Showing 9001 words to 12000 words out of 147628 words

Chapter 4 - A Duniyata Boon 2 Complete Hausa Novel

ba tare da sabawa ba.



"Kai mishi wayarsa" Tace da nadra tana miqa mata wayar,sannan ta miqe tana gyara jakarta tabi bayan nadra zuwa qofar gidan,tana jin yau saita nuna masa iyakarsa ta hanyar fita,idan yaso ya tashi duniyar a yau kowa ya huta.



Nadra ta rigata isa,ta bashi wayar dake ringing,yana duba me kiran yayi hanzarin dagawa tare da matuqar rusunawa yana fadin



"Hello sir" Idanunshi suna sauka kan sabreen,sai ya miqe yana sauraron umarni daga wayar yana kuma kallon sabreen wadda ke tafiya cikin tsananin fushi,har kuma ta samu nasarar sanya qafafunta a qofar gidan.



"......idan naga sabanin haka ka kuka da kanka" Qarshen maganarsa kenan data jawo hankalinsa zuwa ga sabreen wadda ta dauki hanyar barin layin sosai bata tsaya koda waiwayarsa ba ballantana wayarsa da yakeyi,tana jin bata da lokacinsu gaba dayansu.



Da sassarfa abdulgafar ya jefa wayar a aljihunsa ya juya da sassarfa yabi bayanta. Daga yadda yau boss din ya masa magana ya tabbatar akwai magana a qasa. He's speaking seriously,yasan abinda ya fada da gaske yake.



"Madam.....ah.....am,madam sorry......listen please" Ya furta bayan ya cimma bayanta. Nuna ma tasan yana biye da ita a wajenta bata lokaci ne,bata da lokacin batawa ta saurareshi daga shi har boss din nasa



"Madam please ki tsaya ki saurareni,am going to loose my job.....please listen to me". Maganar ya taba mata zuciya........yanzun nar rashin imaninsa yakai ace ya kori mutum bakin aikinsa saboda wani abu daban ya faru?. Daga yadda yake maganan kawai ya gaya mata da gaske yake fadi,don haka tadan sassauta tafiyar ba tare data kalleshi ba tace



"Ina jinka"



"Please madam ki koma gida.....kiyi haquri ba yadda muka iya.....haka boss ya tsara......"



"Wannan kuma bazai yiwu ba,idan baka da abun fada ka koma yafi maka sauqi" Daga hakan taci gaba da tafiyanta. A nutse take ratsa layin,yayin da idanun 'yan sanya ido ya soma yin caa a kanta. Ba yadda zaka kalleta ita da abdulgaffar din kace ba body guard dinta bane,saboda yake take mata baya yana maida takunsa duk inda ta dauke ba tare da sunsan abinda ya sanya ya biyota ba,take tsegungumi suka fara tashi,masu rade radi akan irin mijin da zata aura a yau suka samu tabbacin hakan



Da alama zazzafa ce itama tamkar boss din nasu,ya hanga ya hango babu wani sauran abinda ya rage masa illa ya kira oga farouq,don haka yana biye da itan yayi kiransa,yayi kuma bayani a taqaice.



"Turawa hood location ta watsapp...zaizo da mota ya kaita.....idan yazo din give me a call.....zanyi magana da ita" Yayi maganar haushin fu'ad yana kamashi.



A ganinsa tunda batu ake na aure koma meye ya kamata ya ajiyeshi a gefe,batun aure ya wuce wasa.....ya kuma wuce tunanin mutum.



Wani irin aiki ne da ake yinsa da umarni da kuma doka. Iya tsaiwar da tayi tana jiran ababen hawan da batasan dalilin da yasa duk wanda ta tsaida sai ya wuce ba.....wanda qwarewar aiki irin na abdulgaffar ya sanya yake musu alama me nuna gargadi kan tsaiwar tasu,take suke wucewa abinsu.



A hankali motar ta rage gudu tana qarasowa gabansu,wanda tun kafin takai ga qarasowar abdulgaffar ya ganeta. Motocin da dukka suka jibanci familyn muhammad jadda da kuma gidan alhj hamza kibiya ba boyayyu bane,don hatta da plate number dinsu na dabanne da wani irin kebantaccen tsari na daban.



Bai bari motar ta qaraso gabansu ba ya kirayi farouq din,sai komai yazo a daidai,isowar motar gabansu da kuma matsawa da yayi daura da ita ya saka wayar a handfree yadda idanunta zasu iya ganin wayar



"Ranki ya dade......Allah ya taimakeki,tuba muke,kunyi magana da boss yana cikin fushi ne.......ayi mana alfarma kiyi haquri,ga driver da mota nan ya iso,ki shiga ya kaiki duk inda kikeso,tuba muke,tuba muke" Ya maimaita har sau biyu yana hade tafukan hannayensa guri daya.



Batasan me ysaa ba,amma sai taji tasss ta sauka daga fushin da takeji. Yanayin maganarsu dama komai nasu ba daya bane,batasan kuma waye ba......sannan batasan nasabarsa dashi ba.....amma da iya lafuzan bakinsa kadai ta tabbatarwa kanta yasha banban dashi tako ina.



Batace komai ba ta soma takawa tana nufar motar da tuntuni suka wagale mata qofar suna tsaye suna jiran isowarta,tadan dubi security din kadan ta kauda kai tana tabe baki. Su kuma a haka rayuwarsu zata qare?,basa da aiki sai ta'ammali da murda murdan garadan da babu rahama akan fuskarsu?,idan kuma suna tsaye sai kace gumaka?,wacce irin rayuwa zata shiga ne?. Da wannan tambayar ta shiga cikin motar suka maida murfin suka rufe.



Duk da yadda ranta yake a bade,zuciyar kuma bata tare da komai amma hakan bai hanata fahimtar banbancin inda ta shigo ba. A hankali ta kalli wani sashe na motar,cikin ranta tana jin zallar tsagwaron banbanci. Batayi kuskure ba idan tace tsahon rayuwarta bata taba tsammanin da gaske akwai mota irin wannan a nigeriar mu ba,cikin motar bai mata kama da komai ba saida wani qawataccen madaidaicin falo na alfarma,idan ba yaye labulen window din kayi ba zata ko dan jirin motsin motar kadan ba saika tsammaci cikin wani killataccen falon kake. Taja numfashi a boye tana saukeshi,duk da ita kadaice a nan amma saita killace ganinta. Bangare daya zuciyarta tana bugawa da samun tabbacin lallai da gasken da kawun ke fada su din ba qananun mutane bane......amma ta yaya suke bibiyan rayuwarta?,me yasa sai ita?,me suke tunanin tana dashi wanda zata iya basu?. Amsar dai kamar kowane lokaci.....hasashen kaman na kowanne lokaci shine AKWAI WANI ABU A QASA.



Da wani irin makirin narkakken murmushi ta maida murfin qawataccen akwatin ta rufe bayan ta gama ganin suturar alfarmar da aka tsumata da wasu tsatsube tsatsube na musamman da suke a mazaunin matakin farko na fara tunkarar shirin data yiwa rayuwar mutum biyun.......sanadin wato sabreen.....da kuma maqasudin wato muhammad fu'ad.



"Komai yayi hajja........suturar million biyu kam baa kashe kudinsu a banza ba.......yanzu zuwaira za'a aika?.....inajin kamar nayi tattaki naje nakai Mata da kaina,don inaso ta fahimci muhimmancin sanya suturar nan" Tayi zancan da wani irin muhimmanci cikin sautinta,tana tuna bayanan bokan da bata dana biyunsa a yanzu haka



_".......tana sata a jikinta ta fara zuwa hannu fa hajja......hakanan shi Kansa fu'ad kallon farko da zaiyi mata da suturar zai jarabtu da sonta,abinda zai bada damar gudanar da aikinmu cikin sauqi,zai karbi komai daga hannunta yaci ya kuma sha ba tare da wani matsala ko tangarda ba"_



Murmushi hajja ta saki tana dora qafarta daya saman daya



"Tafiyar zuwaira ita daya yana nuna aiken bame daraja bane,hakanan zuwanki da kanki zai jefa shakku a idanun mutanen da hankulansu ke kanmu irin aminatu hamza kibiya......wannan saqon babbar aminiya kuma amintacciya ya kamata ta isar dashi" Murmushi me sauti ya qwacewa maamah,ta bawa hajja hannu suka tafa tana fadin



"Allah yabar mutum da nasa.......bari na yiwa usama magana" Ta fadi tana dauko wayarta dake ajiye gefe ta fara lalubar number wayar usaman.



Zuwanta wajen aysha da dawowarta....farincikin data samu na ganin yarinyar ta dawo cikin cikakken hayyacinta da wata lafiya data sanya kumatunta cikowa shine ya haifar da sakewar fuskarta,ya kuma saka mata farincikin da ta kusa mantawa da abinda ke tunkararta a gobe.



Kallon masu kallo da idanun masu sanya idanu tun daga qofar gidansu da lafiyayyar motar ta ajiyeta bai dadata da qasa ba,har zuwa sanda ta isa tsakar gidan,ta kama matakala tana haurawa zuwa saman nasu.



Tana sanya qafarta sukayi kacibus da momma dauke da tray da lemuka da ruwa akai.



"Yauwa yanzu nake shirin kiranki......kina da baqi suna qasa,ki hanzarta ki samesu" Ta gaya mata tana rabata zata wuce



"Baqu momma?,su waye?,daga ina kuma?"



"Kinga duka wadannan tambayoyin ki adanasu idan kinje kyayi musu.....me lalle ma ke take jira tunda kika fita". Ambaton sunan me lalle saiya fara dagula mata lisssafi,bayan dirje fatar da aka dameta dashi na kwanaki kusan goma yanzu kuma wani me lalle ne na daban zata zauna yi?,salon a bata mata hannu da qafar da bata shirya diga musu komai ba?.



Ganin momma tayi gaba har tana gangarawa qasan stairs din ya sakata itama ta laqume dukka tambayoyinta tana wucewa ciki. Zuciyarta fal da saqe saqe ta sauya abayar jikinta zuwa wata sassauqar doguwar Riga cotton me gajeran hannu data zauna daidai jikinta,ta dauki qaramin hijab daya tsaya mata iya kafadu ta maqala ta juyo tana saukowa.



Dukkansu su biyun suka amsa mata sallamar idanunsu a kanta



"Tubarkalla ma sha Allah" Zuwaira da tayo rakiya ta qarfi da yaji don ba haka Hajja taso ba ta furta kyan sabreen yana bugar da ita. Duk yadda take jin hira da yadda aka tsara komai bata taba kawowa kyan yarinyar yakai haka ba,ta dauka maamah din nada tsananin wayo......zata dauko yarinyar da bata da cikakken siffa gudun juyewar reshe da mujiya. A iya sanin data yiwa halittar 'ya'ya maza masu jarabtuwa da kyakkyawar mace komai kamewarsu kuwa. Sanda suka iso gidan batayi tunanin gidan masu matsakaicin qarfi da gata irin wannan yana qunshe da kyakkyawar sura har haka ba,taci gaba da qare mata kallo yadda shape me qirar Coca-Cola ya fita sosai ta cikin rigar ta wajen qugunta.



Duk kallon da zuwaira ke qare mata hankalinta baikai ba,saboda hankalinta daya tafi akan hajja da suka fara hada idanu. Ta yaya zata manta fuskar matar?,bayan tana a wajen sanda sukazo da tallar qazamtacciyar hajarsu?,kuma kusan itace tafinta a wajen matar dake iqirarin mahaifiya take a wajensa.



Yadda sabreen din ta tsareta da idanu tana zama a dosane a hannun kujera irin yadda takeyi idan zuwan mutum magana ko mu'amala dashi baiyi mata ba



"Sannu ko?" Hajja ta fada tana qaqaro murmushin dole. Wani irin kishi me girma ya sauko mata akan Sabreen din. A haduwarsu da suka taba yi qwaya biyu hankalinta bai taba kaiwa kan sassanyan kyan da yarinyar ke dashi ba. Wani irin halakakken kyau dake boye a kowanne sashe da kuma halittarta. Anya wannan ba kuskure bane?,idan har tayi saken daya fadawa sonta rabasu kuwa zai zama abu me sauqi kuwa?.



Tabbas bata taba kula da wannan kyan ba,wanda inda tasan dashi tana da dukkan makaman da zata rusa tafiyar........a yanzu bayan komai yayi nisa ta yaya zata katse wannan wasan da bata taba ganin abinda maamah ta ciwa buri a kansa har haka ba.



"Yauwa sannu" Sabreen ta maida mata da salon yadda tace da ita. Haka kawai taji ba zata iya gaida matar ba,tun a waccar ranar duk wata kima martaba da kuma mutunci da ake ganin dan adam me girma da shekaru nasu duka su biyun suka kwaranye mata.



"Ya gida ya shirye shirye?" Hajjan ta sake dauriyar fada yadda sabreen din ke shan qamshi yana qara qona mata rai,amma duka wannan ba komai bane......tasan s nan kusa zata fahimci wace ita?kuma su waye su.



"Alhamdulillah" Ta sake amsa musu. Kai tsaye hajja ta gabatar da abinda ya kawosun,da dukkan alamu sun nuna ba'a maraba dasu ata nan din



"Saqone daga mamarki" Hajja ta fadi tana turawa zuwaira akwatin,ita kuma tana sadar dashi xuwa ga sabreen dake binsu da idanu.



5��5��5�
�5��5��5��5��5�� 5�-�5�*�5�5�5�5�5�"�5�'�5�*�5�/� 5�,�5�6�5�%�5�*� 5�/�5�&�



08187255862



5�� 5�� 5�
� 5�� 5�� 5�� 5�� 5��

5�!�5�"�5�'�5�"�5�'�5�"�5�#�5�*�5�:�5�"�5�3�



6B6O6O6K 62



g,D� D� �



5�K�5�<�5�B�5�@� 10





Page 10





Can cikin tsakiyar kanta maganganun mutane ke mata yawo sanda motar ke tafiya cikin nutsuwa saman lafiyayyar kwaltar dake shimfide a kanta. Muryoyin mutane daban daban da sukayi mata fadan shiga gidan miji wai a cewarsu



"Allah yasa dai ki iya zama......don zaman aure daban da zaman bariki,zaman gidan miji daban da yawon bariki" Muryar bibo kenan da nata salon fadan da yafi kama da turun mutuwa



"Da dadi ba dadi kiyi haquri ki zauna......Allah yasa mutuwa ce zata raba,kiji kiqi ji,ki gani kiqi gani" Muryar daada kenan wadda ta kama hannuwanta tana fada muryarta a sanyaye. Ko da can ba zatace ga wani mummunan abu da daada ta taba musu ba,ita dai barta da shariya da rashin shiga lamari da sabgar kowa cikin gidan. Idan ka ganta kuwa a ciki to tabbas abu yaci tura,amma bibo da yaabi koda dan wani akeyi suna iya ara su yafa tun usul.



"Mommaa......nadra.....haneefa.....huda" Sunayen data iya kirawa momma kenan sanda take yunqurin sakata a cikin motar da zata yi musu jagora zuwa inda zasuje.



"Ina sane dasu......kuna su din ba nauyinki bane" Ta amsa masa a tausashe.



Ta cikin lafayar jikinta take iya hangen yadda motar ke tsala gudu abinta,amma saboda lafiyar motar da irin tsarin da akayi mata zaka rantse ba gudun takeyi ba.



Ta maida idanunta ta lumshe,wasu hawaye da batasan sanda suka taru ba suka biyo kuncinta suka diga bayan hannunta dake ajiye saman cinyarta. Har yanzu dai ta kasa gasgata abinda take gani,har yanzu ta kasa gasgata abinda kunnuwanta da zuciyarta ke nanata mata.



Da gaske mutumin nan yaci galaba a kanta da dukka tsarikansa.....da gaske shike da nasara ba ita ba.......da gaske ya cinye wasan a wannan gabar.....saidai kuma hakan baya nufin zaita nasara kenan a kanta,hakan baya nufin ta fadi kenan har abada.....lallai zata canza labarin......zata canza qaddarar da dukkan iyawarta.



"Gidan mamarshi zamu fara shiga.......sai gidan riqonsa,kamar haka matar data shigo dazu tace ko?" Daada ta fadi tana dan duban momma bahijja da hannun sabreen yake cikin nata.



"Eh haka ne" Ta amsa mata idanunta sauke kan faffadan sabon gate din gidan maamah dake nuna zallar dukiyar dake narke cikin gidan.



A nutse jerin gwanon motocin suka cusa kai makekiyar harabar gidan data kasance mafarkin maamah na shekara da shekaru,gidan daya dauki hankula da bakunan dukkan jama'arta dake hulda da ita. Gidan da a cikin ranta ita kanta ta gamsu da dukiyar daya lashe,amma zuciyarta bata gama nutsuwa da hakan ba saboda har yanzu gidan alhj hamza kibiya da iyalinsa yafi nata girma yalwa da kuma tsari,ba tare data duba yawan da suka darata dashi ba,da kuma yawan al'umman da gidan ke dauka suke riqo a yanzu haka.



Tunda motar ta tsaya a parking lot na gidan gabanta yake wani irin faduwa,ta maida idonta ta lumshe tana sauraren bugun da zuciyarta keyi da bata taba jin irinsa ba,sai taji bugun har kusa da maqogoronta. Sake runtse idanunta tayi sanda momma bahijja ke fadin ta fito,tana jin bugun zuciyar na sake daduwa amma kuma ta rasa me ya kamata ta karanta?,wacce addu'a ce ta dace da irin wannan yanayin da takejin kanta a ciki?.



Riqon hannunta da momma din tayi shine ya sassauta mata abinda takeji kadan,ta sake riqe momma din itama da kyau ba tare tasan ta yadda zata gaya mata abinda takeji cikin qirjinta ba.



A dan hanzarce ta shigo dakin nata,sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key. Da dan hanzarin still ta isa gaban madubin nata dake manne da wasu lafiyayyun lockers. Ta murza daya daga ciki ta bude ta,sannan ta saka hannu ta ciro baqar ledar dake a ciki ta dora saman madubi. Ko ina a jikinta amsawa yakeyi da wani irin doki da son fara aiwatar da nata aikin,a yau batasan sau dubu nawa tana addu'ar samun wannan sa'ar ba......batasan sau nawa ta roqi samun nasara a wannan ranar ba,nasarar da indai ta rasata kamar wadancan kwanakin ta tabbatar komai zaizo mata da wahalar gaske.....batasan kuma ta yadda zata tari abun ba.



Kusan leda shidda ce,kowacce sai data kunceta sannan ta saka hannu ta fara ciro kayan ciki. Kusan tarkace ne a idanun me kallo,amma a wajen maamah gwara rashin million dubu da rasa daya daga cikin kayan. Wasu kwalabe ne masu dauke da wani irin baqin abu a ciki,wani kuma kore kore ne,saidai yana da dan qamshi qamshi kadan a ciki mara qarfi. Ta bude kowanne ta tsiyaya cikin tafin hannunta,ta kuma mulke hannun nata da kyau kamar yadda aka umarceta da tayi,sannan ta maida komai muhallinsa kamar bata taba komai ba cikin dakin.



Gaban madubin ta tsaya tana qoqarin controlling kanta da daidaita nutsuwarta. Idanun ta fes cikin fuskarta tana maganar zucci da kanta da kanta,wanda batayi wani nisa ba knocking din da ake mata ya isa kunnuwanta. Adan fusace tace tambaya don bata buqatar doguwar mu'amala da kowa har sai wadda tayi shirin saboda ita ta iso



"Zuwaira ce" Ta bata amsa a tsanake.



"Sun iso,suna falon qasa sun......."



"Gani nan" Ta tari numfashin zuwairan ba tare data jira sauran bayaninta ba. Ba sauran bayaninta take da buqatar ji ba,tunda taji abinda take buqatar jin,ta waiwaya tana zura takalmanta data cire tare da kallon tsadajjen mayafin data lullube jikinta dashi ta tabbatar ya zauna a jikinta......ya sanyata tayi kwarjini da wata irin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login