah da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login