Showing 51001 words to 54000 words out of 207756 words

Chapter 18 - Bakar Inuwa Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

660

fuska yana girgiza kansa. “Ba komai Yafendo, dama nazone akan batun Ramadhan”.
       Bappi ya sauke ajiyar zuciya a hankali, “Dama muma shi muke tattaunawa anan, dan munga dukan hirar da akai da Alhaji Andi ƙaura, nasan kuma itace kaima ta hargitsoka. Karka wani damu, dama wannan itace siyasar, duk wani abu da zasu masa yarfe damu kanmu yanzu bazasu gajiya wajen bincikosa ba. Sai dai mu mun riga munsan kanmu, addu'a kawai za'a dage da ita. Insha ALLAH a cikin satin nan za'a kai kuɗi a tsaida magana, sai a ɗaura auran bayan an gama zaɓe hankalinmu ya kwanta.”
        “Bappi haka shine dai-dai amma idan son samune dama a ɗaura auren kawai yanzu, sai ta cigaba da zama a gidan nasu bayan zaɓen sai ta tare ɗin”.
     Ɗan jimm Bappi yay yana tunani, kafin yay magana Anne tace, “Ya kamata ku fara jin ta bakin iyayenta dai, ku basu haƙƙinsu har sai sun yanke muku lokacin da sukaga ya dace da su. Da campaign da zaɓe har zuwa rantsarwa inaga watanni uku ne zuwa huɗu ai. To idan kunji ta bakinsu kunga yayi nisa sai ku roƙi alfarma. Kokuma shi uban gayyar ku tuntuɓesa ko yanada wani lokaci daya tsara”.
          Bappi yace, “Masha ALLAH hakan yayi kuwa. insha ALLAH zanyi magana da Ramadhan ɗin da safe idan ALLAH ya kaimu, na tabbatar yanzu yay barci. Ni bammasan yanda za'a kwashe da shi akan wannan barcin wurin ba yanzun. Dan kuwa ba nasa bane ba barci inhar da gaske ƙasar NAYA zai riƙe da ƙyau”.
     Ƴar dariya suka ɗanyi su duka.

__________________________________

        Alhmdllhi kamar yanda su Bappi suka yanke shawara an kai kuɗin auren Raudha Hutawa, dan Bappi ya dakatar da M. Dauda sake zuwa Bingo da yay niyyaryi akan son lallaɓa Asabe ta koma aurensa, yace yay haƙuri suɗan kammala wasu abubuwan. Shima M. Gambo ya bashi shawarar ya zauna su taya Ramadhan campaign anan daga baya sa san dabarar lallaɓa Asaben, sai shima ya gamsu.
      An amshi kuɗin auren Raudha harda hakimi, hakama dangin M. Dauda kowa so yake ace da shi akayi. Anba M. Dauda zaɓin tsaida lokaci, babu wani tunani ya yanke watanni huɗu. Duk da ba haka Bappi yaso ba sai baice komaiba sukai fatan ALLAH yasa haka shi yafi alkairi. Dan shima Ramadhan ɗin koda ya tuntuɓesa cayay wata huɗun, dan yafi son maida hankali akan wannan maganar campaign ɗin, ya kuma kawo hujjar idan akai auren yanzu za'aga kamar yayine dan amfani da Raudha wajen campaign. Sai dai abinda Bappi bai sani ba Ramadhan so yake ya zamewa auren, so yake kafin wata huɗun ya samu wani ya aurama Raudha ɗin batare da sanin su Bappi ba.

  ★★★

    A ɓangaren ƴan jam'iyya babu ɓata lokaci aka hau campaign ta kowanne ɓangare bayan an bada damar hakan ga ƴan takara ta kowanne fanni. Duk wani ɗan uwa da abokin arziƙi ya fito domin tallata *_ Brr Ramadhan B. Hameed Taura (Young millioner)_* kamar yanda matasa ke kiransa. Ta ko ina posters nashine ke yawo. Matashi na matasa kenan.
       Duk wani ƙarfin halin Ramadhan da tunanin zai iya sai abin ya koma bashi tsoro, lallai siyasa ba wasa bace ba. Ƙoƙari yake yaga ya hana duk wani ɗora matasa akan ta'addaci na basu ƙwaya da makamai da wasu manya keyi amma hakan ya gagara. Dan su Alhaji Yaro glass sun rigada sun kammala shirinsu tsaf a bayan fage. Hasalima Ramadhan baida maraba da hoto game da kowanne irin tsari nasu. Sai dai duk wani tsari nasu mara kyau sun binne iya su. Mai ƙyawunne kawai suka fiddo garesa. Hakan yasa yake cigaba da musu kallon mutanen kirki.

      Tabbas an kaɗa gangar siyasa. Mutanen ƙasa kuma sun amsa. sannan Alhmdllhi ta ko ina Ramadhan ya samu karɓuwa musamman a wajen matasa ƴan uwansa. Dan suna ganin wannan karonfa yaƙin nasune bana kowaba. A gefe kuma ƴan siyasa nata yarfe ga abokan hamayya. Musamman Ramadhan da tako'ina aka sakashi tsakkiya akan bai cancantaba. Ta yaya wanda ko aure baida shi zai iya riƙa ƙasar NAYA. Taya mai ƙarancin shekaru irinsa zai iya riƙa ƙasar NAYA? Taya ɗan gata irinsa zai iya riƙa ƙasar NAYA? Taya... Taya... Tay.... Dayawa suketa faman lissafi.   
       Sai dai kuma masu iya magana kance _zakaran da ALLAH ya nufa da cara ko ana mazuru ana shaho sai yayi_. To hakanne kam ga Ramadhan, dan tako ina bakajin sunan kowa sai na _Young millioner_ ga ƙuruciya ga kuɗi ga gayu ga ƙyawu.
      A ɓangaren ƴammata suma ba'a barsu abaya ba wajen yaƙin ganin sun ture gwamnatin Raudha sun maye gurbinta. Wasuko gani suke koda ita babu abinda za'a fasa fatansu dai Ramadhan ya amshi tayi kawai. Dukan saƙonsu da shishshiginsu yana hankalce da shi. Sai dai kuma basune agabansaba yanzun. Ita kanta da aka saka masa ranar auren da ita bata gabansa. Dan yakanma manta da wata saranar aure dake a kansa gaba daya. Shi hatta sunan Raudha sai abakin ƴan siyasa ma ya fara jinsa. Kuma bazaice ya riƙeba duk da ana yawan ambata saboda yarfe da ake masa akan batun aure dama auren nata da mutane kan fassarasa a siga kala-kala.
        Kallo ɗaya zakai masa ya baka tausai, duk ya rame yayi duhu saboda wahalar campaign da rashin barci. Duk ƙoƙarinsa nason ganin kowa ya fahimcesa hakan bai hana wasu jifansa da kalmar *Mai girman kai ba* susukance ya cika girman kan tsiya da izza. Duk lokacin da kalmar nan ta fito a bakin wani ɗan siyasa yakanyi murmushi, dan shi dai wannan girman kai nasa da aketa faɗa har yanzu bai ganinsa..........✍


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_



Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*



Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77



*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*

https://arewabooks.com/book?id=628103f05798291d0ecedd09

Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[6/10, 7:45 PM] NANA: *_Typing📲_*







*_Episode 20_*


.............★A ɓangaren gimbiya su'adah da fulani da Asmah suna akan bakansu na ganin sun hana auren Ramadhan da Raudha suma. Sai dai kuma hayaniyar campaign ta sakasu ajiye wannan batun gefe. Kowa fatansa a yanzu Ramadhan ya haye mulki kawai, daga nan koma miye zai biyo baya sai ayi. Dan sun ɗau alwashin yaronsu bazai auri ɗiyar talakawa ba. Zuwa yanzu sunyi bincike mai tsanani akan Raudha har Hutawa, shiyyasa suke tunanin karya lagon su Bappi da wannan sirrin a haukarsu.

★★★

       Raudha kam tun kwanaki biyu da kai kuɗin aurenta aunty Hannah da First lady suka yanke shawarar ɗauketa anan gidan, tare da kafama hajiyar birni hujja da kar Asabe ta zugeta, aiko tai azamar amincewa dan ita kanta lamarin Asaben tsoro yake bata duk da tasanta da kafiyar tsiya tunba yanzu ba. Tunda itama haka tayi ga masu kuɗi na sonta a wancan lokacin amma ta dage sai M. Dauda, itako a yanzu bazata yarda Asaben tai mata baƙin cikin samun abubuwa da damaba a dalilin auren Raudhan. Sun maidata wani gida keɓantacce wai ana koya mata dabarun mulki irin na first lady. Bawai suna mata hakan danta ƙaru ba, sunayine kawai danta saki jiki dasu har idan buƙatar sakata musu aiki ya taso anan gaba tayi babu musu.
        Kasancewar an haɗota dasu Yasmin kuma harda aunty Hannah duk da bata cika zama ba saboda yawon campaign sai hankalinta bai tashiba sosai, ga wata dattijuwa da sukace tana aikine a fadar shugaban ƙasar shekaru goma kenan cir na mulkinsa mama tambaya, sai ƙarin mutane biyu ƴan gayu sukuma masu koya mata abubun daya shafi gyaran jiki da dai sauransu. Sai shahararriyar mai kayan gyaran jikin nan dake gyare Raudha ɗin lungu da saƙo da ingatattun kayanta kayan ƙamshi dana sanyi *AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE 08067558902* _(guys ku garzaya dan zaku samu duk abinda kuke buƙata ga amaryar kb, daga kayan ƙamshin jiki, gida, kayan mata, maganin sanyi ingantacce😋😘😍🤗)_
          Kuma akwai wata islamiyya dake anan kusa da gidan saboda matsawarta yasa suka sakata ita dasu Yasmin. Sai dai bata fita sai da dogon hijjabin Uniform ɗin makarantar harda niƙaf. Ba'a dabarun mulki kawai aka tsayaba har gyaran jiki dasu saka kaya, girki duk koya mata akeyi, dan ma Alhmdllhi dama ta iya abubuwa da yawa na aikin cikin gida sai dai bana ƴan gayu irin haka ba, ba kuma sosai take girki ba a gida saboda icce suke amfani da shi ita kuma Asthma.
       A gefe kuma damuwar auren nata na nan daram a ranta. Musamman yawan ganin Ramadhan da takeyi a tv saboda campaign yanzun. Hakama idan ta fita islamiyya duk da anguwace ta manya tana ganin posters nashi. Ita kanta tasan ƙyaƙyƙyawane, yanayinsa da kwarjininsa dole ya shiga ran mai kallonsa da hanzari, sai dai ko kaɗan batajin sonsa a ranta, kamar yanda tasan itama bazai taɓa ya sota ba. ita da kanta kuma tana tilastama kanta saka ƙinsa a ranta saboda wasu dalilai

       ★Al'amarin campaign ya miƙa, kowa yana hangen nasara tattare da Ramadhan duk da masu iya magana kance siyasa kamar mace mai ciki ce, ba'a san mi zata haifa ba. Abubuwa da yawa masu daɗi da marasa daɗi sun faru a wajen campaign ɗin nan, wasu sun wuce an manta, wasu ko bazasu gogu a zuciyaba sai bayan mutuwa.
     Da gaske Ramadhan ya manta da batun wata Raudha saboda hargitsin campaign, sai idan wani ya ambaci sunanta ko zancen auren nasa ya fita a bakin wani yake tuna wata sa rana dake kansa ta aure. Sai dai ga Bappi da Pa da Anne ba haka bane, dan sunata shirye-shiryensu na biki duk da hatsaniyar campaign ɗin da kowa ke a ciki. Ga gimbiya Su'adah kuwa tunda ta gama binciki tushen Raudha hankalinta ya sake tashi ta birkicema Pa. Ko kulata baiyiba balle ta samu amsa. Hakan ya kuma ɓata ranta ita da su Fulani, batare da sanin kowaba suka shiga ƙulle-ƙullen yanda zasu ɓadda Raudha, sai dai sunbi duk wata hanya data dace amma basu sameta ba saboda ɓoyeta da akayi. Wannan dalilinne yasa gimbiya Su'adah tun karar Pa ana gab da rufe campaign.

        “Wai nikan nakega ya kamata ko sau ɗayane ai matar da Ramadhan zai aura a ganta wajen campaign, kar mutane su fassara rashin ganin nata da wani abu kuma ai”.
      Shiru kamar Pa bazai amsaba duk da tasan ya jita sarai, sai da ya gama kallon rahoton da akeyi a tv game da taron campaign daya faru na Alhaji Andi ƙaura a jihar Sato sannan, cikin fushi dajin ɗacin kalaman da Alhaji Andi ƙaura yay amfani dasu a wajen da yarfen da yayma Ramadhan yasa muryarsa kausasa.
        “K dake matsayin uwarsa tunda aka fara campaign ɗin kinje ne?”.
     Fuska ta kumbura, cikin zafinta tace, “Miye alaƙar ganina da ganinta a wajen? Kuma ni ai inada masu zuwamin”.
      “To itama ai danginta sunje sun wakilceta, dan mahaifinta campaign ɗin da yayi a yankinsu bana tunanin wani a gidan nan yayi kwatankwacinsa ma.”
      “Tunda ko yana neman gindin zama da shegen kwaɗayi ai dole yayi. Imagine yarona kamar Ramadhan dake da kowane irin gata na duniya ya ƙare da auren ƴar karuwa da ɗan duniya. Jikar mai tuwo-tuwo tikari a saudia. Miyasa idan dan alkairin da tayinne baza'a bata kuɗi itada iyayen nata ba tunda su sukafi buƙata. Sai an wani ƙaƙabama yarona? Idan kuma auren nata dole ne basai a samu wani a bashiba a ma'aikatan gidan nan”.
       Pa yasan ya cigaba da saurarenta zai iya mata abinda duk yazo masa a rai, dan haka ya miƙe tsam ya bar mata falon. Hakan ba ƙaramin sake ƙona mata rai yayiba, dan harda ƙwalla suka taru mata a ido, zuciyarta na ƙarajin tsanar Raudha da duk wanda ya shafeta. Tayi alƙawarin koda sunfi ƙarfinta anyi auren nan wlhy sai Raudha ta gwammace mutuwa da rayuwa.
        Da wannan ɓacin ran ta yini ranar, da daddare ta buƙaci ganin Ramadhan, duk da yanda yake a matuƙar gajiye dan yau jihar Nobama sukaje campaign haka ya daure ya amsa kiran nata. Tunda ya shigo take kallonsa, duk ya rame yayi duhu saboda wahalar kai kawo, sai dai hakan bai dametaba, dan tasan yana samun mulki zai koma normal harma yafi da.
        “Barka da dare Maa!”
Ya faɗa cike da girmamawa yana kaiwa zaune kujerar dake gefenta. Tab.. ɗin hannunta ta ajiye cike da ƙasaitarta tana dubansa. “Baka dai, lafiya ne na ganka sukuku?”.
       Numfashi yaɗan furzar, cikin muryarsa mai ɗan faɗi yace, “Kaina ke ciwo, nasan hayaniyarnan ce kawai”.
         “Basai kasha magani ba, ya za'ai mutum ya zauna da ciwo”.
     “Bana son na cika yawan shan maganinne, nasan da nayi barci zan ware”.
         Baki kawai ta ɗan taɓe, ta sake harɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya da tsuke fuska. Dan tana so ya fahimci ba zancen wasa bane. “Ina muka tsaye game da auren wannan yarinyar da aka ƙaƙaba maka?”.
        Baya ya ɗanyi da jikinsa ya kwantar a kujerar, ya lumshe idanunsa tamkar baiji mitace ba. Kusan sakan biyar sannan ya furzar da iska batare daya buɗe idanun ba. “Babu wani abu da zan iya yi akan auren nan tunda Pa da Bappi da Anne sun dage, kawai na yanke zan auretan daga baya zan san abunyi”.
          “Jikar tikari mai tuwo-tuwon zaka yarda ka aura? To bara na faɗa maka idan ma baka saniba. Uwarta kanta sai da tai karuwanci, a barikinne ma ta haɗu da uban yarinyar dan shima ɗan duniyarne na bugawa a magazine, daga kakarta har ƴan uwan uwarta duk karuwai ne har yanzun. Idan ma barci kake ka farka, duk yanda zaka zame ka zame kafin cikar waɗan nan kwanakin da suka tsaida”.
      Harga ALLAH maganganunta sun sokesa. Kuma dama tayi amfani dasu ne dansu soke-san tunda tasan yanda ya tsani karuwai tun yanada ƙarancin shekarunsa balle yanzun. Idanunsa dake kumbure da ɗan ja a cikinsu saboda rashin samun isashen barci ya zuba mata. Sai kuma yaɗan janye cikin taune lips. “Maa waya faɗa miki?”.
        Harara ta danƙara masa tana miƙewa, “Kaje ka bincika tunda na saba maka ƙarya...” Tana faɗa tabar wajen.
       “Maa Please.....”
Ya faɗa da sauri yana ƙoƙarin ganin ta tsaya amma tai masa banza ta shige. Jagwab ya koma ya zauna a kujerar yana dafe kansa daya ƙara ƙarfin gudun ciwo. _(Ƴar karuwa, jikar tikari mai tuwo-tuwo. Ubanta ma a yawon duniya suka haɗu da mamarta sukai aure, sannan duk ƴan uwan uwarta karuwaine har yanzun)._  “Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un”. Ya faɗa a fili yana dafe kansa da ya sake wata irin sarawa kamar zai faɗo ƙasa. Duk yanda yaso miƙewa a wajen kasawa yay. ALLAH ya taimakesa sai ga Rafi'a ƙanwarsa ta uku ta shigo falon da shayi a hannu da waya a kunne alamar magana takeyi.
      Cikin sauri tace, “Subahanallahi Yaya!”. Wayar da kofin shayin ta dire bisa centre table tayo kansa, duk yanda taso taimaka masa ya tashi ta kasa, dole ta fita ta kira Pa da sauran ƴan uwanta dake can babban falo kowa na harkar gabansa. Waɗanda ke a cikin ɗakunan barcinsu kuma suka firfito suma saboda yanda take kwakwazon kiran Pa.
       Komai Pa baice masaba, sai taimaka masa da yayi ya miƙe, da kansa ya kaisa har sashen su Anne su Rafi'a biye da shi hankali tashe, wasunsu ma hawaye sukeyi duk da bawai ya suma bane ko yanayi yayi tsamari. Kawai dai idan ka kallesa kasan babu lafiya tare da shi.
     Suma su Anne hankalinsu ya tashi, a take aka nemo doctor duk da yace su barshi shi lafiyarsa ƙalau, amma basu sauraresa ba. Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga doctor Shamsu. Koda ya dubasa sai yace musu gajiyace da ƴar damuwar data saka jininsa ɗan haurawa. Sai kuma sugar ɗinsa yayi low sosai da alama kwana biyu baya kula da shan maganinsa.
        Da ƙyar Ramadhan ya yarda aka saka masa drip, sai da Bappi yay masa jan ido ma, ALLAH ya taimaka bai jima da fara shiga jikinsaba barci mai nauyi yay awon gaba da shi. Su duka tausayinsane ya kamasu. Dan sun san yana matuƙar ƙoƙari akan abinda bai saba ba. Duk da yana zirga-zirgar kasuwanci ba irin wannan bace. Dan ko hayaniyar campaign ɗin nan tashin hankaline. Balle kuma akwai ƴan kunji-kunji kala-kala a gefe ga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login