Showing 24001 words to 27000 words out of 72572 words

Chapter 9 - Taurin Zuciya Return Complete Hausa Novel

Anish   

02 Feb 2025

334

ni ne nan "
" kamar ban gane ba ? "

Shiru ya yi na dan lokaci kafin ya mike ka mata laptop din shi , ba musu ta sa hannu ta karba ta na kallon screen din

Da sauri ta lumshe idanun ta na kauda kai gefe ta na fadin " Inallillahi ! Minene wannan abun Ash ? "
Karbar laptop din shi ya yi , kafin ya kashe ta , ya ajiye saman cinyar shi ba tare da ya ce komai ba

A hankali Ummi ta bude idanun ta , ta juyo ta kale shi ta ce " Ba dai yaran nan ne ba "
Cikin nitsuwa ya ce mata " su ne ? "
" Oh my God , yanzu wanene zai yi wa yaran nan irin wannan abun , babu ko tausayi "
" ni ma abun da na ke son sani kennan , shi ya sa na taho nan , a binciken da na yi , da ga Nigeria a ke kai yaran nan US da sunnan za a sama musu aiki "

Cikin nitsuwa ta katse shi da cewa " da ga nan a yi sacrifices din su "
A hankali ya girgiza mata kai kafin ya ce " no ba Sacrifice din su a ke yi ba "
Shiru ta yi ba ta ce mishi komai ba dan ta ma rasa abun da za ce mishi
A hankali ta kontar da kan ta saman shoulder din shi ta lumshe idanun ta , ta daura hannun ta saman na shi cikin sanyin murya ta ce " Ash kar a je su ne su ka kashe...... "

Katse ta ya yi da cewa " no , ba su ba ne "
" I really missed Him " ta fada kamar za ta yi kuka
A hankali Ash ya lumshe idanun shi ya na bude su murya kassa kassa ya ce " Me too ! "
Dan karamin murmushi Ummi ta saki kafin ta daura dayan hannun ta saman kirjin shi saitin zuciyar shi cike da zolaya ta ce " kenan wannan zuciyar ba ta dutse ba ce , Allah ya kawo wadda za ta shiga ciki to "

Daura hannun shi ya yi saman na ta ya ce " bayan ke da mummy babu macen da za ta samu wuri a ciki " ya kai karshen ya na janye hannun ta

Dago kan ta ta yi ta na kallon shi ta ce " kenan ka na so na , shi ne kuma ba ka taba fada min ba " ta kai karshen ta na marairaice fuska

Slowly ya juyo ya kali face din ta " I love you more than my life "
Wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta rungume shi ta na fadin " I love you too my little "
A hankali ya zagayo da hannayan shi a bayan ta ya rungume ta shi ma , nan take ya ji wani sanyi cikin zuciyar shi , har ya manta last time da ya rungumi Twins din shi , amma ya san tun kafin ya fara horon soja ne , an jima gaskiya

Dan bubuga mata baya ya yi ya na fadin " okay , sake ni na ci gaba da aiki na "
Da to ta amsa mishi kafin ta sake shi , sai da ta manna mishi kiss a saman forehead din shi sannan ta tashi ta bar wajen , shi kuma ya dauki laptop din shi ya ci gaba da aikin shi


▪ZINDER

( KAUYEN NAWACH KALÉ )

▪BARIRA


Bakin ta dauke da sallama ta shigo cikin gidan na su
Harabar gidan ta na da girma sosai , cen na hango wata mata zaune saman tabarma , dattijuwa ce gaskia , da ga gani za ta wuce shekara 60

Barira na ganin ta ta saki kukan munafirci , ta nufe ta gudu
A rude matar nan ta ke fadin " Barira lafiya , me ya faru ki na kuka haka " ta fada dai'dai lokacin da Barira ta karaso ta zauna saman tabarma ta rungume matar nan ta na ci gaba da kukan ta ,

" kaka , Issa ya sake ni " ta fada cikin kukan na ta
Cike da tashin hankali matar nan ke fadin " na shiga uku ya sake ki ? "
Gyada mata kai Barira ta yi kafin ta daura da cewa " eh kaka , saki uku ma , kuma gashi ya sa Hayat ta bar gida kaka "
" ban gane ba , kamar ya ta bar gida "

A hankali Barira ta dago da ga jikin matar nan ta na fadin " eh kaka , kun fi kowa masaniya a kan auren da ya ke shirin yi mata da Rabeh , duka duka Hayat a nawa ta ke , ko al'ada ba ta fara ba , amma za ku sa ido ya dauke ta ya bawa mutumin da sai ya yi jika da ita , kaka Hayat ta tsere daren jiya , sai da ta ce min ita ba za ta aure shi ba amma na rufe ido , yanzu ga shi na rasa ta "

" inallillahi wa'ina illaihi raji'un , yanzu ina Hayat za ta tafi " Matar nan ta fada kamar za ta yi kuka ,
Mikewa tsaye Barira ta yi ta nufi dakin da ke fuskantar su ta na ci gaba da kukan ta , kayan ta ma a nan ta bar su

Ta na shiga matar nan ta mike ta nufi hanyar fita gidan ta fice sai sauri ta ke kamar za ta tashi sama , a haka har ta nufi fadar mai gari dan ta san wanda ta ke nema ya na cen

Ta na karasowa fadar mai gari ta ga wajen cike da mutane , a rude ta karaso wajen ta na tambayar lafiya , ba ta gama rufe bakin ta ba idanun ta su ka sauka kan gawar Issa , gaban Mai gari , kan shi sai zubar da jini ya ke

Ba ta san lokacin da ta saki wata razananiyar kara har da toshe bakin ta , nan take duk hankalin mutanan wajen ya dawo gare ta , da sauri wani dattijon da ke zaune kassa geffen mai gari ya taso ya nufe ta ya na tambayar me ya kawo ta nan

Cike da rudu ta ke fadin " Malam lafiya me ya same shi ? "
Bai ba ta amsar tambayar ta ba ya kamo hannun ta su ka juya ya na fadin " kontar da hankalin ki ba abun da ya faru , mu je gida zan fada miki "

Ba musu ta bi bayan shi su ka koma gidan da ta fito , su na shiga ta shiga jero mishi tambayoyi
Sakin hannun ta ya yi kafin ya juyo ya kale ta ya ce " komai ya wuce yanzu , Rabeh ne , ya tarda shi har gida ya yi mishi dukan tsiya wai ya cinye mishi kudin shi , yanzu haka maganar da na ke yi miki sun tafi su kai shi birni wajen yan sanda , shi kuma Issa a na jiran mai magani ya zo ya duba shi , abun da na ke so da ke , ki je gidan shi ki taho da Barira da Hayat tun kafin wani abu ya same su "

" to ai Barira ta na cikin gidan nan " Ta fada mishi
Cike da mamaki ya maimaita abun da ta fada
Gyada mata kai ta yi kafin ta ce " eh , dalilin da ya sa ma na je fada neman ka , Hayat ta tsere ta bar garin nan , ita kuma Barira Issa ya sake ta , malam don Allah ka sa samarin garin nan su tafi neman ta tun wani abu bai same ta ba " ta kai karshen kamar za ta yi kuka

Bayan inallillahi ba abun da malam ke fada , ya na dan zazaro idanu ya ma rasa abun da zai ce
Duk maganar nan da su ka yi a kunnen Barira ta na jin su amma ta ki fitowa sai ma Allah kara da ta ke yi wa Rabeh da Issa
Bari dai mu dan leko Hayat mu gani





TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍




( RETღRN )









(ROMANTIC LUV STORY )💋🔥







❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤

𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞


Wattpad : @bennybite







Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA
EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER )
TWO LIGHTS ( YAR JARIDA )
and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN )








FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕






اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️








TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION

👇👇👇👇👇👇

https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb






DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK

👇👇👇👇👇👇


https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i






𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠

👇👇👇👇👇👇👇


https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i















_________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________











[ 🅿🅰🅶🅴̥ 6 ❤🔥 ]







▪NIGERIA ( KANO STATE )


▪HAYAT 💦



Bayan ta baro gidan Bus tafiya ta fara yi saman titi sam ba ta san inda za ta je ba , amma ita ko a jikin ta , sai ma tafiya ta ke ta na cin bread din ta , ta na korawa da ruwa

Har sai da cinye kayan ta sannan ta fara lura da inda ta ke , Dum ta ji gaban ta ya fadi lokacin da idanun ta su ka yi mata arba da wata dankareriar mota da ta yo kan ta da mugun gudu

A razane ta saki wata irin razananiyar kara ta na sakin kumshin kayan ta , ta na toshe kunnuwan da duka hanayan ta biyu ta lumshe idanun ta , ta na jiran motar nan ta buge ta , Amma sai ta ji shiru

Slowly ta bude idanun ta , ta na kallon kassa sai ganin tayoyin motar nan ta yi dab da kafafun ta ,
A hankali ta dago kan ta , idanun ta ba su sauka ko ina ba sai saman wata kyakyawar mace , sanye cikin wani tsadaden lace milk colour ya na da ratsin baki , an yi mata babban dinki , ta yi daurin dan kwalin ta irin wannan no respect , ko gyale babu a jikin ta , ta yi uban make up , abun har ya ba ka tsoro amma ya yi mata kyau over , a shekaru za ta kai 40 haka , amma da ga ganin fatar jikin ta , ta na samun hutu irin wadanan manyan hajiyoyin

A hankali ta dafa shoulder din Hayat ta na fadin " daughter ba ki ji ciwo ba dai ko ? "
Gyada mata kai Hayat ta yi allamun a'a
Kallon Hayat matar nan ta yi da ga sama har kassa , sannan idanun ta su ka sauka kan kumshin kayan ta , nan take ta saki wani kyawatencen murmushi , ta kai hannu ta dauko kumshin kayan ta , ta riko hannun ta ta na fadin " shikenan mu je na rage miki hanya "

Ita dai Hayat da ido kawai ta ke bin ta , ta kassa cewa komai
Haka matar nan ta bude kofar wajen mai zaman banza ta ce ma Hayat ta shiga , ba musu ta shiga sannan matar nan ta rufe kofar , ta bude gidan baya ta saka kayan ta , sannan ta ragayo ta shiga mazaunin driver ta tada motar su ka bar wajen

Sai da su ka dan yi nisa sannan matar nan ta kali Hayat ta ce " ya sunan ki daughter "
Wasu yawu Hayat ta hadiye kafin ta ce " Hayat "
Gyada kan ta matar nan ta yi ta na dan tabe baki sannan ta ce " shikenan Hayat , ina zan sauke ki ? " ta fada ta na kallon ta ta wutsiyar ido

Dan sunkuyar da kai Hayat ta yi ba tare da ta ce komai ba
" a'a daughter lafiya , ba ki fada min ba , kar na wuce gidan na ku " matar nan ta fada cike da damuwa

A hankali Hayat ta bude baki kamar za ta yi kuka ta ce " guduwa na yi da ga gidan mu , kuma ba zan koma ba "
" asha , ki yi hakuri ki fada min ina ne gidan ku , saboda ba garin nan na ke ba , kaduna zan wuce , ba zan iya tafiya da ke ba "
Nan take Hayat ta fashe da kuka ta na girgiza kai ta ce " don Allah ba zan koma gida ba , auren dole su ke son yi min , ni zan bi ki don Allah kar ki meda ni "

" yanzu in su ka shiga neman ki , a ka gan ki tare da ki za qu ce sato ki na yi don Allah ki yi hakuri ki fada min , kar ki janyo min matsala "
" babu wanda ya san na taho kuma , kuma ba da garin nan na ke ba , da ga Niger na ke , babu wanda ya san nan na taho "

Parking motar ta matar nan ta yi geffen titi sannan ta juyo ta kali Hayat ta ce " shikenan , zan tafi da ke kaduna da sharadin bayan sati guda zan meyar da ke gidan ku "

Da sauri Hayat ta gyada mata kai ta ce " eh eh na yarda "
Dan karamin murmushi matar nan ta yi kafin ta zaro handkerchief guda ta mikawa Hayat ta ce ta goge hawayen ta , ba musu Hayat ta kai hannu ta karba ta fara goge hawayen ta

Ta na karba matar nan ta juya ta tada motar ta su ka bar wajen


▪ KADUNA

▪ASH 🔥


Zaune ya ke cikin parlourn part din shi , da ga shi sai short da singlet , ya daure wanan lalawsan gashin kan shi a baya ya sako wasu dan sirarren a gaban goshi , sai baza kamshi ya ke yi , ya kurawa Tv gaban shi ido babu ko kiftawa

Ya na a haka Iqbal ya shigo parlourn ya na sallama kassa , ya karaso geffen Ash ya zauna

Ba tare da ya juyo ba Ash ya ce mishi " What's wrong with you , tun da safe na ga sai kai kawo ka ke yi "

Dan karamin tsaki Iqbal ya yi kafin ya ce " Big bro , Wai me ya kawo mu Garin nan , ba mu yi ten hours ba da zuwa amma har na yi wanka shidda , saboda zafi "

" and ? " ya fada a takaice
" kamar ya and ? Ina fada maka zafi na ke ji ka ce min and , so ka ke sai na mutu " Iqbal ya fada kamar zai yi kuka

" ni na san ba zafi ba ka ke ji , fada min gaskiya , ita ce ta fada maka ka dawo ko "
Dan zaro idanu Iqbal ya yi , baki sake ya ke fadin " how did you know ? "
" ka na kewar ta ne ? " Ash ya tambaye shi

Dan kontar da kan shi ya yi saman shoulder din Ash ya ce " sosai ma , i don't know why duk lokacin da na rufe ido ina tuna........ " shiru ya yi ya kassa kai karshen maganar shi

Slowly Ash ya juyo ya kale shi , da sauri Iqbal ya kauda kai gefe ya na musurai da idanu
" why ka yi shiru ida maganar ka " Ash ya fada dan ya gane abun da ya ke son cewa

Da sauri Iqbal ya tashi ya na shirin fita dakin , amma bai yi taku daya ba , Ash ya riko hannun shi cak ya janyo shi da karfi ya dawo ya zauna inda ya taso
Cikin tsare gida Ash ya ce mishi " za ka kai karshen maganar ka , ko sai na fido shi da karfi "

Kukan shagwaba Iqbal ya shiga yi mishi ya na fadin " uhmm uhmm , Ni fa ba abun da zan ce "
" Shut up , ba na haka yi min wannan shirmen ba "
kunbure fuska Iqbal ya yi ya na turo dan bakin nan na shi
ya na shirin magana Ash ya riga shi cewa " Oya stanp up ka fara Frog jump "

dan zaro idanu Iqbal ya yi ya na fadin " Frog jump ? no , Really big bro frog jump sai dai Vedad ni na girma " ya kai karshen ya na kauda kai gefe

gyada kan shi Ash ya yi kafin ya ce " gaskiya ne , dole ka ce ka girma ka fara jin kamshin mace ba dole ba , za ka tashi ka fara ko sai na "

dan karamin gunguni Iqbal ya yi kafin ya tashi , ya koma tsakiyar parlourn ya tsuguna ya fara frog jump , ya san duk lokacin da Ash bai kai karshen maganar shi ba to ba da wassa ya ke ba , yanzu in ya ce ba zai yi ba , wlh dukan tsiya zai yi mishi kuma ba me

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login